Showing 30001 words to 33000 words out of 45946 words
ma sbd ganin take duk cikinta ne sanadin komai har Ahmed 'dinta ya rasa ransa
Fitowa tayi daga bedroom ta zauna kusadashi tareda 'dan kwantawa jikinsa tace,
My us navy captain pls kayi hkr ka rage damuwarnan sbd tanasani damuwa nima kawai tunda sun Riga sun tafi sai mu haqura koba komai Ai haqqin kashe mana baby ne yafita a kan....
Idanuwansa daya bu'de ne suka masifar razanata ta miqe tareda ja baya da sauri.
Batareda yace komaiba ya maida idanuwansa ya rufe sbd ko kallonta baya buqatar yaci gaba dayi dan zai iya yi mata komai akan zancenta daya daki zuciyarsa.
Khadija ma sannu ahankali ciwon zuciyarta ya kwantar da ita sbd damuwar rasuwar Ahmed data shigeta sosai ga wani irin tausayin kanta dana neesah dake shigarta akowace daqiqa.
Ummi ma dai sauqi sai agurin Allah sbd Sam takasa daina kukan rasuwar Ahmed saima wata sabuwar soyayyar neesah dake shigarta sbd saiyanxu tagane sona haqiqa Ahmed yayiwa neesah dan haka yanxu kamar amanar Ahmed take ganin neesah.
Ummi da kanta ta daure a daddafe ta shirya zata asibiti dubo neesah.
Shigowar ayeesha tayi daidai da fitowarsu ummi da mamar khadija dake gidan tun bayan rasuwar bata komaba.
Khadija ce tafito itama duk ta qarmaje ta zabga uwar rama sbd ciwo sake cinta.
Gaidasu ayeesha tayi tareda qaqalo murmushi tace,
ummi fita zakuyune keda bakyajin da'di.?
A 'dage mama ta kalleta sbd Sam ta tsani matar Jamaal dan ita 'yarta khadija taso 'daya daga cikin 'yayan ummi su aura amma ko yanxu ba sakin kari tayiba saita tattara wannan tsinanniyar ayeeshar ayeeshar ta watsar waje khadijarta tasamu damar zama matar Jamaal suyi ku'di kamar yanda take buri.
Mama hatsabibiyar mace ce dazata iya tarwatsa gida cikin awa 'daya komai taronsu da ha'din Kansu.,babban burinta khadija ta auri Jamaal ko Ahmed sbd dukiyarsu da sunansu batareda tasan itama khadijar Jamaal take kwa'daitawa kanta tuntuni.
Tsaf mama ta tsani ayeesha kuma da manufar fiddata gidan kota halin qaqa yasata fasa komawa tacewa yayanta( _dadynsu Jamaal_) anan zatayi zamanta dan dama batada aure sbd babansu khadija da qanwarta maryaam ya da'de da rasuwa.
Murmushin qeta tasaki tareda kallon ayeeshar tace,
Asibiti zamuje dubo kishiyarki aneesah.
Jiri ne yakusa zubar da ita ta dafa kujera jikinta na rawa cikin tashin hankalin daya kasa 6oyuwa tace,
Neesah bata mutuba ne?
Ummi mama ta 'dan kalla sbd ganin tambayar ta ayeesha ta 6ata mata rai saita saki mugun murmushi tace,
Bangane wannan tambayar takiba da kinason ace ta mutu ne?
Yawu ta ha'de tafara kame kame
mama tasaki murmushi tabi tawuce sbd sarai taga takaicin maganar ayeeshan a idon ummi.
Suna ficewa Palon ta zube qasa zuciyarta na tafasa akan jin labarin rashin mutuwar neesah gefe 'daya taga alamar idan tayi wasa mama zatafisu iya tsula iskanci.
Da gudu takoma part 'dinsu ko gani batayi ta rarumo wayarta takira zeey ta fada mata.
Wani wawan ashar zeey ta sako tareda dirowa daga gadon datake kwance cikin masifa tace,
Dole a daran yau basai gobe va muje asibiti mu qarasata sbd idan tadawo hankalinta mungama yawo.
Mamuh💋
🌲 *R H F W F*🐄
_Don't forget to vote, follow and comments_
[8:31AM, 4/9/2018] �?+234 703 593 2228�?: *_DACEWA_*
_(when east meets west)_
_By_
_Mamuh geee_
*_Viawattpad@mamuhgee_*
*52-53*
_wannan page 'din na ta'aziya ne daban hakuri ga masoyan Ahmed da zukatansu suka ta6u_🙏
Zaune take tsakiyar gadon ta kwantarda kanta kan qafafunta idonuwanta qure kan qofa ko qiftawa batayi saidai sun ka'da jajir duk ta qara zabgewa duk Wanda ya ganta saiya tausaya mata sbd ta canxa kamar ba neesah ba.
Mamy zaune riqeda remote tana ragewa Ac 'dakin sanyi sbd jin jikin neesar kamar da zazza6i.
Ummi ce a gaba kafin mama sai khadija.
Gurin neesah ummi ta nufa ta zauna jikinta na 'qara sanyi hawaye na taruwa a idonta sbd fuskar Ahmed take gani data kalli neesah.
Mamy gaisawa tayi da mama kafin ta amsa gaisuwar khadija dake raku6e kusada qofa tana kallon yanda yau neesah 'yar gayu da class takoma banbancinta da mahaukata ka'dan ne duk sbd aikin maqiya.
Rintse idanuwanta tayi wasu hawaye masu 'dumi suka gangaro mata ta lumshe ido tanajin damuwar rayuwar data tsinci kanta aciki Wanda sai yanxu take tabbatarda Allah ya hanata Jamaal ne sbd wannan azabar da neesah ke ciki ba qaddararta bace dan qila da ita'dince to da tuni su zeey 'din sun kasheta.
Shiru ya ratsa 'dakin na 'dan wani lokaci saiga Jamaal yashigo tareda ayeesha data biyosa damin ganin 'dakin da neesah take.
Kallon tuhuma mama ta watsawa ayeesah kafin ta saci kallon gefen Jamaal dake duba magungunan daya Dr kudi 'dazu da safe asiya tai fuskar mamaki tana fadin,
Meyasa ayeesah 'dazu kikayi mamakin da'akace neesah na raye harkina cewa bazai yiyu ace wani ya rayu a wutar nan ba?
A maganarki sai inaga kenan kina tsaye abin yafaru ko?
Dukkaninsu a bazata zancen yashigesu suka 'dora idanuwansu akan ayeesha don jiran mezatace ita.
Jikintane ya'dau rawa wani mugun zufa ya karyo mata ta kalli Jamaal taga ya kafeta da idanuwansa qasa qasa ai nan dabara ta fara kwance mata tana rawar murya tace,
Um..um...am..nazo wucewa ne dana dawo daga asibiti naga.....
Katseta mama tayi da cewa,
Wow wat miracle harkin iya fita keda kikai 6ari kuma idan ban mantaba a ranar aka dawo dake daga asibiti ina fatan dai ba wata matsalar ce tadawo miki ba harkika fita zuwa asibitin.
Wani yawun ta ha'de tana Neman abin cewa saikuma taji maman tasake cewa,
Kuma Kinga qanwarki nan khadija kwanakin nan tana fama da rashin lapia amma taqi zuwa asibiti sbd tsoron shiga mutane ne da ita kozaki fa'damin sunan asibitin dake hanyar barin gari saina kaita.
Cikeda baqin ciki da takaicin mamar daya cikata tace,
Nibansan wata asibitin bayan gariba.
Zaro ido mama tayi tace,
Aa kuma kikace zaki asibiti ne kikaga ha'darin a bayan gari?
Zaro ido tayi sbd shaf ta manta da haka tafada da farko.
Ummi da mamy takalla taga kowaccensu tayi nisa cikin nazarin maganganun a ranta tace nashiga uku wannan tsinanniyar matar zata kaini karshe na tona asirina da kaina dole nayi gaggawar sanar da zee a 'dau mataki akanta.
Jamaal kuwa ficewa yayi a 'dakin yana jujuya zancen mama da yanayin da ayeesha tashiga akan tambayar.
Wani mugun kallo ayeesha tabi mamar dashi tana qissima irin mummunar kisar dazatai mata.
Khadija kallonda ayeesha kewa mamarta ya ta6a zuciyarta sbd tagane manufarsa saidai bata tunanin zata bari sukai ga cutatar da mamarta zata takawa cin amanarsu da munafurcinsu burki kowama ya huta.
Mamy da ummi ne suka tafi gida sbd mamy zata 'danyi barci rana ta huta shima sbd mamar ta matsa ne akan taje ta huta ita zata zauna da neesar.
Bayan fitarsu khadija ta matso ahankali ta tsaya gaban mama tace,
Mama ki fita duk wata harkar ayeesha da mutanenta sbd they are very evil and dangerous,
I know wat they are really capable of in fact they can kill without any hesitation so pls mama stay away from them banason wani Abu yasameki all abinda nakeso yanxu shine neesah tasamu sauqi nabata all the evidence nadanakedashi tayi facin 'dinsu kuma badan komai nakeyiba sai sbd Ahmed.
Dariya mamar tayi duk da tayi mamakin maganar khadijar sosai tace,
Karki damu khadija kawai dai yanxu ki sanar dani komai inason nasani.
Ayeesha itada.....
Shigowar zeey 'dakin tana kuka ya katse khadija fadar abinda tai niyya ta miqe tana kallon zeey dake kukan munafurcin tausayin neesah.
Babu Wanda yace mata qala harta qaraci kukanta ta miqe ta fita tana jin takaicin qin fitarsu khadija 'dakin.
Kallon mama khadija tayi murya qasa qasa tace,
Be careful mama these people are very very dangerous.
Fita khadijar tayi tareda rufo qofar ya rage daga mama sai neesah dahar lokacin ko motsi batayiba kuma idonta a bude.
Ga mamakin mama sai ganin neesar tayi ta rintse idanuwa hawaye sun gangaro.
Mamakine yakamata sbd Dr yace qwaqwalwarta bata aiki daidai to meyasa take hawaye alhalin batasan komaiba yanxu.,
Well idan kuwa neesah na hawaye it means akwai abinda take tunawa tana hawayen.
Gyara zama tayi sbd gwada tabbatarda zarginta ta yamutsa fuska tana cewa,
Wai meyasa haryanxu mamyn neesah bata dawoba nidaifa tsoro nakeji kar masu bibiyar neesah subiyo ta hanyar mamynta gashi ita bata hankalinta bare ta fa'desu a kar6o mamyn kafin itama su....kasa qarasawa tayi tace,
Allah karka bari komai yakuma faruwa da kowa.
Ta gefen ido ta qurawa neesar ido ga mamakinta saitaga idanuwanta a bude jikinta na rawa hawaye na ganganrowa da gudu daga idanuwanta.
Miqewa tayi ta qaraso gaban gadon takalli neesar da kyau tace,
Poor neesah,,,
Tell me neesah tun yaushe kika dawo normal sbd you can't fool me narigada Nagano ki.
Lumshe ido neesar tayi batareda tabada kantaba ta juyawa mamar baya.
Murmushi mama tayi tace,
You see neesah nasan matsalarki duk da khadija bata zayyane min komaiba but you see khadija nason taimaka miki amma bazan bar hakanba until nima zakiyi min wani Abu 'daya.
Idan kin amince I promise to stand wit you until you bring them down,
Koma meyene zanyi danki samu yanda kikeso just promise me zaki barwa khadija Jamaal ta aura.
Cikin wani sabon baqin cikin sunan Jamaal kawai data kira yasata miqewa idanuwanta na rinewa da qiyayyarsa datakejin tana qara kama kowace kusurwa ta jikinta takalli mamar murya a shaqe tace,
And why will I trust you bayan abubuwan dana gani da idanuwana suna faruwa da mutanen dana yarda dasu gashi na rasa Ahmed..
Kuka tasaki mai cinrai tanajin tsananin kewar Ahmed na cinta har cikin jininta.
Neesah keba maqiyiyata bace kuma banason kizama maqiyiyata shiyasa nake baki wannan damar domin dukkaninmu musamu abinda mukeso cikin ruwan sanyi after all koma mezakiyi you need evidence kuma this is the only option for you to get it.
Cikin kuka da takaici tace,
'Yarki na 'daya daga cikin mutanen dana tsana sbd she knows everything amma taqi fada gashi yanxu na rasa Ahmed bakusan ya nakeji ajikin zuciyataba jinake gwara na mutu nabi Ahmed sbd shikadai ne me sona and now I can never be with him.
Share hawayenta tayi tareda kallon mamar cikin ido tace,
Na yarda da shara'dinki sbd bana buqatar ko jin sunansa bare buqatar cigaba da zama dashi sbd zamana dashi ya qare har abada so you can take him all for your daughter but let me clear sumthing to you,,don't double cross me sbd zuciyata yanxu a bushe take nima zan iyayin komai ga duk Wanda yayi gangancin sukata,
And for you daughter zanji da ita idan nagama da manyan sbd wannan alqawarine na 'dauka duk Wanda keda sa hannu ko sanadin mutuwar Ahmed will pay ciki harda Jamaal,ummi kawai nacire duk da itama bazan iya cigaba da zama a gurintaba.
Idanuwan neesar take kallo tabbas banda qiyayya da bala'i babu abinda take hangowa a tsakiyar idanuwan.
Ajiyar zuciya tasaki tace,
Well let's say the deal is sealed..
Sabbin hawaye ne suka gangaro mata ta kwanta tana sheshekar kuka ahankali tana kiran sunan Ahmed ahankali sbd she's ready ta fight them koda zata rasa ranta.
Shigowar mamy yasa mama miqewa tana cewa,
Bari naje gida Nima na 'dan miqe.
Cikin murmushi mamy tace,
Ai kuwa angode sosai.
Tana fita a mota ta tarar da khadija bayan tagamo ganin likita dataje.
Harta tada mota ta hango zeey zaune cikin wata ash corolla8 tai saurin kallon mama taga hankalinta baya wajen taja jiki ba qwari sukabar asibitin.
Da daddare mama takalleta tace,
Khadija inason kifa'damin duk wasu bayanai dazaki bawa neesah idan ta warke.
Cikin kallon mamaki tace,
Mama karki shiga wannan alamarin idan neesah ta warke zan fa'da mata komai da kaina dan ko suwaye ma yanxu nafasa fa'da miki sbd banason kisa kanki a rigima.
No khadija kifadamin komai ina son nasani sbd inason protecting 'dinki takowane hali,
Inason nizan bada bayanin sbd koma suwaye su fuskanceni bakeba sbd karsu cutatar dake.
Jikin khadijar ne yayi sanyi ta miqe tareda cewa,
Zan fa'da miki komai gobe insha Allah mama.
Harsun kwanta taji takasa barci sbd zeey data gani a asibiti 'dazu.
Saukowa gado tayi ahankali tareda zura dogon hijab ta 'dau wayarta da kudin mashin ahankali ta fice.
Asibitin ta nufa ta tsaya 'daga nesa ka'dan da 'dakin.
Wata nurse taga tazo tashiga saikuma taga mamy tafito 'dakin.
Bataga fuskar nurse 'dinba saitaji tsoron abinda yasa mamy tabaro nurse
Ita kadai a 'dakin.
Ahanki ta lalla6a ta isa qofar 'dakin ahankali ta tura qofar.
Zaro ido tayi jikinta na rawa sbd ganin fuskar zeey sanye da kayan nurses ta na kallon neesar dake bacci tana dariyar mugunta ahankali.
Wayarta ta zaro ahankali ta danna video recording.
Sosai fuskar zeey tafito ta zaro wani qaton dogon syringe zata yiwa neesah allurarsa saikuma ta tsaya tana tunani alamar ta manta wani Abu saita ciro wayarta daga aljihu ta danna kiran.,,
Ayeesha gani nasamu shigowa na manta a ina leloh yace na soka mata.
Cikin qaguwa ayeesha tace,
Ki soka mata koma a ina kika samu mudai ta mutu mu huta konasamu kan Jamaal nikadai.
Kashe wayar tayi ta 'daga syringe din zata da6awa neesah wayar kiran mama data duba bataga khadijarba yashigo wayarta
A tsorace zeey tajuyo sukai ido biyu da khadijar ta zaro ido cikin tsoro sbd ganin recording take.
Da gudu khadija tabar jikin qofar zeey tabiyota da mugun gudu.
Cikin mugun tsoro khadijar ke gudu gashi dare yayi kuma zeey a mota take.
Daqyar tasamu mashin jiki na rawa ta hau tafada masa inda zai kaita.
Pls qara gudu takusa kamomu wlh zata iya komai idan takamani.
Gudu mai mashin 'din yaqara sbd shima ya tsorata matuqa.
Gudu zeey keyi sosai dan ta kamosu tabi ta Kansu da mota kowama ya huta.
Wayar ayeesha takira tasanar da ita komai.
Suna isowa gidan tun bai tsayaba ta dira ta fa'da gidan tareda qalgama sakata ta nufi sashensu Jamaal da gudu sbd shi ka'dai takeson gani yanxu ta miqa masa wayar sbd harzancen ayeesha saidaya 'dauku.
Daf dazata isa taji saukar wani qaton ice a tsakiyar kanta tayi baya ta zube kanta na jini.
Janta cikin flowers ayeesha tayi kafin ta Lalla6a taje tabudewa zeey gida sukazo suka jata suka fitar waje zeey ta 'dago syringe 'din da dah neesah zasu sakawa ta sokawa khadijar shi tareda tatse mata ruwan ciki tsaf suka wuce suka barta gurin yashe tana shure shure.
Mamuh💋
🌲 *R H F W F*🐄
_Don't forget to vote, follow and comments_
*_DACEWA_*
_(when east meets west)_
_By_
_Mamuh geee_
*_Viawattpad@mamuhgee_*
*54-55*
Kasa zama mama tayi tasake danna kiran khadijar.
Motsin dayaji yasa ya tashi baiga ayeesha ba amma yaji qarar ruwa a toilet alamar tana ciki saiya fito Palo.
Sakejin motsin yayi a waje ya ta6a qofar palon zai bude ya fita ga mamakinsa saiyaji qofar a bu'de.
Fitowa yayi yafara dudubawa daidai lokacin da mama tasake kiran khadija saiya hango hasken waya ahankali ya qarasa ya tsaya ya kalli wayar ganin hoton khadija gaban wayar yasashi 'dauka dan ya tabbatarda tatace ta yadda.
Juyawa yayi yakoma ciki daidai shigowar ayeesha ta gate tazo gurin tayita dudduba wayar bata gantaba ta lalla6a takoma.
Turus tayi jikinta na 'dan rawa ta ha'diye wani mugun yawu ganinsa tsaye tsakiyar 'dakin.
Cikin mamaki ya kafeta da ido sbd har lokacin ruwan toilet 'din aiki suke ya tsammaci tana ciki.
Tun kafin yayi magana tarigasa da cewa,
Am dama dana Shiga nan toilet 'din ruwan ciki ya tsaya sainaje na bedroom "dina ashema na manta nabar wannan akunne gashi yanxu ya kawo bari na kashe.
Qala baice mataba sai ido daya bita dashi yana naxarin yanayinta daya nuna duk a ru'de take da ganinsa a farke.
Hankalin mama yakai qololuwar tashi ta fito Palo tafara dudduba ko Ina ba khadija tuni tsoro da fargaba suka shigeta.
Motsinta ya fiddo da inna Rabi nan itama hankalinta ya tashi suka bu'de qofar palo suka dudduba harabar gidan.
Ummi ce itama ta taso jin motsi Allah yasa dady yakoma tana 'dakinta na qasa shiyasa tajisu.
Tuni mama jikinta yafara sanyi hawaye na Neman tsinke mata.
Wayar Jamaal ummi takira ta sanar dashi ba 6ata lokaci ya fito tareda wayar khadijar a hannunsa yace,
Yanxu bada da'dewaba naji motsi nafito amma wayarta kawai nagani a qasa.
Da hanxari mama ta kar6i wayar jikinta na mugun rawa tace,
Daidai ina ka tsinci wayar?
Nuna mata gurin yayi taqarasa gurin da sauri ta duqa tana dubawa taga jini kwance a gurin.
Durqusawa shima yayi cikin mamaki dan da farko Sam bai luraba,,
Jinin suka farabi har bayan flowers kafin kuma suka cigaba dabi inda jinin yabi har gate.
Jiki na rawar tashin hankali mama ta bude gate 'din tareda sakin wani razanannen ihu ganin khadija kwance shame shame cikin jini kamar gawa.
Cikin sauri Jamaal ya fito da mota gaba 'dayansu suka 'dunguma zuwa asibiti.
Suna isa aka kar6eta cikin gaggawa duk da tsakar dare ne asibitin akwai wadataccin doctors.
Zaman 'yan bori mama tayi tana risgar kuka zuciyarta na tafasa.
Jamaal kuwa zama yayi tareda dafe Kansa yana tunanin alamarin.
Idan har yanda sukabi jininta to tabbas
A daidai inda ya tsinci wayarta adaidai gurin akai mata koma menene kafin aka jata bayan flowers tukuna kuma aka kuma 'daukarta ya jefota wajen gate.,,
Idan kuma hakan ne to koma menene ko wayene hakan na nufin 'dan cikin gidan ne tunda aciki komai yafaru.
Lumshe ido yayi tareda tunano ranar da aka shigo gidan lokacin da akazo ta windon neesah,
Ko a wannan lokacin tabbas wani daga ciki ne ya bude musu gida a zatonsa Ahmed ne to yanxu Ahmed bayanan to waye?
Ana kiran sallar asuba doctors 'din dasuke ciki suka fito kowanne fuska ba da'di.
Dr sulaiman Wanda case 'din neesah ke hannunsa yanxuma na khadijar a hannunsa ya fa'da shiya kirasu office 'dinsa bayan ya zauna ya 'dago ya kalli mama dake tsiyayar hawaye kamar numfashinta zai 'dauke
Maida kallonsa gurin Jamaal yayi murya a sanyaye yace,
Captain maganar gaskia akwai matsala sbd patient 'din nan ba qaramar buguwa kanta yayiba dan harsaida mukai mata 'dinki yanxu.,,
To duk madai ba wannan ne babbar matsalarba
The biggest problem is she was injected by par*****POI's.
Murya na rawa mama tace,
Me hakan ke nufi Dr?
Girgixa kai yayi cikin tsananin jimami yace,
Jikinta ya mutu gaba 'daya,
Bazata iya tashiba,
Bazata iya motsiba,
Bazata iya maganaba kawai banbancinta da gawa shine numfashi..
Yanke jiki kawai sukaga mama tayi a sume.
Nurse Dr yakira suka 'dauketa aka nufi emergency da ita.
Ummi ma jikinta rawa ya 'dauka gashi dama yanxu lafiyartata sai ahankali tun rasuwar Ahmed.
Riqeta Jamaal yayi shima idanuwansa a rine sbd alamarin gidansu yafara basa tsoro.
Kallonsa Dr yayi yace,
And one more thing shine wannan alamarin is a serious case sbd allurar laifine saida ita dan haka zamuyi involving hukumar bincike ciki domin agano waya siyeta,gurin wa aka siyota kawai dai ka duba inda kuka 'daukota ka samo mana syringe 'din da akai allurar zamu fara tracing hannun daya riqe syringe 'din.
Ahankali yace,
Yes Dr nima zanyi farin ciki idan akayi hakan sbd alamuran sunfara zama ru'du sosai.
Bayan gari yayi haske ansamu mama ta dawo hayyacinta su ummi suka nufi 'dakinsu