Showing 21001 words to 24000 words out of 36765 words

Chapter 8 - Fadeelah Book 1 Hausa Novel Complete

Fadeelah   

03 Jan 2025

246

take ji. Mahaifiyar Fadila bata tanka mata ba haka ta gaji da tsugunno k'arshe ta tashi ta tafi dan bata da wata mafita wadda ta wuce hakan dan yunwa nagaf da illatata.



Fadila na zuwa office d'in MD ta fara shiga dan gani take ma kamar zai dakatar da ita , inda tun da suka rabu ma ko ya kirata ya ji ya jikinta.


MD da kallo ya bi Fadila ganin yadda ta rame ta yi bak'i , cikin tausayamata ya ce " Ya jikin naki ? " Na ji sauk'i na dawo bakin aiki ne? " Kai MD ya jinjina ma Fadila batare da ya tanka mata ba, sannan ya ce " Shi kenan , kima Jamilu magana "


Fadila ko yadda ta ga abokan aikin nata na kallanta tasan duk sun ji abin da ke damunta. Haka dai ta daure batare da nuna ta damu da kallan da aike mata ba suka gaggaisa, sannan ta nufi office d'insu.


Kasan cewar Fadila ta sanar da Jamilu dawowarta aiki ya sa bai yi mamakin zuwanta ba, saidai ya yi ta binta da kallan mamakin ganin ramar da bak'in da ta yi.


Fadila bayan ta zauna haka ta kwashe kaf matsalar gidansu da halin da take da mahaifiyarta ta sanar da Jamilu.


Jamilu sosai ya tausaya ma Fadila , kud'i ya bata ya ce ta je restaurant d'in kusa da su ta ci abinci.


Abin da ya ba Fadila mamaki lokacin da ta tashi aiki MD ya aiko mata da dubu daya (1000) kamar yadda ya sa bata ya ce ta hau Napep, sosai hakan ya ba Fadila mamaki.



Yanzu Fadila ta koma aiki, aikinta take kamar da , inda a hankaki-ahankali cikin jikinta sai k'ara girma yake. Sannan yanzu rayuwar tasu da sauki tana yin amfani da dubu d'ayan da MD ke bata suna yin cefane .


Saidai tsakaninta da mahaifiyarta har yanzu babu wani sauk'i. Dan har yanzu bata amsa gaisuwarta kuma so da dama sai taita yi mata magana ta yi banza da ita.


Haka rayuwa ta yi ta tafiya har cikin Fadila ya tsufa , yanzu kam duk wanda ya san ciki kallo d'aya zai yi mata ya gane tana da ciki, duk da ta kasance ba mai girman ciki ba.



Rahama TV yanzu hankalin su gaba d'aya ya koma akan taron da za su yi na murnar cikar gidan TV shekara goma da fara aiki. Sosai suke shirin taron wanda za su yi Ranar Asabar kamar yadda suka tsara.



ADAMAWA STATE




Muhammad yanzu rayuwarshi ya ke lafiya lau ya cire duk wata damuwa a ranshi . Yau Muhammad bayan ya dawo aiki ne yana zaune falon mahaifinshi suna fira, mahaifin Mahammad ya ce " Mahammad, yakamata dai wannan Karan ace ka k'ok'arta ka je murnar cikar shekara goma da Rahama TV za ta yi , kodan kasan cewarsa mallaki ga mahaifiyarka, Allah sarki lokacin ta yi k'ok'ari sosai ganin gidan TV ya fara aiki sai dai bai fara aiki ba har sai bayan ranta , dan idan ba zan manta ba sai ta ya yi shekara kusan koma cir da bud'eshi amma ba'a fara amfani da shi ba sai bayan kusan shekara koma, tun da kadawo karatu kullum nake maka magana akan kaje ka ganshi amma kak'i "Muhammad kai ya jinnina ya ce " Daddy, in sha Allah wannan Karan dai zan je, yaushe za'ai taron ? " This coming Saturday" Shi kenan zan yi k'ok'ari inga na je" Tom zan yi magana da Murtala Isa shi ne shugaban gidan TV "



KADUNA GARIN GWAMNA



Yaune ya kama za ai taron Rahama TV , inda Fadila ta shirya ta tafi da wuri duk da bata jin dad'in jikinta sosai , tun jiya take fama da ciwan mara haka dai ta daure ta tafi.



Taro ya yi taro inda taron ya samu halarta manya mutane da dama , daga ciki hadda Muhammad Sagir mai shadda da ya yi tattaki shima tun da ga Adamawa ya zo.


An yi taro angama inda sosai abun ya k'ayatar da Muhammad ,sai dai yadda ya ji ana bada tarihin yadda mahaifiyarshi ta shiga ta fita dan ganin ta bud'e gidan TV , sai dai Allah da ikonshi gidan TV bai fara aiki ba har sai bayan ranta, hakan ya sa Muhammad ya k'udirci taimaka ma gidan TV ganin ya d'aukaka yafi da haka.

Bayan an gama taron ne aka gabatar da Muhammad amatsayin wanda zai ba ma'aikatan gidan TV Frame na shaidar karramawa. Haka aka fara Kiran d'aya bayan d'aya ana basu har aka zo kan Fadila, wadda ta tashi duk a d'arare dalilin cikinta da ya fito.


Muhammad cikin fara'arshi ya mik'ama Fadila Frame d'inta inda aka d'aukesu photo dai dai zai mik'a mata.



Haka aka yi taro aka tashi, bayan taro ya tashi ne Muhammad ya yi ma MD magana akan yana so ganin lungu da sak'o na gidan TV. MD Fadila ya Kira a waya ya ce ta samai a office d'inshi, bayan ta zo ne ya ce " Fadila, ki zagaya da shi ko ina na gidan nan " Fadila cikin daurewa da ciwan marar da take ji ta tafi.


Muhammad tashi ya yi ya bi Fadila , duk in da suka je Fadila za ta yi mai bayanin wajan. Inda Muhammad ke jinjina kai kawai ba tare da ya tanka ba.


Fadila d'akin da suke gabatar da shirye-shiryensu ta kai Muhammad ta ce " Nan ne muke gabatar duk wani shiri da muke yi " Muhammad kallan Fadila ya yi yana mamakin yadda ba sai ya tambayeta ba take mai bayanin duk in da suka je kuma takan yi mai gamsassan bayani da ba sai ya naimi k'arin bayani ba.


Muhammad kallan Fadila ya yi ya ce " Ke awana b'angaran kike ?" Fadila shiru ta yi ,dan yanzu takan ji ma kunyar fad'in b'angaran da take aiki akai,haka dai ta daure cikin sanyi ta ce " Ni ce shubatar Shirin DARAJAR 'YA MACE " Wonderful " Muhammad ya ce , sannan ya ci gaba da cewa "Wata matsala ce kuke fuskanta ? Sannan me ye kike ganin zai k'ara d'aga darajar gidan TV nan dan na yi sha'awar bada gudinmuwata? " Fadila da mamaki ta d'aga kai tana kallan Muhammad , take kuma ta kauda mamakinta dan shi d'in ya yi kama da wanda zai iya hakan"
Fadila magana zata yi ta kasa jin yadda mararta gaba d'aya ta murd'a , dama kuma dauriya kawai take dan tun jiya take jin hakan. Fadila da sauri ta duk'e a wajan tana mai dafe mararta tana cije baki.


Muhammad da mamaki ya kalleta ya na tambayarta " Lafiya ? "Fadila da kyar ta iya bud'e baki ta ce " Cikina " Subhannallah baki da lafiya ne ? " Fadila zuwa yanzu ba ta iya magana , durk'ushewa ta yi awajan ta rik'e marar katakam.


Muhammad juyawa ya yi da niyyar ya yi ma MD magana, sai dai kafin ya d'aga k'afar Fadila tsabar azaba da ta ji ta rik'e mai k'afa d'aya katakam, tana jijjiya kai dan na kud'ace gadan-gadan ta taho ma Fadila.


Muhammad rasa yadda zai yi ya yi yana son zuwa ya Kira MD amma Fadila ta rik'eshi bada wasa ba. Muhammad Kiran MD ya yi awaya ya sanar da shi halin da Fadilar take.


MD da sauri ya nufo inda suke , yana zuwa ya kalli Muhammad ya ce " Da'alama na k'uda take aihuwa zata yi " Haihuwa kuma ? Shi ne ta zo aiki kuma ? "


Jamilu da yaga lokacin da Fadila da Muhammad suka wuce yanzu kuma ga tahowar MD da sauri tashi ya yi ya nufi inda suke dan shi gaba d'aya ya fara zargin MD akan cikin Fadila .



Jamilu koda ya je ya ga halin da Fadila ta ke ciki cikin rud'ewa ya yi kanta. Tsawar da MD ya yi masa ce ya sa ya fasa kamata d'in da ya yi niyya.


Muhammad kuma kallan MD ya yi ya ce " Ku kira mijinta mana ku sanar da shi halin da take ciki ? " MD shiru ya yi baitanka ba, sai zuwa can ya ce " Da akwai wata asibiti nan kusa bari in je in taho da d'aya daga cikin likitocin su dubata.


Muhammad da Jamilu nanan kan Fadila da ke ta cije-cije a wajan , kuma har yanzu rik'e take da k'afar Muhammad.


Muhammad da mutum ne mai tausayi sosai kallan Jamilu ya yi ya ce " Ku kira mijinta mana " Jamilu shiru ya yi dan bai san amsar da zai ba Muhammad ba, kuma hakanan ya ji baya buk'ar sanar da shi Fadila bata da miji.


Muhammad sunan tsaye MD ya zo da likitoci biyu mata.


MD da ya fara rud'ewa da yadda ya ga Fadilar ya ce " Ku kamata mu tafi asibitin mana " D'aya daga cikin likitocin ta ce " Nak'udarta ta riga ta kankama zata iya haihuwa a mota muna tafiya sai dai mu bari ta haihu a nan ✍🏻



SANARWA : Ba zan yi posting weekend ba , sai ranar Monday za ku jini in sha Allah.



πŸ“š FADEELAH πŸ“š

πŸ””πŸ“š
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATIONπŸ“š*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo

πŸ’ͺ🏻J.A.W πŸ’ͺ🏻


Na
Fadila Sani Bakori


SANARWA : Masu tambaya akan gyaran jiki akwai hanyoyi kala daban-daban da zan kawo musu na gyaran jiki acikin wannan littafi mai suna FADEELAH.




*🀝 SDEENDTM DATA SERVICES🀝*
*MTN* . *Airtel*
1GB = ₦300. 1GB = ₦300
2GB = ₦600. 2GB = ₦600
3GB = ₦900. 3GB = ₦900
4GB = ₦1200. 4GB = ₦1200
5GB = ₦1500. 5GB = ₦1500

*GLO* . *9MOBILE*
1GB = ₦350. 500Mb ₦250
2GB = ₦700. 1GB ₦500
3GB = ₦1050. 2GB ₦1000
4GB = ₦1400. 3GB ₦1500
5GB = ₦1750. 4GB ₦2000

*VALIDITY: 30DAYS/1MONTH*
For cable subscription or sell recharge card
Call this number or whatsapp
πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½
*πŸͺ€08066268951*



Page 9


MD da ya fara rud'ewa da yadda ya ga Fadila ya ce , "Ku kamata mu tafi Asibiti mana? " D'aya daga cikin likitocin ta ce " Nak'udarta ta riga ta kankama zata iya haihuwa a mota muna tafiya sai dai mu bari ta haihu a nan " Tana fadin haka ta kalli MD ta ce " Ku d'an bamu waje "


MD da Muhammad da Jamilu duk a tare suka fita.



Duk wani taimako da ya kamata sun ba Fadila anma bata haihu ba, hakan ya sa d'aya daga ciki ta fito ta zo ta samu MD ta ce" Ina jin fa sai dai mu tafi da ita Asibiti, saboda kan yaron bai gama yowa k'asa ba "


Muhammad da takaici ya cikasa ga haihuwa nan kusa amma tsabar rashin sanin aiki wai sai sun je da ita Asibiti. Muhammad kallan MD ya yi ya ce " Ku sanar da mijinta idan ya amince ni zan amshi haihuwarta " MD shiru ya yi yana kallan Jamilu , kamar mai son tuna wani abu sannan ya ce " babu damuwa ai taimako zakai zaka iya dubata "


Muhammad kallan likitocin ya yi ya ce " Ku muje in gwada muku wani abu "


Tare da Muhammad suka koma wajan Fadilar.


Muhammad koda ya duba ya ga halin da Fadila ke ciki bai tab'a taba fita ya yi ya ce ma MD " Bata da k'arfin da zata iya haihuwa da kanta sai dai ayi mata aiki ( theater) yanzu bari mu k'arasa Asibitin sai ka sanar da mai gidanta kafin nan "



Da taimakon Muhammad da na likitocin mata su ka sa Fadila a motar MD suka tafi.


Suna isa Asibitin aka shigar da Fadila theater room.


Muhammad suna kaita ya juya zai tafi MD ya kamo hannunshi da sauri ya ce " Kasan cewar muna saurine ya sa na kawota Asibitin nan , gaskiya daga gani kamar ma basu da kwararrun likitoci da kayan aiki , idan babu damuwa ka dubata mana, zan yi magana da d'aya daga cikin likitocin Asibitin"

Muhammad da gaba d'aya shima ya raina Asibitin dan daga gani ma kamar basu da wasu kayan aiki , hakan ya sa ya amince saboda hakan nan sai ya ji tausayin mai haihuwar ya ke.



Muhammad da kanshi ya shiga theater room nasu . Cikin kwarewarshi ya yi ma Fadila aiki ya zaro mata baby boy d'inta.



Sannan ita kuma ya yi mata al'lurai masu k'ara kuzarin jiki , sannan aka maidata d'akin hutu.



Lokacin da Muhammad ya fito da yaron da sunan ya ba MD shi sai ya ga baya nan sai Jamilu kad'ai . Muhammad da alamun mamaki ya kalli Jamilu ya ce " Har yanzu wani nata bai zo ba ? "



Jamilu ganin kokarin da Muhammad d'in ya yi akan Fadila , hakan ya sa ya ce " Ranka shi dad'e, bata da aure shi ne dalilin da kaga har yanzu babu wanda ya zo wajanta " Muhammad da mamaki ya kalli Jamilu jin furicinsa amma sai ya share ya ce, " Shi kenan, ni zan tafi " Jamilu da sauri ya ce " Ranka shi dad'e , tabbas Fadila zata so yi maka godiya, idan babu damuwa ka tsaya ta farka ko ka ban numberka in bata dan ta isar da sakon godiyarta gareka " Muhammad kai ya girgiza ya ce " Karka damu na yi mata dan Allah bana buk'atar godiyarta " Muhammad na fad'in haka ya juya zai tafi .


Jamilu da sauri ya kuma cewa " Ranka shi dade, nasan Fadila tana daga cikin halittun Allah musu godiya da son saka ma duk wanda ya taimaketa koda ko kad'anne tom bare kuma kai , tabbas nasan zata shi ga damuwa idan har akace ta rasa hanyar da zata isar da sak'on godiyarta a wajanka " Muhammad kai ya jinjina sannan ya ce " MD na da number ta" Ya na sanar da shi haka ya tafi.



Jamilu ko ganin Fadila zata farka ba kowa kusa da ita hakan ya sa ya yi tunanin zuwa ya sanar a gidansu.

Mahaifiyar Fadila suna zaune da Aisha suna fira da Jamilu ya yi sallama ya shigo. Bayan sun gaisa ne Jamilu ya ce " Mama , Fadila ce ta haihu bayan an yi mata theater an ciro yaron , yanzu haka tana nan Asibitin sawa , shi ne na zo in sanar ko Aisha ta je gudin karta farka ba kowa kusa da ita " Mahaifiyar Fadila wadda tun da Jamilu ya fara bayani kirjinta ke dukan uku-uku . Hannuta ta d'aga sama tana godiya ga Allah tana cewa a cikin rawar murya mai son fidda kuka " Alhamdulillah ! Allah na gode maka da ka amsa rok'ona kasa Fadila bata zubar min da wannan bak'in jinin anan ba " Mahaifiyar Fadila mai da kallanta ga Jamilu ta yi ta ce " Allah ya raya abun da ta haifa ya kuma bata lafiya , amma babu wanda zai je acikinmu " Mahaifiyar Fadila ta fad'i maganar tana goge hawayan da ke zubar mata.



Jamilu shiru ya yi dan ya rasa abun cewa ,sai zuwa can ya ce " Mama , dan Allah ki y....." ? Mahaifiyar Fadila d'aga ma Jamilu hannu ta yi ta ce " Jamilu , sai an jima ka sanar da ni haihu tom na yi mata addu'a da ita da abun da ta haifa , tom sai me ye kuma ya rage ? " Ta fad'i maganar da alamun ranta a b'ace yake.

Jamilu tashi ya yi bai kuma cewa komai ba.


Har ya tafi mahaifiyar Fadila ta ce " Ka sanar da ita katta dawo min nan bana buk'atar kara zama da ita "


Jamilu ganin idon mahaifiyar Fadila ya rufe ya sa bai k'ara cewa komai ba ya tashi ya tafi.


Aisha k'anwar Fadila goge hawayanta ta yi ta ce " Mama , ki yi hak'uri ki bar Aunty Fadila ta dawo nan ta zauna , idan kin koreta ina zata ? "


Mahaifiyar Fadila cikin kuka ta ce " Aisha , zuciyata ba zata iya jurewa ba inga Fadila da yaron shege tana raino , ina ba zan iya daure haka ba , ku yi hak'uri karku sake rok'ona wata alfarma akan Fadila ta zauna , idan kuma kun matsa sai dai ni in bar muku gidan "

Aisha shiru ta yi bata k'ara cewa komai ba.


B'angaran Fadila ko lokacin da ta farka ba kowa kusa da ita . D'akin ta bi da kallo, daga gani dai Asibiti ne hakan ya sa ta shafa cikinta da sauri sai jin shi ta yi wayan ba komai. Fadila cikin jin dad'i ta ce " Alhamdulillah . Allah kai ne abun godiya Allah na gode maka " Fadila ta fad'i maganar tana goge hawayan da ke zubar mata dan ita ta yi tunanin cikin da ke jikinta ya zube ne .
Fadila na a wannan halin ne d'aya daga cikin likitocin da suka dubata ta shigo ringume da jaririn yana kuka.



Fadila d'aga kai ta yi tana kallan Jaririn da ke a cikin tsunma a hannun likitar. Fadila cikin rud'ewa da ganin jaririn ta ce " Jaririn waye ? " Murmushi likitar ta yi ta ce " Jaririn da kika haifa kenan, amsarshi ki shayar da shi" Ta fad'i maganar tana d'ora ma Fadila jaririn akan k'afarta.



Fadila duk'ar da kai ta yi tana kuka sosai ta kasa magana. Likitar ko dama ta riga ta gama fahimtar Fadila babu aure ta haihu , hakan ya sa ta ce "

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login