Showing 6001 words to 9000 words out of 34734 words

Chapter 3 - Kulsum Book 2 Complete Hausa Novel

23 Sep 2025

519

shi ya ce,
“Sakeenah fa ba ta dawo ba?”
Ta ce, “Ai ba ta jima da fita ba ma”.
“O.K”. In ji Engnr. Farouq sannan ya juya ya dau abin da ya dawo da shi ya fita ya sake komawa ofis.
Sai karfe daya Dr. Sakeenah ta dawo, yaran suka rungume ta suna mata oyoyo! Kulsumu ta karbo jakar hannunta zuwa dakinta, ta ce, “In ce ko ba ku yi wa Aunty Kulsumu rigima ba?”
Har suna hada baki wajen cewa, “Ba mu yi ba Mummy, ta dafa mana noodle da egg mai dadi mun ci mun koshi”.
Ta dubi Kulsumu da fara’a ta ce, “Good, na ga alama Kulsum kina da kokari. Na gode sosai”.
Dan murmushi ta yi ta ce, “Lah Aunty me na yi na godiya?”
Ta ce, “Kula da yara mana, bari in yi girki sai mu samu mu zauna. Amma tare za mu shiga kitchen din”.
Tare suka shiga madafin tana ba ta kananan ayyuka tana taya ta, tana yi tana mata bayanin komai. Nan ta fahimci Kulsumu yarinya ce mai saurin daukar abu dakaifin basira, kuma ba ta da kauyanci duk da cewa daga kauyen ta fito. Komai ta gwada mata sau daya ta gane, har tambayoyi ta ke yi mata, wannan duka zan yanka ko ya ya? Ana motsawa ko ba a motsawa? Maggi dunkule guda nawa za a zuba? Da haka har suka gama girkinsu mai rai da motsi.
Sakeenah ta ce ta dauki warmers din ta jera a dinning ta je ta yi sallah, sai ta zo ta dau abincinta ta ci. Ita sai mijinta ya dawo za su ci tare.
Dr. Sakeenah ba ta samu zama da Kulsumu officially ba sai washegarin ranar sabida Kulsumu ta kara sakewa da ita sosai, kuma ta samu hakan, don cikin kwanaki biyun da suka yi tare Kulsumu ta saki jikinta da Sakeenah sosai. Yau da dare wajejen karfe takwas ta shigo dakin nata, ta yi sassaukar kwalliya sai kamshi ta ke da alama mijinta yana gida.
Kodayake ta lura ko ba ya nan Dr. Sakeenah kullum cikin ado da kamshi ta ke, dazu ta ba ta wasu (deo sprays) masu sanyin kamshi har guda uku ta ce ta dinga amfani da su. Ta tadda Kulsumu na gyara kayanta da ke cikin trolley tana jera su a wardrove don Dr. ta gaya mata komawarta Abuja ba rana. Da sallama ta shigo, Kulsumu ta amsa.
Ta ce, “Aiki ake ta yi ne Kulsum?”
Ta yi murmushin ta mai kyau, har dimples din suka lotsa cikin kumatunta sosai, ta ce, “Kayana nake mayarwa wardrove zan fi jin saukin daukansu a can”.
Sakeenah ta zauna a gefen gadon tana bude kofofin hancinta sosai ko za ta ji sauyin atmosphere a dakin, amma ba ta ji ba. Kulsumu tana kula da kanta sosai da muhallin da ta ke zaune, ba ta bari a ji wani sauyin atmosphere ko ya ya a tare da ita mai alaqa da lalurar ta.
Dr. ta ce. “Bar aikin ki zo mu yi magana mai muhimmanci in mun gama sai ki ci gaba”.
Ta ajiye rigar da ta dauko ta dawo gefen Sakeenah ta zauna, ta kuma tattara dukkan hankalinta ta mika mata.
“Tun yaushe ki ke yin fitsarin kwance?”
Ta sunkuyar da kai cikin jin nauyi.
“Abin da zan iya tunawa gaskiya tunda aka haife ni”.
Dr. ta ce, “Kamar ya ya ki ke ji kafin ki yi shi?”
“Mafarki nake na tsugunna a toilet zan yi, daga nan sai kawai in ji ni cikin laima”.
Dr. Sakeenah ta dan kura mata ido, sannan ta nisa ta ce, “Kulsum sunan matsalarki a kimiyyance 'NOCTURNAL ENURESIS’. Ana kuma kiran sa 'bed-wetting' da harshen turanci. Wasu tun haihuwa sai sun girma suke dainawa. Treatment din sa guda biyu ne; pharmacological and non-pharmacological. Na farko da zan dora ki akai 'is non-pharmacological' ni da ke za mu hada gwiwa mu yi shi.
Da farko dai daga karfe shidda na yamma kar ki kara shan ruwa ko wani abu mai ruwa-ruwa. Sannan kafin ki kwanta ki tabbatar kin yi fitsari. Da tsakar dare zan dinga zuwa na tashe ki ki je ki yi fitsari, sai kuma da asubah na sake zuwa na tashe ki ki je ki yi. A hankali system din jikin ki zai saba da hakan, zan saita alarm da zai dinga tashi na ina zuwa tashin ki at interval. In ya ki bari bayan watanni kamar biyu zan yi referring dinki ga 'kidney and bladder specialist/nephrologist' akwai maganin da za su rubuta miki bayan sun yi examining din ki”.
Kulsumu ta gyada kai cikin fahimta, Dr. Sakeenah ta kara da cewa, “Muna fatan ya tafi after this non-pharmacological treatment, ba sai mun kai ga shan maganin ba”.
A sanyaye ta ce, “Insha Allahu Rabbi”.
Dr. ta ce tana mai mikewa tsaye, “In kin gama jera kayan sai ki je ki yi fitsarin ki kwanta, Allah ya tashe mu lafiya”.
Ta amsa da, “Ameen Aunty, nagode”.

*** *** ***
Tun daga wannan ranar suka fara wannan excercise din, Sakeenah ba ta yi kasa a gwiwa ba, kuma ba ta kuskure wa wajen tashinta a kan lokaci sau biyu cikin dare da kuma asubahi ta je ta yi. In ta bushi iska kuma ta zaga gari da ita ta ga garin Lagos ta yi mata sayayyar kayan amfani tare da su Walid. Hajiya na kira akai-akai ta ji development (cigaban) da ake samu haka Goggo, Dr. Sakeenah na yawan kiranta ta hada su a waya, har Baffa ma in yana gida. Kulsumu sai kara mulmulewa ta ke boyayyen kyawunta na bayyana sarari. Garin Lagos ya karbe ta har fiye da Abuja.
Dr. Sakeenah ta samu aiki da Lagos Specialist Hospital, don haka zamanta a gidan sai ya karanta. Duk hidimomin gidan da kula da su Waleed sai ya dawo kan Kulsumu. Ba ta da kiwa ko kadan da jikinta da zuciyarta ta ke taimaka wa Dr. Sakeenah. Wannan ya sa ta shiga ran Sakeenah sosai, ta kuma dage wajen koya mata duk abin da zai amfane ta, kama daga girki, tsafta, turanci da sauransu. Da daddare sukan zauna duk gidan su yi hira kafin lokacin kwanciya barci, amma Kulsumu ba ta sakewa sam in Engnr. Farouq na wajen, Dr. Sakeenah kuma ba ta barinta a daki ita kadai in har suna gida sai ta takura mata ta zauna a cikinsu. Ta kan ce,
“Kulsum in kin tafi zan yi kewarki!”.
Rabon da ta yi fitsari cikin barci har ta manta. Ita kanta a jikinta tana jin ta fara samun lafiya, ko ko ta ce ta samu lafiya daga lalurar fitsarin kwance. Duk da haka basu bar fargabar ko zai dawo ba.
Ilai kuwa, bayan wata biyu da rabi suna murna lafiya ta samu kawai rannan ta kuskure bacci ya dauketa ba tareda ta je ta yi fitsarin ba, ai kuwa ba'a jima ba ta ji ta cikin danshi.
Washegari hankali tashe ta gayawa Dr. Sakeenah, inda ba bata lokaci tace ta shirya su wuce asibiti tare. Asibitin da take aiki ta kaita, da kyar suka samun appointment na ganin 'kidney and bladder specialist' wanda shi kadai ne duk fadin asibitin. Kuma visiting Doctor ne a wata sau daya yake zuwa, sun yi sa'a sanda suka samu appointment saura sati daya ya zo asibitin.
Ranar da suka samu ganin nephrologist din ya dade yana yiwa Kulsumu tambayoyi, ta dinga amsawa da taimakon Dr. Sakeenah. Ya ce da Sakeenah "urinary incontinence (another medical name for bed-wetting) among adults is now rampant. Wato lalurar fitsarin kwance ga manya matsala ce da ake samu sosai yanzu. A karshe ya hada ta da wasu magunguna (tricyclic antidepressants) wato tofranil (imipramine), da kuma DDAVP (desmopressin acetate) bayan series of gwaje-gwaje, wadanda Kulsumu zata dinga sha based on prescription. (A bisa ka'ida).

In ta zauna sai ta yi ta tunanin wahalhalun da kakanninta suka yi shekara da shekaru suna sha wajen nema mata lafiya, yawo tsakanin kauyuka bukkokin masu magani, ashe ciwon ta maganinsa na asibiti ne Allah bai taba ankarar da su ba. Domin tuni jikinta ya saba da system din da Dr. Sakeenah ta dora ta a kai kuma yana karbar medication din da take sha babu kuskurewa. Cikin ikon Allah suna saka ran ingantacciyar lafiya ta samu ga Kulsumu.
Wasa-wasa yau ta kwashi watanni hudu gidan Sakeenah, Hajiya Nasara ta yi-ta yi Sakeenah ta dawo mata da Kulsumu, tunda ta tabbatar mata ta samu lafiya kamar yadda babban likitan ta ya tabbatar mata a ziyarar karshe da suka kai masa amma Sakeenah ta ki, kullum da uzurin da ta ke bai wa Hajiyar. A zahiri kuwa ta saba da Kulsumu ne, ba ta son rabuwa da ita. Ita ma Kulsum ta saba da Sakeenah da yaranta sosai, amma ta fi so ta koma wajen Hajiya ko sabida Nasma, sun saba sosai kullum suna tare a wayar Sakeenah. Rannan da Nasma ta bugo mata waya, Dr. Sakeenah ta kawo mata daki, sai ta ce,
“Ni dai bari in dauki salary dina, waya zan saya miki, ko kwa bar ni in huta ke da Nasma”.

Nasmah ta gaya mata hutunta ya kare cikin satin nan za ta koma makaranta.

“I will be calling you when I get back to Nottingham. I wish you all the best Sis".
(Zan din ga kiran ki idan na koma Nottingham. Ina miki fatan alkhairi).

Wannan ce sallamar su ta karshe da Nasmah, kafin ta bar gida Abuja zuwa U.K.
*****

Dr. Sakeenah ta cika alkawari, tana daukar albashinta ta saya mata ‘yar karamar waya samfurin Siemens, zo ki ga murna wajen Kulsumu. A ranar Goggo da Baffa suka san ta yi wayar kanta, domin kuwa raba dare suka yi suna hira.
Washegari kuma ta kira Nasmah, “Nasmah albishirinki, Aunty Sakeenah ta saya min waya”.
Nasma ta ciji yatsa, “Shi ne ta riga ni? Ya Taufeeq na tahowa wannan satin, na ba shi waya mai kyau ya kawo miki”.
“Allah sarki Aunty Nasma, ke da Aunty Sakeenah ban san wa ya fi kirki ba. Kada ki damu, zan aika wa Babana daya ‘Yalleman, ni kuma in yi amfani da daya, ba ki yi asarar kudinki ba. Na gode ‘yar uwa”.
Cikin ranta ta ke tambayar kanta, tsakanin Hajiya Nasara da ‘ya’yanta wa ya fi son kyautata mata???

*** *** ***

UNIVERSITY OF READING, UK
Yana sanye da bakaken Japanese suit, ya daura farar rigar likitoci a kai, baki ne dogo, tun da can ba shi da kiba kamar yadda ba shi da rama. A duniya akwai kyayawan bakar fata wadanda kyawunsu kan sanya nationality dinsu cikin kokonton daga kabilar da suka fito. Hakika wannan matashi yana cikinsu, domin kai tsaye ba za ka gane daga kasar da ya fito a (Africa) ba in har ba shi ya bude baki ya fada ba.
A babban dakin taron malaman jami’ar 'Reading' wato ‘seminar room’ duk ciki su biyu ne bakar fata.
Dakin Seminar din a cike yake da malaman jami’ar daga tsangayoyi daban-daban na faculty of medicine. Kowanne daga ciki yana wakiltar tsangayarsu ne (delegates). Babban teburi ne mai tsayi da fadi wanda aka zagaye da kujeru, a gaban kowanne delegate dan karfe ne mai dauke da sunan mamallakin kujerar da sunan tsangayar da yake representing hadi da matakin ilminsa. Tattaunawa suke a kan sabuwar tsangayar da za su fitar cikin faculty of medicine na jami’ar ta 'Reading' wanda a baya babu shi a jadawalin koyarwar jami’ar, wato Ophthalmology Department (tsangayar karatu a kan likitancin ido), sun kuma cimma matsaya guda a karshen tattaunawar tasu.
A lokacin da suka rufe tattaunawar kowa ya mike ne don barin dakin taron abun ya faru kamar yadda ya saba faruwa da shi lokaci zuwa lokaci. Yana mikewa kansa ya sara, mummunar sarawa, jiri ya debe shi, gumi ya lullube shi. Daga nan kuma bai san abin da ya sake faruwa ba, sai farkawa ya yi ya samu kansa a gadon asibiti.
A gefensa babban amininsa ne, wanda suka fito kasa daya, wato Abdul’Ahad Maikano zaune a daidai saitin kansa ya kura masa ido. Ruwan da aka makala masa a jijiyar hannunsa ya bi da kallo kamar mai kirga saukar kowanne digo na ruwan zuwa cikin jikinsa. Amma a zahiri ba ruwan yake kallo ba, innocent and naïve fuskarta ce ta ke gilma masa. Wani mummunan scene da ya kasa bace masa, a rana ta karshe da ya tsallake ya barta, bayan ya karbe mata alfarmarta cikin wani yanayi da duk mai imani ba zai yi irinsa ba. Muryar ta ce ke yi masa amsa-kuwwa cikin roko, tana rokonsa da ya tausaya mata, al’amarin da ba shi da maraba da rape ban da igiyar aure da ta lullube shi.
Tun daga ranar kuma, har izuwa inda yau ke motsi, bai zauna lafiya da zuciyar sa ba, bai samu farin cikin da yake hasashen samu in ya guje ta ba. Ya samu cikar kowanne cikin burikan sa, amma ya kasa samun kwanciyar hankali, zuciyar sa kuma ba ta huta ba. Wani irin maganadisu ne ke jan zuciyar tasa zuwa gare ta...., da wani irin extraordinary feeling mai wuyar fassarawa.
Feeling din da har gobe bai san ma'anar sa ba, bai gaya wa wani ba, balle ya samu fassarar sa.
Ya san dai daga ranar zuciyar sa ba ta kara hutawa ba. Ruhin sa bai bar azabtuwa ba da tunanin ta. Girman laifin da ya san ya aikata mata kuma, daga ita har iyayen sa, ya hana shi samun karfin gwiwar komawa gida ya fuskanci iyayen sa. Sannan tunaninta ya ci gaba da yi masa dabaibayi irin wanda ya hana shi jin dadin komai.

Ga dai ilmin da ya fito nema ya samu yadda ya kamata, wanda a take bayan kammalawar sa jami’ar ta dauke shi aiki a Teaching Hospital dinta amma duk da wannan achievements din, ya kasa samun farin cikin da ya kamata ya samu. Ya kuma kasa samun contentment din da ya kamata mai nasarar rayuwa irin sa ya samu.
Girman laifinsa ga iyayensa da kullum yake hangowa, ya hana shi zama lafiya yaji dadin nasarorin nasa; sun yi masa gatan da yake ganin takurawa ne a gare shi, ya bula musu kasa a ido ta hanyar kin komawa garesu, tare da kin waiwayar wadda ta kasance a karkashin alfarmarsa. Ga shi sakamakon hakan yawan tunani da damuwa ya haifar masa da ciwon kai na barin kai guda (migraine) wanda a duk lokacin da ya tasar masa, sai ya fidda shi daga hayyacinsa, kuma sai ya sha drip a asibiti.


“Are you okay Man?”

Abdul’Ahad ya tambaye shi.
Lumshe idanunsa ya yi daga kan ruwan da ya daura su ya kasa daukewa. Abdul’Ahad ya kama hannunsa na hagu wanda babu ruwan a jiki.
“You better be careful da lafiyarka Aboki (sunan da yake kiransa), Dr. Andrew ya ce kana tsanantawa kwakwalwarka tunani ne, shine silar migraine din ka, as a medical doctor ba sai an tsaya gaya maka illolin hakan ga lafiyarka ba. Har gobe ba ka dauke ni yadda na dauke ka ba Aboki, ba sai ka yi haka zan san ba ka yarda da ni ba. Sannan ban kai matsayin da zan zamo amini a gareka ba.
Ka ki gaya min damuwar ka ta shekara da shekaru. Tunda muka zo a haka nake ganin a. Ni ba abin da ba ka sani a kaina da iyayena ba, amma har gobe ban san komai a kanka ba. A kalla in ka gaya min damuwarka ko ban yi maka maganinta ba, zan ba ka shawara, shawara wadda in ka bi ta za ka samu sassaucin damuwarka. Na yi-na yi ka hada ni da mahaifanka ko sau daya ne mu gaisa a waya tsayin shekarun nan Aboki, ka ki yin hakan. Kullum da uzrin da zaka bani. Har yau ba ka yarda da ni ba ne, ko kuwa ba ka ba ni matsayin aboki na gaske ba?”
ABUBAKAR (TURAKI) ya sake lumshe kyawawan idanunsa. Duk inda ake neman aboki na gari, to Abdul’Ahad ne. Ya rungume shi kamar dan uwansa na jini tun zuwansu garin (Reading Barkshire). Ba wai bai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login