Showing 60001 words to 63000 words out of 115623 words
Ni ban san a ina Auta ta kwaso mana ita ba. Baka san abinda tai ba da baka tare ni ba. Abinci na bada a kai sashen Hajiya Babba da magungunanta kafin naje na bata shine na tadda shegiyar yarinyar nan ta amsa a hannu masu kuka da ita tana floshing ɗin tables ɗin a cikin toilet saboda ita cikakkiyar ƴar iska ce. Kai dole ne ma musan miya kawota gidan nan yau”. Ta ƙara kai min duka. Kasa motsawa nayi a yanzu. Dan sumar tsaye nayi a wajen da jin kalaman makirci da sharrin da take min. A take idanuna suka ciko da hawaye. Na cije lips ɗina sannan na kallesa. Kansa a ƙasa yake bashi da alamar cewa komai. Sai da na share hawayen da suka ziraro min sannan na ce, “Wlhy ba haka ban...”
Bamm ta buge min baki da ƙarfi har sai da ya fashe. “Dan ubanki kina nufin ƙarya na miki ke nan. Lallai yau kam zanci ubanki a gidan nan. Anya kuwa yarinyar nan keba ƴar leƙen asirinmu bace ba ma? Ba wani ya turoki ba dan ki cutar da mu. Dan Ni ba'a taɓa fitsararriyar ƴar aiki tsagera mara kunya irinki ba anan gidan.”
Cikin tura baki gaba na ce, “To ni dai Mammah ai bamma kowa rashin kunya ba sai wanda ya shiga harkarta. Ni kuma bana son ana min sharri akan abinda banyi ba. Kuma manya idan suna ƙarya mutuncinsu zubewa yake yi”.
Ɗauu naji saukar wani marin mai azabar zafi da yafi na ɗazun a saman fuskata. Tsabar yanda ya shigeni har sai da jina ya ɗauke na wucin gadi. Ina ɗagowa ta sake ɗaga hannu zata ƙara min ya shiga tsakkiyar mu. Cikin silent voice ɗin nan tasa mai cike da ƙasaita ya furta, “Mammah it's enough.”
Babu wanda mamakin jin abinda ya fito a bakinsa bai bayyana a fuskarsa ba. Duk da mafi yawansu sun san ba sabon abun bane gatsa magana kai tsaye daga garesa musamman idan yana a ɓacin rai, sai dai dalilin yin ta yau ɗin ce ta Bama kowa mamaki. Irin wannan tsawa haka. Cike da azabar masifa itama Hajiya Mammah ta daka masa tsawa. “Awwab!! Kana fa jin abinda shegiyar yarinyar nan ke faɗa har kake iya cemin ya isa. Ka barni na dawo da ita a hankalinta idan bata san matsayina a gidan nan ba ta sani da ga yau!”.
Maimakon bata amsa ko barinta dani ɗin sai jinai kawai ya kama hannuna ya fara tafiya. Bani da zaɓin daya wuce bin bayansa. Tsitt falon babu wanda ya sake yin koda tari har muka shige ta hanyar nan data nuna min ranar na kai masa shayi....
⭐💞⭐💞⭐
Rashin wucewar Gwaggo ya ɓata shirinsu Mom. Duk da dai ita dama Ummanta ce ke tausarta. Saboda tafi ganewa ta fito ayima duk wacce za'ayi amma Umman tace a'a subi komai a sannu suma fara sanin wacece yarinyar tukunna. Gefe kuma rashin jin daɗin jikinta ya hanata iya komai. Dan da gaske jinin nata ya hau ga ciwon kai da ƙirji mai tsanani dake damunta...
A ɓangaren Halime amarya sai da aunty Zakiyya ta sakata gyara jikinta tsaff ta kuma ƙara tsaftace mata sashenta sannan ta wuce. Dan haka daga ita har sashen nata banda bulbula ƙamshi babu abinda sukeyi. Tayi fes da ita ƙyawunta da rashin kula ya ɓoye ya sake fitowa sosai. Duk wanda ya kalleta yasan tana cikin farin ciki da walwalar sabuwar rayuwar data tsinta kanta a ciki. Sai dai ta wani sashen zuciyarta rashin ganin Abba tunda aka kawota gidan na ɗan sosa ranta. Dan tun jiyan da suka iso bata sake ganinsa ba. Sai da safen nan da taji muryarsa yana gaida iyayenta dake falo. Tayi zaton zai nemeta amma sai taji shiru. Lokacin da ƴan uwan nata ma zasu wuce taji muryarsa a tsakar gida, sai dai kukan da take yasa batai yunƙurin kallon sashen da yake ba. Tunda kuma suka wuce bata sake jin motsinsa a cikin gidan ba. Ajiyar zuciya ta ɗan sauke a hankali, sai kuma ta taɓe bakinta dan tasan zama ta iya ganin fiye da hakan kodan matar nan tasa a zababbiya. Jifa yanda aketa cin uwar sabada a gidan tun isowarsu jiya, a hakan ma tasan dan bata san itace matar da aka auro ɗin ba ma...
Yanda take ta faman yamutse fuska da taɓe baki ya saka Abba dake tsaye a kanta tun ɗazun kasa daurewa ya saki murmushi. Sai kuma a hankali ya kai zaune kusa da ita yana mai kai hannu ya shafi fiskarta. Tsorata tayi, dan harga ALLAH bataji koda ƙamshin turarensa ba balle motsinsa. Dan haka ta miƙe a firgice zata ƙwala ihu. Da sauri shima ya riƙota yana mai ɗora hannunsa saman bakin nata tare da jawota gaba ɗayanta cikin jikinsa yana faɗin, “Calm dawn Halimatussa'adiyya please calm down ni ne”.
Wata irin nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tare da numfashi a jajjere. Sai kuma taji duk kunya ta baibayeta. Ƙoƙarin zamewa tayi daga jikin nasa ya hana hakan ta hanyar sake matseta da ƙyau a cikin jikin nasa. A cikin kunnenta ya shiga raɗa mata, “Amin afuwa na tsorata amarya ko.”
Halime babu bakin magana dan gaba ɗaya a kunyace take. Sai ma mutsu-mutsu da takeyi na son tashi shiko yaƙi barinta. Dole ta haƙura ta nutsu ganin bafa barin nata zaiyi ɗin ba dai. Sun kai tsahon mintuna goma a haka sannan Abban ya sassauta mata yana sauke tagwayen ajiyar zuciya tare da mannama goshinta da kan hancinta kisses. Ina ma ƙasa ta tsage Halime ta shige ciki dan kunya. Sai dai babu damar hakan dole ta haƙura tana faman cikuykuye kanta a jikinsa.
Yanda take yi ɗin yay matuƙar saka Abba dariya. Dan haka ya shiga tsokanarta da raɗa mata wasu kalamai a cikin kunne da suka sake birkita mata lissafi...
💦★💦★💦
Muna shiga ya sakar min hannu. Ganin yana neman raɓani ya wuce nasha gabansa wani irin kuka mai ƙarfi na suɓuce min. Ƙin kallona yayi, ya sake raɓawa zai wuce ta side ɗin dama ta. Nan ma taresa nayi hannayena duka riƙe da ƙuguna. Tuni na cire duk wani tsoronsa da shakkarsa cike da tsiwa na ce, “Malam wai mi kake nufi da ni ne? Ka maidani gaban iyayena daka ɗakkoni bazan iya rayuwa a wannan gidan da ba'a san darajar ɗan adam ba”.
Tamkar bazai kallan ba sai kuma ya yamutse fuska tare da sake tsuketa. Cikin gadara ya furta, “Ki gayama wanda ya kawoki. Sannan bana son rashin kunya”. Daga haka yay wucewarsa. Wani irin takaici da bakin ciki ne suka sake turniƙe ni. Tuni na shiga kokawar maida hawayen dake neman zubomin. Dole ne fa ayita yau ta ƙare dan bazan iya wannan zaman ƙasƙancin ba saboda ni ba jaka bace ba. Bazan taɓa zama a maidani yanda aka maida mahaifiyarsa ba. Kaina tsaye na nufi hanyar da yabi dan idanuna sun gama rufewa da masifa. Babu ko gezau a tare dani na bankaɗa ƙofar farko dana gani a wajen. Sai da zuciyata ta jijjiga saboda karo da abinda banyi zato ba. Da sauri na juya masa baya ina mai rumtsewa da ƙarfi, jikina har rawa yake dan tunda nasan kaina ban taɓa ganin namiji babba a yanda yake yanzu ba. Su Yaya Musaddiq ko da boxer da singlet basa zama a gida. Balle kuma ace daga su sai pant kamar yanda yake. Gashi a tsaye ƙyam da suffar ƙarfi dogo masha ALLAH. Bazan iya kallon wannan abin kunya ba, dan haka na fara laluben hanyar komawa inda na fito cikin sassarfa, amma sai hakan ya gagara. Maimakon kama handle ɗin ƙofa da nake lalube sai na damƙi lallausar fata mai santsin tsiya. Da sauri na cire hannun nawa tare da daka tsalle baya ina buɗe rumtsatstsun idanun nawa. Idanu huɗu mukai da shi, tsabar rashin kunya kuma yana a yanda na gansan. Sake juya baya nayi da sauri jikina na rawa. (Wannan wane irin fitsararren mutum ne haka wai) na faɗa a zuciyata ina ƙoƙarin riƙe numfashina da tsumar da jikina keyi........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
.......A bazata naji saukar muryarsa cikin kunnena.
“Ba abinda kika zo gani ba kenan?”. Ya faɗa a hankali cikin daƙilalliyar muryar nan tasa. Bamma san lokacin dana juyo a fusace na ce, “ALLAH ya kiyaye sai kace wata ƴar iska. Kuma ni ka bani hanya na wuce”.
Maimakon bani hanyar ko tanka min sai ya shiga matso ni. Baya na farayi hankalina a tashe, idanuna na fitowa gaba ɗaya waje. Shi kuma bai fasa biyonin ba har sai da muka dangane da ƙaton gadonsa dake a dunƙule tamkar zero. Ganin baida alamar dakatawa na faɗa saman gadon idanuna cike da ƙwalla. Gaba ɗayansa ya ranƙwafo kaina yay min runfa hannayensa duka biyu dafe da gadon ta gefe da gefe na. Kaina na shiga girgiza masa idanuna cike da hawaye. Kafin na buɗe baki da ƙyar cikin ƙarfin hali na ce, “ALLAH zan maka ihun da kowa na gidan nan sai yazo sashen nan”.
Wani lalataccen murmushi ya saki da ɗage gira ɗaya sama. A hankali ya sake matso da furkarsa gab da tawa. Ai babu shiri na ƙanƙame jikina tare da rumtse idanuna na kauda fuskata gefe. Amma duk da haka ina jin saukar dumin numfashinsa akan fuskar tawa. Kafin cikin maganar raɗa a cikin kunnena ya furta, “Da kuwa kowa a yau yasan ke ɗin *_MATAR AWWAB EL-MU'AZZ MAASH_* ce. Idan kuma kin cika matsiwaciya dan ALLAH ki gwada ki mana”.
Hannu nasa na ture fuskarsa batare dana buɗe idanun ba, sai kuma na yunƙura zan tashi dan ji nake tamkar an sakani a kuttun man shanu tsabar yanda kusancinmu ya dabaibaye ni. Da sauri na koma ina mai dafe kaina daya bugu da nasa. Tare da buɗe idanuna ina ɓata fuska tamkar zanyi kuka. Shima tashi fuskar a yamutse take hannunsa dafe da goshinsa alamar yaji zafi, ban san sanda na bushe da dariya ba tsabar jin daɗi. Ganin yanda ya zuba min idanu ya sani haɗiye dariyar na ɓata fuska da harararsa na ɗauke kaina gefe.
“Baki da kunya ko?”.
Ya faɗa cikin wani yanayi dana kasa fassarawa. Baki na sake murguɗawa fuskata a gefe a tunanina bai gani ba. Sai jinai ya furta, “Humm harara a duhu ai na mai tsoro ne. Idan kin isa kiyi ido cikin ido ni kuma zan banbance miki tsakanin aya da tsakkuwa. Bani phone ɗina”.
Da sauri na juyo na kallesa danni nama manta da wani batun wayarsa a hannuna. Sai kuma na maida kaina gefe nace, “Ta ƙarfi ce. Kuma ni ka tashi min a kai, wannan ai rashin kun.....” na kasa ƙarasawa.
Bai tashin ba bai kuma tanka min ba. Kusan tsahon mintuna biyu sai da ya mula dan kansa sannan ya miƙe kamar wanda akai ma ishara da hakan, dan da ƴar sassarfa ya bar wajen haƙoransa cije da lips ɗinsa. Ajiyar zuciya na sauke a hankali, har ina kai hannuna na fara ma kaina fifita da shi dan sam ko sanyin acn dake ɗakin baya wani ratsani. Jin rufe ƙofa ya sani zabura, sai naga bathroom ya shiga. Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi sosai tare da miƙewa. Dan gwara nabar masa ɗakin kafin ya fito min a tsirara kuma tunda naga idanunsa ba kunyace a cikinsu ba. Turus na tsaya tamkar zan fasa ihu jin ƙofar a garƙame, a take naji sabon tashin hankali da hajijiya na neman kwasata, dan na fahimci ƙofar ya rufe kenan....
⭐💞⭐💞⭐
Yanda take safa da marwa cikin ɗimuwa a ɗakin zai tabbatar maka da ranta a ɓace yake. Tabbas kuwa ran nata a ɓacen yake. Dan tunda take ba'a taɓa raina mata hankali irin na kwanakin nan ba. Musamman ma yau. Ranar Awwab ya gasa musu magana harda gorin gidan uwarsa ta tursasa kanta shanyewa batace komai ba saboda wani dalili. Yau kuma yarinya ƙarama tai mata rashin kunya da tsallake dokarta shi kuma ya mata tsawa ya kuma hana ta hukuntata. Kowa fa a gidan nan tsoronta yake ji, amma har yau a samu yarinyar da zata ƙaryatata a gaban ƴan aiki da ƴaƴanta. Lallai sai ta ajiye lesson mai ƙarfin gaske akan yarinyar nan. Kai hatta da Awwab bazata ƙyale ba saboda goyan bayan yarinyar ta fahimci yake yi. Ai ba yau ta fara cin uban ƴan aiki a gidan ba. Kuma ko yana zaune a wajen take yi ɗin ko ɗaga kai ya kalla baya yi ma. Amma ta kula akan yarinyar nan yana neman kawo musu wani sabon salo. Jiba randa Hajiya Babba ta daketa, ɗaukartafa ya dinga yi harda ɗorata a jikinsa yay treating nata da kansa. Kai ita fa gaba ɗaya ma kanta ya kulle.
Waya ta jawo tai kira. Ana ɗagawa ko sallama bata tsaya yi ba ta fara magana cikin damuwar dake tabbatar da ɓacin ranta. Abinda ya faru tun daga randa aka kawo Samraah gidan take sanarma wadda ta kira har zuwa yau ɗin nan. Sai kuma tai ɗan jimm alamar sauraren abinda na can ɓangaren ke cewa. Tsawon kusan mintuna uku kafin ta saki murmushi mai ƙayatarwa, tare da furta, “Kai amma na gode Hajiya Rubayya, Please kiyi maza ki shigo ina saurarenki. Dan wannan shawarar taki na fara jinta a jikina ƙwarai da gaske.” ajiye wayar tai tana sakin dariyar nasara. Sai kuma ta miƙe tamkar ba itaba ta fara zame kayan jikinta cike da nishaɗi. Tana kammalawa tiɓi-tiɓi ko kunyar kanta bata ji ba ta nufi bathroom ɗinta a haka da alama wanka zatayi.....
💞💞💞💞
*_INDIA_*
Kuka take sosai da ƙoƙarin riƙe hannunsa daga haɗa kayan da yake tayi. Sai dai ko kallon inda take baiyi ba balle ya dakata da abinda yake ɗin. Cikin matsanancin takaici da fusata Attahir da ya gama harzuƙa da abinda ke faruwa ya fisge jakar yana mai dakama ƙanin nasa tsawa.
“Mansoor are you mad ne wai?”.
“Yes! I'm. Na ce I'm!. Ba haka kuke son ku ganni ba. Ko ba haka kukafi buƙatar ganina ba?. Nace muku ga wadda nake so, kun rabani da ita batare data ma wani cikinku laifin komai ba. Duk da abin yana min ciwo har yau har gobe ban taɓa ce muku komai ba. Amma hakan bai muku ba kuma sai ace min wai ga mata an ɗaura min aure da ita. Tunda nake da ku na taɓa ce muku ina son wannan yarinyar ne? Wlhy da nayi rayuwar aure da wannan yarinyar gara na shiga duniya. Na gaji da wannan rayuwar haka nan haba. Sai kace ba jininku bane ni, yaya kuke so na cigaba da rayuwa cikin salama ns wa....” kuka ya sarƙesa ya kasa cigaba da magana. Sai ma zubewa da yay a saman gadon yana mai dafe kansa dake sara masa da duka hannayensa biyu, tare da cusa hannunsa cikin sumarsa ya yamutsata.
Sosai jikinsu ya sake yin sanyi. Musamman Mamy da tafi kowa kasancewa a cikin ɗimuwa. Itama zubewa tayi a gaban Mansoor ɗin tare da kamo hannayensa cikin nata tana sake fashewa da kuka. Dad ne da tun ɗazun baice komai ba ya furzar da iska mai kauri daga bakinsa, tare da kai hannu saman kansa ya shafo. Sosai kukan Mamy da Mansoor ke cizon zuciyarsa. Sai dai shi baima san ta inda zai fara ba game da wannan hargitsi daya rasa tushensa balle iyaka.....
Kakarin da Mansoor ya fara ne ya maidosa a hayyacinsa. Kusan a tare shi da Attahir suka zabura kansa. Yayinda Mamy ta sake ɗimaucewa. Yunƙurin amai ya fara sai ga jini bula. Ihu Mamy ta fasa, yayinda Attahir ya fita a guje yana faɗin bari yay kiran asibiti...
Kafin cikar mintuna goma ambulance ta iso. Lokacin da aka fito da Mansoor daga ɗakin hotel ɗin da suke ya gama fita a hayyacinsa. Dama yau kwana uku kenan da sallamosa baya kwanakin kusan wata guda daya kwashe yana jiyya. Samun lafiyar tasa ya saka walwala da farin cikin kowa dawowa a cikin ahalin nasa. Dan nan da kwanaki biyu ma suke shirin komawa gida Nigeria. Sai kuma aka samu akasi Husnah yarinyar Auntynsa da aka ɗaura masa aure da ita a randa aka fasa da Samraah dake Dubai ta ɓaro musu aiki tai kiransa a waya. Kalaman da tayi amfani da su a wajen gaisawar tasu ya sakashi neman fashin baƙi a wajen yayansa Attahir. Shi kuma batare da tunanin komai ba ya buɗe masa zancen cewar ai da gaske Husnah ɗin take an ɗaura mata aure da shi a randa aka fasa da Samraah. Wannan shine dalilin rikicin na yanzu, ga shi kuma da alama aiki ya koma baya.....
🌜🌟🌛
Ina nan tsaye abin duniya duk ya isheni ya buɗe ƙofar bathroom ɗin alamar zai fito. Koda gigi ban yarda na kalla wajen ba balle ma na saka kaina a uku. Har tsawon mintuna uku ina ɗan jin motsinsa cikin yanayin rashin hayaniya. Cikin ƙarfin hali da dakiyar zuciya na ce, “Ni ka buɗe min ƙofa na fita bana son taɓara”.
Shiru babu alamar zai