Showing 36001 words to 39000 words out of 115623 words

Chapter 13 - Tsutsar Nama Book Two Complete Hausa Novel

22 Oct 2025

342

yasan sanadin al'amarin sakamakon Baby data zazzage musu zance. Har an canjama Abba kaya za'a wuce da shi sai ga Nurse a guje yana ƙwala kiran doctor. Kusan dukansu suka afka ɗakin dan azatonsu Abba ya cika, koda Nurse ɗin da doctor suka shigo sun cika ɗakin tare da rufuwa a kansa. Da ƙyar doctor ya samu duk suka fice su kuma suka fara aikinsu.
        Kowa ka gani yana cikin farin ciki da farfaɗowar Abba. Sai kuma fatan ALLAH ya bashi lafiya. Bayan kamar mintuna Talatin kuwa Doctor ya sake musu albishir ɗin farfaɗowar Abban. Sai dai ba'a bar kowa ya shiga wajensa ba sai a washe gari. Alhamdullah jikin nasa da sauƙi sosai, sai dai kansa yasha bandage abin tausayi. Babu wanda yace ma Mom komai duk wani rawar kan dafo abinci da take tana kawowa safe da rana da dare. Shima Abban kuma baya ko kallon inda take duk maganar da zata masa bai amsawa. Dama jiyyarsa Kawu Isuhu ne keyi. Ƙani yake a gurinsa dan ɗan wan mahaifinsu ne. Kwanansa uku aka sallamesa. Ya samu rakkiyar dangi data abokai irin su Alhaji Sadisu.
     Tun isowarsu ya fahimci Halime bata gidan, bai dai ce komai ba har sai da yay wanka ya samu nutsuwa. Falo ya dawo ya kwanta saboda masu shigowa dubasa ƴan nan cikin anguwa. Su Gwaggo Gudidi na zagaye da shi anan ɗin ma. Basu sami lafawar mutane ba sai kusan goma na dare, alokacin ne fa Gwaggo Gudidi ta fara tsiya saboda tayin shiga ɗaki ya kwanta da Mom ta masa. Gwaggo tace babu inda zaije a ƙarasa hakalashi, Musaddiq ya kaisa ɗakinsa yaje can ya kwana. Sosai Mom ta shiga shock, dan batai zaton sun san ainahin abinda ya farun ba, amma sai ta dake ta shiga bama Gwaggo haƙuri da shi kansa Abban wai sharrin shaiɗan ne bazata sake ba. Harda ƴar ƙwallarta kamar yanda Ummanta tace tayi. Fata-fata Gwaggo ta mata a gaban su Musaddiq, sai da ƙyar aka samu tayi haƙuri. Ita dai Mom yau babu bakin magana kuma sai haɗiyar zuciya.....   
      

       💥❤️💥❤️💥

   Bayan sallar isha'i dole na haƙura da batun bin su Bahijja Islamiyya domin amsa kiran Alajah. Muna gaba da shiga sashen Mama Balki ta dakatar dani, cikin nuna kulawa da kwantar da murya ta furta, “Ɗiyata dan ALLAH yau ki danne zuciyarki. Kar ki kula Azizat komi zata miki. Mutanen nan da kike gani sunada rigima sosai, idan aka zo fagen faɗa da bare kansu haɗe yake wajen ɗaukar mataki. Ki ringa haƙuri mu neman arziƙi ya kawo mu. Fatanmu mu samu abin rufama kammu asiri shike nan kawai. Kina ƴar ƙaramarki da ke kar ki biyema wanda suka fi ƙarfin ki kinji”.
          Duk da zantukanta sun tunzurani sai ban nuna ba a zahiri na haɗiye, sai ma jinjina mata kaina da nayi, a hankali na amsa da “In sha ALLAHU Mama komai ya wuce. Ranar ɗin ma akasi kawai aka samu”.
       Cikin nuna gamsuwa da sake lallashina ta sanya min albarka. Daga haka taja hannuna muka ƙarasa shiga ciki. Duk da nasan banjin shakka ko tsoron kowa a raina sai da nayi addu'a sannan na shiga. Da hayaniyar surutunsu yau muka fara cin karo. Kasancewar ta inda muka shigo duk suke a ƙatoton dining yasa sukai min wani farrr cikin ido. A hankali naja numfashi na fesar ina mai karanto (Hasbinallahu wa-ni'imal wakil) a cikin zuciyata. Da farko ba kowa ya maido hankalinsa kammu ba, dan koda mukai gaisuwa bai fi mutane uku suka amsa ba. Ciki harda Alajah data furta, “A'a Mama Balki ba nace sai mun kammala cin abinci ba?”.
      Cike da mamaki Mama Balki ta ce, “Eh da haka kikace Hajiya, amma kuma yanzu da kika kira sai kikace kada mu wuce mintuna talatin shiyyasa kuka taho”.
Sosai mamaki ya bayyana a fuskar Aunty Mama. Harma ta gagara daurewa ta ce, “Ni ɗin?”.
Da girmamawa Mama Balki ta amsa mata da, “Eh” tana murmushi. Kai Alajah ɗin ta jinjina, sai kuma ta furta, “Kuɗan jirani na kammala dinner to please, dan ina son mu ƙarƙare komai a yau tasan aikinta ni zuwa gobe zan koma”.
    Kallon juna Azizat da Arwa suka yi, sai kuma suka saki murmushi suna kashema juna ido ɗaya. “Aunty Mama! Wai waye ake nufin za'a ɗauka aiki anan gidan? Badai wannan mai suffar mamiyo na ruwan ba?”. Kafin ni ko Mama Balki wani yace wani abu Azizat ta faɗa a zafafe har tana wancakalar da spoon ɗin dake hannunta. Kusan atare duk wanda ke'a wajen ya ɗago, a dai-dai nan mayen sirrintaccen ƙamshin turaren Maash kuma ya mamaye wajen. Dan haka hankalinsu ya rabu biyu. Yaran suka shiga gaishesa. Ban ji ya amsa musu ba, dan ban ɗago ba kaina a ƙasa ina ƙoƙarin danne abinda ke taso min akan wannan shegiyar Azizat ɗin. Zungurin da Mama Balki tai min ya sakani kawo nunfashi, na ɗan kalleta. Nuni tai min na gaishesa. Ban musa mata ba a taƙaice na furta, “Barka da dare” a hankali.
      Kamar yanda bai amsawa ƙannen nasa ba nima bai amsa min ba. Dan haka na ɗago kaina cikin takaici, dai-dai yana kaiwa zaune a kujerar da ƙyaƙyƙyawar budurwar da zasu iya sa'anni da Azizat tai saurin gyara masa. Kasancewar kujerar itace ta kamar a ƙarshen table ɗin mu kuma muna daga farko tsaye yasa mukai facing juna. Wani kallon tsana naga Azizat na jefama budurwar, sai kuma ta cije lips ɗinta alamar dai akwai abin faɗa a bakinta amma babu dama. Sai daga baya na fahimci agolar gidan dake kusa da itace ta hanata magana ta hanyar riƙe mata hannu. Alajah ce ta katse yanayin da faɗin, “Azizat wai ina ruwanki da yarinyar nan ne? A kanki zata zauna idan ma anan ɗin zata zauna?”.
     Baki sosai ta tura gaba. Cikin nuna jin haushi sosai ta ce, “Ni dai bana sonta Aunty Mama. Ba kuma nason ganinta dan na tsaneta. Idan kuma har akace a gidan nan zata zauna wataran sai na kasheta. Ta kwana da sanin marin da taimin wlhy sai ta biya bashinsa da fansar ranta....”
          “K! K! Azizat ban gane ba. Mari? Wa ɗin aka mara? Waye kuma yay marin?”. Hajiyar nan da muka samu a falo randa muka zo wadda kuma Bahijja ta tabbatar min itace mahaifiyar Azizat ɗin kuma Yaya ga mahaifin Maash, sannan mai mulkin komai da kowa na gidan ta faɗa a wani irin fusace.
        Kallon Alajah Azizat ɗin tayi, sai kuma ta ɓata fuska tana fiki-fiki da idanu. Da alama dai Aunty Mama ce tai mata gargaɗi. Tsawa mahaifiyar tata ta daka mata. Ba ita ba hatta ni sai da naji hanjin cikina sun wakita. A take kuwa Azizat ta fara rattafo bayanin komai daya faru a ranar da safen dalla-dalla harma da ƙarin gishiri da magi..........✍️


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚_

........Wani irin huci Mahahaifiyar tata take tana kallon Alajah. Idanu Alajah ta rumtse tana ɗan dafe kanta. Sai kuma ta ɗago idanunta akanta. “Please Aunty Nafee relax. Bafa yanda kike tunanin al'amarin b....”
     “Kamar ya ba yanda nake tunani bane Mashi'a! Ƴar aiki ta mari mun yarinya a gabanki amma ki gagara ɗaukar mataki sai ma ki hanata sanar min. Wai ke bazaki taɓa canjawa bane ba. Shike nan nagode, ai kin tabbatar min bake kika haifi Azizat ba. Da Imran ko Sahla ta mara ai da kin ɗauki mataki ko. K!! Kuma zaki ci ubanki. Zan sauke miki rawar kan da kika shigo da shi. Ai dama tun randa tazo dake na fahimci idanunki a buɗe suke irin na marasa mutunci.”
     Idanu na na runtse sosai dan har cikin ƙwaƙwalwar kaina nake jin hargagin nata. Na tabbatar da ace ta kusa da inda take nake tsaye babu abinda zai hanata kai min duka. Abinda ya matuƙar sake bani mamaki shine babu wanda ya iya tanka mata a wajen hatta shi Alhaji El-Mu'azz ɗin. Balle kuma ƙanin nasa ma. Matansu kuwa kawunansu duk a ƙasa kai kace mala'ika ke kansu. Karo na farko na kai idamuna a kansa. Fruit salad ɗinsa yake sha hankali kwance. Sai ka rantse ma baya wajen dan ko sau ɗaya bai kalli kowa ba duk wannan hargagin da akeyi. Hasali ma a dai-dai sanda Hajiya Mammar ko nace Aunty Nafee kamar yanda Alajah ta ambaci sunanta ke faɗin, “Na soke maganar aikinta na farko. Daga gobe zata fara aiki a sashena. Ke kuma Azizat tashi ki rama marinki”. A kusan tare duk wanda ke a wajen ya ɗago yana kallon ta. Yayinda Azizat ta miƙe zaram cike da farin ciki ta nufo inda nake alamar dai zata zo rama marin kenan.
Idanu duk suka zuba min musamman Aalaja da ranta yake a ɓace. Amma shi sai ya ma miƙe abinsa tamkar baiji mima ake faɗar ba. Cike da takun nan nasa mai cike da ƙasaita ya ratsa ta bayansu yazo ta gabana ya gitta kamar ɗazun zai wuce. Wani kalar kallo dana kasa fassarawa ya jefa min....
        “Muhammad!”.
    Alhaji El-Mu'azz ya faɗa dai-dai zai raɓani ya wuce gaba ɗaya.. Amamakina sai naga ya tsaya cak. Tamkar bazai juyo ba sai kuma ya koma da baya tamkar wanda akama dole a hankali ya amsa da, “Yess Paah”.
     Idanu mahaifin nasa ya ɗan tsira masa. Sai kuma yay ɗan murmushi cike da kulawa ya ce, “Ba zaka ci abincin ba kuma? Naga fruit salad ɗin ma kaɗan kasha fa”.
     A daƙile, sai dai cikin sanyin Muryar nan tasa ya ce, “I'm okay Paah. Kaina namun ciwo ina son na ɗan kwanta”.
     Sosai fuskarsa ta nuna damuwa. Hakama sauran duk sai kowa ya maida hankalinsa a kansa musamman Azizat da budurwar nan data gyara masa wajen zama sanda yazo. Dan har wata ƴar zabura sukayi a kusan tare. Cikin jimantawa da kulawa sosai suka shiga masa addu'a. Kansa kawai ya jinjina musu yay wucewarsa ya fice. Sosai zuciyata ke ƙara jinjina rashin mutuncin mutumin nan. Ashe bamu ƴan waje kawai ba hatta family ɗinsa basu tsira da wannan baƙin halin nashi ba. Lallai sai a jinjina masa. Ganin yanda duk suka maida hankalinsu a kansa nasa ƙafa na taɗe Azizat dake ta leƙensa kamar mai son binsa. Razananniyar ƙarar data fasa ya saka kowa zabura sukayo kanta.
     Da wannan damar Mama Balki taja hannuna da sauri hankalinta tashe muka sulale muka fice. Ashe ita taga abinda nayi, suko sai suke tambayar miya faru? Yaya akai ta faɗi. Oho mudai tuni mun ware bamu san yanda suka ƙare ba kuma....

🤣🤣ALLAH ya shiryeki Sam-G.

❤️★❤️★❤️

     “Gwaggo maganar auren nan dama nake son mu tattauna kafin ki wuce. Dan ina son ayi komai a gaggauce cikin watan nan”.
     Cike da ɗunbin farin ciki Gwaggo Gudidi ke kallon Abba dake maganar, ta saki dariya tare da yin guɗa. “Kai kai da ace na iya ghuɗa babu abinda zai hanani tsallarata sama har sai duk ƴan anguwa sunji Imamu. Ka daɗe baka sakani a farin ciki irin yau ba. ALLAH yay maka albarka. Amma ince dai ƴar mutunci ka sama mana ba irin wannan matar taka ba dan bana son a sake yin jifar gaffiyar ɓaidu”.
      Kai Abba ya girgiza yana ɗan murmushi, “A'a Gwaggo in sha ALLAHU sam ba halinsu ɗaya ba. Yarinyar da suka doka ɗin ce dama.”
     “Kai kai to Masha ALLAH. Aiko kayi ƙyan kai, dan hakan da zakayi shine babban murtani da zaka maidawa matarka tasan ka haifu cikin uwa da uba. Amma kuma ai naji yaran na faɗin ta gudu tun a ranar da abin ya faru? Ko kasan inda take ne?”.
           “A'a Gwaggo ban sani ba. Amma dai ta sanar min da garinsu. Nasan kuma insha ALLAHU can ɗin zata nufa tunda Alhaji Sadisu ya bincika daga inda Jalilahn ta ɗakkota ance bata koma can ba. Dan haka nake son muyi azamar bin bayanta tun kafin abin yayi nisa”.
      “Eh to hakan ma dabara ce ai. ALLAH ya bada sa'a da nasara. Yaushe zaku je ɗin?”.
     “Da dai gobe idan ALLAH ya kaimu ne. Sai shi Musaddiq ya jamu dan ni bazan iya tuƙi ba. Alhaji Sadisu ko baida jimirin yin tuƙi a doguwar tafiya sam”.
     Ɗan jimm Gwaggo tayi alamar tunani, dan in bata manta ba Musaddiq ya sanar mata gobe ne zai je gwaji da akace za'a musu a inda aka ɗaukesa aiki. Da ɗan sauri ta girgiza kanta. “A'a inaga shi Jafaru sai ya jaku kawai dan yasan ƴan tumaki sosai tunda shima matarsa ƴar wajen garin ce. Kaga ko ai faɗuwa tazo dai-dai da zama ba sai anta faɗi tashin tambaya ba”.
       Cikin nuna farin ciki da gamsuwa Abba ya shiga tabbatar mata da hakan yayi, ya ɗora da godiya. A take kuma babu ɓata lokaci yay kiran Jafaru ɗin. (Jafaru shine ɗa na biyu a wajen Gwaggo Gudidi. Kusan sa'anni suke ma da Abba dan komai na rayuwarsu tare sukayi. A dalilin Mom tarayyar tasu ta samu rauni. Dan yanda take nuna bata ƙaunar ƴan uwansa su raɓesa duk wanda yazo sai ya tafi da tabon rashin mutuncinta yasa Jafaru janyewa daga jikin Abba. Saboda akwai wani zuwa da yayi Mom ta cimasa mutunci harda ƙwallarsa. Daga lokacin ya tattara Abba ya ajiye gefe sai dai su gaisa sama-sama ta waya ko idan wata sabgar ta haɗasu ta dangi ko in sun haɗu a gidan Gwaggon. Abin na damun Gwaggo amma ta gagara sasantasu, sau yanzu ga dama ta samu kuma)....

         ✨💫✨💫✨💫

    Ko kaɗan Mama Balki batai min faɗa game da abinda naima Azizat ba. Sai ma Sosai yanda ta nuna tashin hankalinta ita da su Bahijja game da batun komawata aiki sashen Hajiya Mammah ya bani mamaki. Dan na sake fahimtar al'amarin babba ne. Duk da kuwa Bahijja ta ɗan bani labarinta a ƙaice ni banga wani abun tsoro tattare da ita ba, idan masifa ce na saba data Mom da ƴaƴanta ai. Sambatu suke sosai da nuna jimantawa har Mama Balki na faɗin na gudu kawai tun ma kafin komai ya faru. Zata saka mijinta ya taimaka min na fita a daren yau.
        Murmushi na saki a hankali duk da kuwa nima ina jin shakkun al'amarin a zuciyata. Sai dai wani sashe na ƙarfafani dan koba komai zan samo labarai. Haka kawai kuma ina son sanin gaskiyar labarin tushen komai. Atake naga fuskokin masu dariya da nuna farin ciki a kaikaice a cikinsu na sauyawa a dalilin murmushin nawa. Nima sai kawai na basar da canja yanayina. Ƙwallar ƙarya nayi ƙoƙarin tarama idanuna. Tare da nuna tashin hankali ina mai roƙon Mama Balki data taimaka min na gudu ɗin... A bazata mukaji an saki tsaƙi, kusan mu dukanmu muka kalli mai tsakin. Ba kowa bace face aunty Kubra. Yanayin shock na gani a fuskar Mama Balki, da alama dai ta fahimci tayi ɓaranɓaramar sakin zancen gaban kowa. Sai dai bata iya cewa komai ba
      Cike da taɓe baki Aunty Kubra ta cigaba da faɗin, “Mama ina baki shawarar ki rufama kanki asiri. Ke dai kinfi kowa sanin halin Hajiya Mammah a gidan nan. Sannan ita ɗin ba ita ta jama kanta ba. Banda kauɗi da rawar kai uwarwa ya kaita marin ƴar masu gida. Jarumta tafi wani a cikinmu da muke haƙurin shekara da shekaru da su ko mi? Kinga yanzu ai ya rage nata ta ajiye kauɗinta da iyayi gefe ta nemawa tsoffinta kuɗin cin tuwo cikin sallama. Idan ba hakaba wataran ba sashen Hajiya Mammah ba Sashen Hajiya Babba zasu kaifafa ko kuma da karnukan gidan nan wlhy zasu haɗata”. Daga haka ta miƙe tai ficewarta tana wani rausaya da girgiza jiki.
      Shiru kowa ya gagara cewa komai, sai shashshekar kukana kawai kake ji. Kusan mintuna biyar Mama Balki tayi ƙarfin halin bama Bahijja umarnin tafiya dani ɗaki na kwanta. Babu musu Bahijja ta miƙe ta kama hannuna. Sai naga itama A'i ta miƙe fuskarta cike da tsantsar damuwa itama ya kama ɗayan hannuna....

       Duk yanda naso rintsawa barci a wannan daren kasawa nayi. Dan komai ya tsaya min arai ne. Duk yanda nake jin rashin damuwa game da yin aiki a sashen Hajiya Mammah ɗin wani sashi na zuciyata na tsoratar dani da nuna min illar hakan, dan na fahimci matar bata da mutunci sosai. Dan duk mai hankali ya auna yanda kowa ke nuna damuwarsa akan batun zai sake tabbatar da bada wasan yara bane al'amarin. Ganin yanda zancen yaƙi barin raina sai kawai na tashi na ɗauro alwala na fara nafilfili. Har asuba ban runtsa ba sai da nayi salla..........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login