Showing 39001 words to 42000 words out of 115623 words

Chapter 14 - Tsutsar Nama Book Two Complete Hausa Novel

22 Oct 2025

339

NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒐𝒏𝒆_


.......Ina idarwa na ɓingire a wajen sai barci. Ban tashi farkawa ba sai da A'i ta tasheni wai Hajiya Mammah na kira na. Yanda take maganar cikin nuna tsoro da damuwa ya sakani tsira mata ido. Sai dai bata bani damar mata tambaya ba ta juya sukuku ta fice tana faɗin, “Kiyi sauri ki shirya muje kar mu sake wani laifin kuma. Dan ga Mama Balki can tasha maruka akan guduwar da kukayi jiya da dare duk da ƙaryar kareki da tayi kan baki da lafiya ne shiyyasa”.
     Sosai naji wani irin masifaffen ɓacin rai. A take ta bududdugin ta motsa (zuciya) na shiga taunar lips da ƙarfi-ƙarfi tamkar zan hudashi. Gaba ɗaya wata irin tsanar matar mai tsananin gaske ta shiga zuciyata. Yanzu dan ALLAH babbar mace kamar Mama Balki ce za'a mara wai. Kai wannan wane irin gidane haka na marasa tarbiyya da girmama mutane. Dan kawai mutum nada dukiya sai akace zai iya taka kowa a yanda yake. Kaicon wannan rayuwa mara fasali da rashin sanin daraja da kimar ɗan Adam.
      A gurguje nayi wanka na shirya cikin Uniform ɗin da A'i ta ajiye min. Koda na fito a falo na sameta tsaye tana jirana. Kallon juna mukayi. Ta ɗan kafeni da kallo sai dai batace komai ba tayi gaba na bita a baya...

💞👉💞👉💞

    “Alhamdullah su Abba sun isa ƴan tumaki lafiya. Tafiyar da Mom bata da masaniya a kanta, dan har yanzu Abba baya shiga harkarta. Ita kuma ta tada hankalinta sunata bibiyar teachers domin sabunta ayyuka akan Abban dan ta lura komai fa na neman canjawa. Kullum cikin ƙaryar fita take duk da kuwa yana gida yana jinya. Bai taɓa hanata ba, kamar yanda Gwaggo Gudidi bata taɓa tanka musu ba. Da tambaya da kwatance suka gano gidan su Halime da ƙyar kasancewar sun sami cikakken address wajen mai kawosu aikatau daga ƙauyen. Wadda da ƙyar suka samu ƙawar Mom ta sanar musu bayan sun danƙa mata kuɗaɗe. Tako kai su amma ta roƙi Abban da kar ya sanarma Mom ita ta faɗa, duk da kuwa ita bata san manufar Abban ba. Ya sanar mata ne kawai zasu bincika idan Halime taje gida kar a samu kuskure tayi wani wajen daban. Ta gamsu ɗari bisa ɗari dan tanama Abban kallon girmamawa duk da tasan aminiyarta ta daɗe da gamawa da shi. Koda yake itama ɗin ta gama da nata mijin ai duk da basu taɓa tarayya da Mom wajen zuwa gidan teachers ba. Kowa nayin al'amarinsa ne a bayan fage..

        Sun ɗauki kusan mintuna talatin a gidan mai anguwa da sukai dabarar fara zuwa kafin Baba da aka aika kira ya ƙaraso. Tun shigowarsa Abba keta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya, dan ko makaho ya laluba yasan shine mahaifin Halime saboda kama da sukeyi matuƙa tamkar yayi kaki ya ajiyeta. Sake gyara nutsuwa Abba yayi, hakan har ya saka Alhaji Sadisu sakin murmushi. Bayan Baba ya gaisa da mai anguwa ya juyi gasu ba. Kafin ma ya gaishesu su sun shiga gaida shi. Dan ko babu batun abinda ya kawosu zai girmesu gaskiya. Bayan an kammala gaggaisawar mai anguwa ya nunama baba su Abba.
       “Malam Yusufa baƙine dama suke neman gidanka. Naso saka yaro ya rakasu sai suka buƙaci haɗuwa da kai anan shiyyasa na aika akayi kiranka”.
    Da ɗan nuna alamun mamaki Baba ke kallon su Abba. Ganin yanda Abba ya duƙar da kansa Alhaji Jafaru ya fara magana a nutsensa. “Ni sunana Jafaru, wannan sai ƴan uwana Alhaji Sadisu da Alhaji Imam. Baba baka Sammu ba gaskiya. Wannan ɗan uwan nawa Alhaji Imam shine mai gidan da ƴarka Halimatu take zaune acan birni.....”
      Sosai Baba ya waro idanu, tare da sakin salati ya ce, “Kai kai Masha ALLAH. Bawan ALLAH ashe baka rasuba Sa'adiyya duk ta kasa zaune ta kasa tsaye. Tunda ta iso garin nan kwana biyar kenan kullum bata da aikin daya wuce kuka. ALLAH mun gode maka”.
           Murmushi Abba yayi cike da jin sanyi a ransa Halimensa ta damu da shi. Murya a sanyaye ya ce, “ALLAH kam shine abin godiya Baba. Nima kuma ina ƙara gode masa da ya zamto gida tayo ba wani wajen ba. Dan muna can hankalinmu duk a tashe da ƙyar aka samo wadda ta ɗauketa daga nan ta bamu address.”
     Sosai Baba ya nuna jin daɗinsa da wannan kulawa. Fuskarsa washe da murmushi shima ya ce, “Ai dama duk tsanani Sa'adiyya bazata nufi ko ina ba sai gida. Nima Nagode sosai da wannan kulawa taku, lallai na yarda da gaske yarinyata tana a hannun mutanen kirki. ALLAH ya kiyaye gaba ya ƙara lafiya”.
    A tare duk suka amsa da Amin. Kafin Alhaji Sadisu ya ɗora da bayani bayan sun ɗan yi jimm na wani lokaci. “Baba dan ALLAH idan bazaka damu ba muna neman wata alfarma ne”.
      “Ku faɗi komi kuke buƙata a gareni kai tsaye in dai baifi ƙarfina ba zan muku shi in sha ALLAHU”.
   Cike da jin daɗin furucin nasa Alhaji Sadisu ya cigaba da faɗin, “Muna neman alfarmar ka bamu auren Halimatu”.
       Ba baba kawai ba hatta da mai anguwa sai da ya waro idanu sosai cikin nuna ƴar tsorata......

       🌛🌟🌜

    Kallo ɗaya nayima Mama Balki dake gurfane gaban Hajiya na ɗauke idanuna zuciyata na suya. Da ƙyar na iya control ɗin kaina nima na kai durƙushe. Latse-latsenta take a laptop tamkar batama san da zuwan namu ba. Gefenta Azizat ce kwance itama tana latsa wayar fuskarta mamaye da fara'a. Sai da ta mula dan kanta sannan ta ɗago bayan ta rufe laptop ɗin. Fuska a yatsine kamar taga kashi ta daka min tsawa. Dakewa nayi batare da nuna razana ba. Sai cemata da nayi “Ina kwana”.
        “Daban kwana ba ƙya ganni firiritacciya. Ke mai ido a tsakar kai kinzo cin arziƙi gidan mutane har da marin ƴar masu gida ko?”.
     “Ko kuma ƴar cin arziƙin itama ba”. Na faɗa ƙasa-ƙasa.
     “What! Mi kikace?”.
   Ta faɗa a matuƙar tsawace. Idanuna na ɗago na kalleta fuska a shagwaɓe. “Nifa bance komai ba Mamma. Please ki daina faɗan firgitani kike sake yi”.
      Ba ita ba hatta Azizat ɗin Tata sai da ta juyo tana kallona da mamaki ƙarara a fuskarta. Balle su Bahijja da suka waro idanu da wangale bakuna. Niko yi nai tamkar ban gansu ba na sake shagwaɓe fuskata da taɓeta. Sai kuma na ɗauka ruwan dake a cikin kofi a gabanta na miƙa mata. “Kisha ruwan sanyi Mamma zuciyarki zatayi sanyi. Ba'a son masu shekaru irin naku da yawan faɗa za'a iya samun matsalar hawan jini daga nan ta zama ta zuniya”.
      Galala ta sake yi tana kallona. Niko na tsatstsareta da idanu ina sake tura baki da marairaice face. Da wani irin masifar ƙarfi ta cije lips ɗinta tamkar zata hudasu. Sai kuma tasa hannu ta kaɓar da kofin hannun nawa. A take ruwan ya tarwatse mana a jiki har ita. Cikin masifar ƙaraji da wutar bala'i ta ce, “Balki!!!”. A razane Mama Balki ta amsa tana miƙewa daga durƙuson da tayi zaram. “Na.. na... Na'am Hajiya”.
     “Ɗauki yarinyar nan ku ɓace min anan kafin na haukata jikunan ku da duka ku duka. Na kuma fasa aikin nata a sashena ki kaita sashen Hajiya Babba ta gyaro shi kafin nan kafin azhar”.
          Wani irin waro idanu na masifa Mama Balki tayi, cike da tashin hankali da suɓutar baki ta furta, “Sashen Hajiya Babba kuma Hajiya?”.
      “Ko bazaki kaitan ba ne?!!”.
   Cikin rawar jiki mama Balki ta shiga girgiza kanta da faɗin, “To to to Hajiya ALLAH ya huci zuciyarki, za..zan kaita mana.” mama Balki ta faɗa tana kama hannuna jikinta na rawa sosai. Da ƙyar na iya danne dariyar dake cina har muka baro wajen, dan tana ambaton Hajiya babban naji tamkar na dirga tsalle dan daɗi. Muna kammala hawa upstairs ɗin a stairs ɗin ƙarshe na ɗan kallo ƙasan, sai da na haɗiye dariyar dake cina sannan na kwaɓe fuska kamar zan fasa kuka. “Mammah dan ALLAH ni dai ina neman alfarma. In dai akwai matsala da zarar kunji na banka ihu a kawo min ɗauki koda sassaƙa-sassaƙan garadan nan na bakin ƙofar gida ne a turamin idan ma ku bazaku iya ba”.
       A matuƙar fusace ta watso min muguwar harara da gwala-gwalan idanunta “Sai dai a turo miki Ubanki. Ƴar iskar yarinya sheɗaniya. Da alama kema dai mahaukaciyar ce get out of my side kafin na canja miki kamanni”.
     Baki na tura mata cikin sake narke fuska da yamutseta na ce, “Ai dai ubana yana aljanna in sha ALLAHU badai shi b....”
         Kafin ma na kai ƙarshe Mama Balki ta fisga hannuna jikinta na rawa. Duk yanda naso ta sakan taƙi yin hakan har sai da muka ɓacema ganinsu. Kamar zata saki kuka ta ce, “Kandala baki da hankali ko? Yanzu wannan hukuncin da suka zartar a kanki bai isheki ishara ba ki koya kimtsa bakinki? Dan ALLAH ƴar nan kada ki sakamu a masifa mutanen gidan nan sun wuce fiye da yanda kike tsammani a fitina wlhy. Kiyi fatan Alhaji ƙarami bai bar gidan nan ba yazo ya fiddaki a wajen nan da wuri, zanje na samesa yanzun nan”.
      Da sauri na ce, “A'a mama dan ALLAH kada ki kirashi. Miye dan tace nazo nayi aikin anan?”.
     “Yarinyar nan baki da hankali, wautarki tayi yawa wlhy. Kandala wannan sashen da kike gani baida maraba da rami mai kwazazzabo da in ka faɗa a cikinsa sai abinda ALLAH yayi. Gara kiyi aiki a sashen Hajiya Mammah ɗin dan ita masifa ce kawai da takura, amma nan ranki ma zaki iya rasawa. Ni dai ki jirani anan zan je na duba Alhaji ƙaramin ALLAH yasa bai fita ba”.
      Ƙasa kawai nayi da kaina batare da nace mata komai ba.. Ita ma sai bata sake magana ba tai gaba.......✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒕𝒘𝒐_

___________


Toh Nazo maku
Da kayan arziki
Kudai kunsan mata sai da gyara
Macen da Bata da gyara ta zama yar kallo a gidan ta
A katafaren kamfanin mu na BEENAD HERBAL MEDICINE
Mun shahara wajen kawo maku ingattatun magunguna mata da na gyaran jiki,kayan mu guarantee ne
Muna da
Shedaniyar gumba
Gumba mai saying
Garin mai kabbara
Mai dalalan miyau
Wayyo dadi
Mai bunsuru
Dan jarida
Soyayya dole
Bakin kyalle
Tadire ta girke
Gumba mai likkafani
Maza taye
Zumar kwakwa
Zumar ridi
Zumar dabino
Zuma mai ma'ul ijaba
Farin jini
Mallakoki
Gumba kalla kalla da dai sauran su
A BEENAD HERBAL muna da turarukan wuta da humrah kalla daban daban sai Wanda kika zabba
Ga kuma maganin slimming
Gyaran nono
Maganin hips
Maganin Kara kiba
Da dai sauran su
Kayan mu tested and trusted ne
Muna maraba da masu siyan Daya ko sari
Muna Nan cikin garin kaduna
Kuma muna tura Kaya duk inda kike da yardan Allah

Ni ce taku har kullum
AMINA GACHI
07034404975
CEO BEENAD HERBAL MEDICINE &INCENCE
KADUNA
Phone no 07034404975

____________

......Riƙota nayi ina girgiza kaina. Ta tsaya tana kallona. Idanuna cike da ƙwalla na ce, “Kiyi haƙuri Mama ki buɗe min zan gwada na gani. Koba komai itama mutum ce kamar mu. Muma kuma bamu san ya rayuwa zatai damu ba anan gaba. Dan ALLAH ki buɗe min kawai ALLAH yana tare da ni”.
      Sosai alamar sanyayar jiki ya bayyana a gareta na jin kalamai na. Dan haka ta nufi ƙofar dake a falon batare da ta sake cemin komai ba. Bayanta nabi ina mai jin tausayinta. Babbar mace kamila yanayin rayuwa yasa tana gurfana a gaban wadda bata wuce sa'arta ba. Lips ɗina na ciza. Kafin na furzar da iska nabi bayanta nima. Sosai tsaruwar falon farko na sashen yay matuƙar ɗaukar hankalina. Fes yake yana ɗaukar ido saboda kayan alatun da yasha. Da alama ana gyarashi kullum. Kamar zanyi magana sai kuma nayi shiru dan ganin yanda Mama Balki ke ɗari-ɗarin buɗe ƙofa ta biyu. Sai da ta runtse ido da karanto addu'a sannan ta murɗa handle ɗin. Da sauri tayo baya tamkar mai shirin zurawa a guje. Kallonta na tsaya yi kawai cike da nazari, sai kuma na sauke numfashi. “Uhhh mama, inaga kije kawai daga nan babu damuwa zan ƙarasa ni kaɗai.”
      Waro idanu Mama tayi, sai kuma ta marairaice fuska idanunta na cika da ƙwalla. Ƴar nan dan ALLAH kiyi addu'a kinji, ko ki zauna a wannan falon sai zuwa anjima ta tashi ki gudo, Kinga shike nan an rabu lafiya”.
      Murmushi mai kama da yaƙe kawai na mata ina jinjina kaina alamar to zanyi. Numfashi ta sauke mai nauyi, sai kuma ta haɗiyi yawu jiki a sanyaye ta juya ta fita tana waigena. Ni dai kallonta kawai nake har sai da ta maida ƙofar falon ta rufe a hankali. Sai kuma ta sake buɗewa. “Karki sake ko kulle kowacce ƙofa dan ALLAH Kandala. Ki barsu a buɗe yanda zaki samu damar gudowa koda an sami akasi”.
    Kaina na jinjina mata nan ma ina murmushi. Ta sake ɗan jan ƙofar batare data rufe duka ba ta barta. Shiru nayi kawai a wajen tsaye har zuwa wani lokaci. Ni kaina a tsoracen nake. Amma inata ƙoƙarin dakewa kun dai san ɗan jarida da jarumtar wahala. Shiru sashen yake babu alamar motsin mai rai, sai ɗan yanayin kamar bashi-bashi dake bugowa daga ƙofar da Mama ta buɗe. Ƙofar na tsurama idanu na wani lokaci, kafin nayi ƙundun balar nufarta cikin sanɗa da ambaton sunan UBANGIJI......

📯📯📯📯

    Farin cikin da Musaddiq yake a wannan rana bazai taɓa musaltuwa ba a zahiri. Sai dai ya barma UBANGIJI komai. Tsaff ya fito cikin shirinsa na shadda ruwan ƙasa mai haske harda hula. Sai ƙamshin turarensa yake mai sanyin daɗi. Hannunsa riƙe da takardunsa yake ƙoƙarin kulle ƙofar. Juyowa yay da sauri jin kamar mutum ata bayansa yana kallonsa. Ilai kuwa ido huɗu sukai da Umma mahaifiyar Mom da alama isowarta gidan kenan. Kauda tsarguwar kallon ƙurillar da take binsa da shi yayi, tare da sakin nutsatstsen murmushinsa ya ƙaraso inda take. Cike da girmamawa ya ce, “Sannu da zuwa Umma. Ina kwana? Anzo lafiya?”.
      Cikin ɗan daburcewa da dawowa a hayyaci ta shiga amsawa bakinta a washe. Dan harga ALLAH yaron ya gama firgita mata zuciya da guntun lissafin ta. Wani kalar mahaukacin sirrintaccen ƙyawu fa taga yayi mata da ƙiba harda haske. Ga arziƙi muraran ya nuna a jikinsa kai kace ma shine ɗan masu gidan ba ɗan riƙo ba. Dan ko mahaukaci ya kallesa ya kalla Abbas yasan akwai banbanci da tazara mai yawa ta cigaban rayuwa....
     “Ki shiga Umma ai su Mom ɗin suna nan ciki”. Ya faɗa cikin katse mata tunanin data lula. Firgigit kuwa ta dawo a hayyacinta. Sai kuma ta washe baki cikin in ina ta ce, “T... t.. to ɗan nan nagode kaji, ALLAH ya muku albarka ya ƙara arziƙi. Bari na shiga ɗin dai to”. Ta ƙare maganar tana tafiya da waiwayensa a lokaci guda har taci tuntuɓe tana neman faɗuwa. Ta dai samu ta dafe gini idonta a kansa har lokacin ga baki a washe kamar sakara.
      Shi dai Musaddiq cike da al'ajabinta yay ficewarsa. Kaɗan-kaɗan sai ya kalla kansa ko zaiga abinda takema kallon ƙurulla a jikin nashi. Amma sai baiga komai ba. Haka dai ya tare napep ya shiga komai na masa kai-kawo a rai da zuciya. Koda ya iso gate ɗin companyn sai da ya nuna ɗan katin da ogansa ya bashi sannan aka barshi ya shiga. Sosai yake jinjina ƙudira da rahama ta UBANGIJI. Dan gaskiya wannan Company ya matuƙar tafiya da imaninsa. Gini ne iya gini da baka iya ƙuresa da idanu. Ga ma'aikata nata faman kai-kawo da securitys. Ga kayan aikin tako ina da zai tabbatar maka da komai fa da gaske ake babu wasa. Da taimakon wani security akai masa rakiya office ɗin Manager.....

         💦✨💦✨💦

   Ji Abba yay tamkar ya tashi ya buga ihu da tsalle dan farin cikin hukuncin Baba. Domin ya tabbatar musu in dai Halime na son Abban zai bashi ita. Hakan yasa aka aika aka kira Halime. Koda tazo taci karo da su Abba sai da ta nuna ƙololuwar mamakinta har ta gagara yin magana sai da Babanta yay mata magana ma ta iya gaishesu muryarta na rawa. Zata ɗora da zance Abba daya san mi zata iya faɗa yay saurin katseta. Dan baya fatan ta tona asirin komai musamman akan abinda ya faru a randa ta gudo ɗin, saboda ya fahimci bata sanarma su Baban komai ba. Shirun kuwa tayi kamar ta fahimci abinda yake buƙata, daga haka mai anguwa ya sanar mata abinda ya kawo su Abba. Sake diriricewa kuwa tayi tana faman zare idanu. Da ƙyar Abba ya iya danne dariyarsa. Alhaji Jafaru da Alhaji Sadisu kuwa sai da suka dara kaɗan. Mai anguwa ma dai yayi kaɗan kafin ya ɗora da tambayarta ko tana son Abba ɗin.... Ai baima rufe baki ba suka tsinceta can ta zura a guje cikin gidan mai anguwar.
        Basu Abba ba hatta da Babanta yanzu kam sai da ya dara. Fuskarsa da sauran dariyar ya dubi Abba. “Imamu kaga fa shirmen mutuniyar taka. Anya zaka iya da ita?

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login