Showing 90001 words to 93000 words out of 115623 words
na saka Hayatu ya amso”.
Kai na jinjina mata cikin gamsuwa.
✨❤️✨
Yau kwanaki biyu kenan Mom bata saka Abba a idanunta ba. Dan tun jifar da tai masa a washe garin angwancinsa bai sake shiga inda take ba. Hakama amaryar tasa taƙi fitowa. A tunaninta dana yaƴanta harma da Ummanta ai tsoro ya hana amarya fitowa. Dan haka suka fara jin alfahari a ransu musamman ma Mom. Haka zata fito tsakar gida tana habaici da yada magana. Daga Gwaggo Gudidi har Halime da Gwaggon ce ta kwaɓeta babu mai kulata. Hakama Abba yayi watsin ruwan tsarki da ita shan shagalinsa kawai yake da amaryarsa. Gaba ɗaya ya ajiye shekarun girmansa gefe yana koyama Halime salo-salo da tabbatar mata ita ɗin ma fa mace ce. Itako banda raki da taɓara babu abinda take ɓarar masa. Gaba ɗaya ta susuce bawan ALLAH baya ganin komai da tuna kowa a gabansa sai ita. Hatta kasuwa a kwani biyun nan babu inda yake zuwa a gidan yake yini salla kawai ke fidda shi. Dole kuma akayi abinci Gwaggo Gudidi taje ta ɗiba musu tasa Bibaa na kumbure-kumbure takai musu har falo.
Yau dai zaman ɗaki ya ishi Halime. Tana ganin Abba ya fita sallar la'asar ta fito. Tsaff take cikin kwalliya, duk kwalliyar ba'a yi ta yanda ya kamata ba kaya data saka sun fiddo jikinta tsaff da yi mata ƙyau. Ga uban turare ta bulbula. Tun a gaban mirror ake gwada tafiyar da za'ayi, dan haka koda aka fito taku ake ɗaɗɗaya ana juya jiki su adole amare. Nan ko a cikin ɗaki raki takema Abba😂. Gwaggo Gudidi tai shirin fara gaidawa. Dan haka kai tsaye ɗakin da take ta shiga. Ta samu Gwaggon na haɗa kayan tafiya, dan magana ta gaskiya taɓarar da Abba ke zuba musu a gidan na kasa kimtsa bakinsa ya fara isarta itama. Bata ji na daren farko ba amma jiya da rana da yau gabannin asuba fes a kunnenta. Wannan taɓara da rashin sanin ciwon kai har ina. Gara dai ta gusa taɗan basu waje ai ita uwa ce. Maybe ma idan ta wuce ɗin waccan mahaukaciyar surukar tashi itama tayima kanta faɗa ta shirya ta tafi, dan har yanzu Umma na gidan ta fake da jiyyar Mom duk da itama fa abinda Abban keyi na damunta.
Cike da farin cikin ganin Halime Gwaggo ke faɗin, “Oyoyo oyoyo ɗiyata amarya”.
Kunya ce sosai ta kama Halime. Tai ƙasa da kanta tana wasa da yatsun hannunta. A ran Gwaggo tace (ashe ke da sauranki Imamu bai ida kakkaɓe sauran taki kunyar ba). A fili kam sai ta riƙo hannun Halime cikin nata. Durƙusawa Halimen tayi ƙasa cike da girmamawa da kunya tana gaida Gwaggo. Sai Gwaggo taji hawaye sun ciko mata. Dan abune da bata taɓa gani ga Mom ba. Ko sanda tana amarya fingai-fingai tazo musu babu alamar kunya tattare da ita. Amma ita wannan jiba dai yarinya ƙarama amma Alhamdullah. Bayan sun gaisa Gwaggo taita jan Halime da ƴar hira. Wani ta amsa wani tayi murmushi kawai cikin kunya. Sunfi mintuna ashirin a haka suka fara jin hayaniya na tashi. A tare suka fita, dan muryar Umman Mom suke jiyowa. Cak bakin Mom dake ƙoƙarin yin magana ya maƙale, tun daga bakinta da hanci da idanu duk akan Halime. Kasa haƙuri tayi ta nufo inda suke da sauri. Gaban Halime ta tsaya sai kuma ta nunata da yatsa lips ɗinta na rawa. Amma mi a mamakin kowa sai gani sukai Halimen ta saki murmushi tare da rissinawa a girmame ta ce, “Yaya ina yini? Fatan duk kuna lahiya ke da yara? Ya gajiyar bik.....”
“Wacece ke? Miya dawo dake gidana dan ubanki?”. Mom ta katse Halime jikinta har ɓari yake. Murmushi Halime ta sake saki da ɗan bin Mom da kallo daga sama zuwa ƙasa. Sai kuma ta sake murmusawa da yin fari da ido tana wani watsa hannuwa gaba da baya cikin iyayi ta ce, “Halime mana nasan kin gane ai. Na dawo matsayin da kema kike a gidan, wato MATAR ABBA IMAM”.
Wani shegen tsalle Mom tayi gefe tamkar wadda taci karo da baƙin maciji. Yayinda Gwaggo Gudidi da abin ya bama dariya ta saki murmushi da gyara tsaiwar ta. Wani irin zaburowa Mom tayi kan Halime tana faɗin, “Shegiya munafuka algunguma ƙarya kike wlhy, mi mijina zaiyi da kucaka ƴar aiki irin ki. Dan ubanki faɗa min miya kawo ki?”.
Murmushi Halime ta saki, tare da ja baya kaɗan ta kaucewa cakumar da Mom ke ƙoƙarin kawo mata. Cike da fari da sake yarfar da hannu. Sai kuma ta ɗan duƙo cikin raɗa-raɗa ta furta, “Abinda mijin naki yake yi dake nima shi yake yi dani a cikin ɗaki” ta ƙare maganar da kashe mata ido ɗaya cike da son sake bata haushi ta gittata ta wuce cikin takun da aka gama kowa a gaban mirror.
Gaba ɗaya Mom tai baya zata zube bakinta a hangane sai da Ummanta da itama tayi sumar tsaye ta tarota....
❤️❤️❤️❤️❤️
Sosai abubuwan da naji a bakin Mama Balki suka sakani a cikin damuwa da ɗimuwa musamman akan mijinta daya rasu, dan gaba ɗaya suffofin data ambacesa dasu kama suke dana Babbanmu. Idan kuma ban manta ba Mom ta taɓa min gugar zana da cewar ai ubanmu har karuwa garesa a Lagos. Lallai tabbas ina buƙatar ganin hoton nan nashi.
Damuwa tamun yawa sai dai ina matuƙar daurewa dan kada kowa ya gane min. Musamman Bahijja sarkin tambaya. Data ganni shiru tata nacin son jin mike damuna. Har cikin rai nima ina ƙaunar yarinyar, sai yanayinta ke ɗauke min kewar Auta. Kwanki biyun nan jikin Ummie da sauƙi sosai, dan na duƙufa addu'a. Yanzu hatta a ruwan wankanta da Mama Balki ke shiga a ɓoye tai mata safe da yamma sai nayi addu'a. Abincin ta da ruwan shanta duka. Dan na daina bata abinci gidan sai wanda nasan ni na girka ko Mama Balki. Damuwa da yawan tunani ya sani ɗan fitowa yau ina zagaya gidan ko zan rage nauyin zuciya da kewar ahalina, dan ina son kiran Yaya Musaddiq akan abinda naji amma na kwaɓi kaina har sai na tabbatar sannan. Wayar Bahijja ce a hannuna na gama magana da Yaya Musaddiq dake sanar min a wajen aikinsu sunce zasu turashi ƙasar waje ya ƙaro karatu. Farin cikin wannan magana ta sani cigaba da tsaiwa a wajen ina kallon kai kawon masu aiki maza dake sabgoginsu a garabar gidan.
A dai-dai nan naga ana ƙoƙarin buɗe ƙaton gate ɗin gidan. Ban kawo komai a raina ba na ɗauke kaina ina cigaba da game a wayar. Har motocin suka gama shigowa ban ɗago ba, dan na ɗauka normal baƙine tunda gidan baya rabo da shiga da fitar motoci. Sai da naji tsaiwar mota a inda nake sannan na ɗago, dan dama a jikin wata motar nake a rumfar ajiyesu. Haka kawai sai da naji ƙirjina ya motsa da ganin wanda banyi tsammani ba. Dan rabonsa da gidan kusan sati ɗaya kenan dama wasu kwanaki.
A hankali ya ziro ƙafafunsa dake cikin takalma boot brown masu laushi da ɗaukar idanu tamkar wani miski, gasu da ɗan tsaho ta sama dan har akan wandonsa sosai suka hau. Ko maƙiyi ya kallesa daga sama har ƙasa yasan yayi ƙyau matuƙa cikin shigar tasa. Ga mayen ƙamshin turarensa da tuni ya mamaye wajen kamar anyi ɓarinsa. Cike da matuƙar girmamawa duk masu aikin suka zube suna gaishesa, cikin lumshe idanu da sake dai-daita nutsuwarsa ya ɗaga musu hannayensa alamar amsawa. Kafin ya motsa lips ɗinsa kaɗan cikin silent voice ɗin nan tasa ya furta, “Kuna lafiya?”.
Cike da jin daɗi da girmamawa duk suka amsa masa. Shima sai bai sake cewa komai ba ya juyo gareni. Kallon cikin ido mukaima juna, na kauda nawa da sauri ina ɗan tura baki. Ganin yanda duk yaransa suka samun ido musamman Hayatu ciki-ciki na ce “Ina yini”.
Bai amsa min ba, bai kuma daina kallona ba. Sai da ya mula dan kansa ya ɗaga ƙafafunsa zai bar wajen. A bazata naji shigar furucinsa cikin kunnena. “Karna sake ganinki a anan wajen”. Da sauri na ɗago, sai dai kafin na iya cewa wani abu yabar wajen yaran nasa na take masa baya. Sai Hayatu ne a hankali ya ce, “Good afternoon maa”. Harara na ɗago na watsa masa. Ya wuce yana murmushi.
Masu aiki dake durƙushe har yanzu kansu a ƙasa duk miƙewa sukayi tare da darewa suka bashi hanya. Shiko ya ratsasu cike da takun nan nasa na mazantaka da tsantsar kamala da nutsuwa. Hayatu da wanda ban san sunansa ba da ƙyamusashiyar baturiyar nan Juliet suka take masa baya. Baki na taɓe tare da raka bayansu da harara. Sai kuma naji duk tsaiwar ta gundireni. Haka na koma ciki ina ƙunƙuni.
Ban sake jin labarinsa ba dan ina sashenmu ina wanke kayan Ummie har yamma. Na kwaso kayan zanje na kai ciki aunty Zakiyya ta kirani a wayar Bahijja. Shine na ajiye na fito domin amsa wayar dan bana son su fahimci komai. Ina fara wayar ƙamshin turarensa ya mamaye wajen. Ɗagowa nai da sauri, sai na hangesa ɗan nesa da ni kaɗan ya nufi gate ɗayan mutumin nan daban san sunansa ba (TJ) biye da shi. Da alama masallaci zasu je dan sanye yake cikin blue jallabiya data fiddo da shi tamkar wani balaraben yankin sudani. Ɗauke idanuna nayi da sauri saboda hararar daya watsomin da ban san ta miye ba. Wayata na cigaba dayi da aunty Zakiyya ina dariya har sai da na kammala sannan na koma na ɗauki kayan Ummie na shiga ciki. Labarin data bani na ɗirkama Halime kayan mata dan ta rikita Abba yasa na kasa daina murmushi. Na samu ummie tana barci, dan yanzu abinda tafi yi kenan. Sai uban ƙamshin turarensa daya tabbatar min daya shigo sashen. Baki na taɓe na ajiye kayan na fita........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒇𝒊𝒗𝒆_
.......Wajen ƙarfe tara na fito nemawa Ummie abinci, dan nasan tana farkawa shi take fara nema. Ina shiga Hajiya Mammah dake kitchen ɗin ban san mi take yi ba ta aikeni sashensa. Cike da jin haushi na shigo ɗauke da abincin da Hajiya Mammah ɗin ta sani kawo masa. Ko sallamar ma ciki-ciki nayita. Tsaff katafaren falon nasa yake kamar ko yaushe, ga ƙamshin nan dana rasa daga ina yake samunsa dan ya bambanta da duk wani ƙamshi dana taɓa sani ko shaƙa a wajen mutane. Komai nasa dabbane dana saura. Sallama na sake yi a ƙuntace dai-dai isowata tsakkiyar falon sosai. Dan naga alamar basu ji ta farkon ba, inda dan shi kadai ne bazan damu ba. Dan koda yaji zai iya shareni wannan ƙaramin aikinsa ne, amma Hayatu bazaiyi hakan ba duk da takaicinsa da nake, shima kuma ƙwallon kansa ne.
Yanzun ma dai Hayatun ne ya ɗago da sauri alamar dai basu san da shigowar tawa ba da gaske. Cike da kulawa ya amsa min yana wani ɗan rissinar da kansa. Harararsa nayi kawai na ɗauke kai, dan wannan girmamawar da yake min na baƙanta min zuciya. Shiko gogan baima nuna alamar yasan da shigowar tawa ba. Gaba ɗaya idanunsa da ƙyaƙyƙyawar fuskarsa na kan screen ɗin laptop ɗin cinyarsa da takardun hannunsa. Fuskar nan ciɗin-ciɗin babu alamar sassauci kamar wanda ma ke cikin ɓacin rai. Cikin i don't care na laɓe bakinna da dangwarar da tray ɗin saman Centre table ɗin daya ajiye ƙafafunsa masu tsananin tsafta da haske. Gashi cas babu wani girma sosai irin na maza. Dan wata macen ma sai ta fishi girman ƙafa. Da alama dungurarsa da tray ɗin ya ɗanyi ya saka shi ɗan ɗagowa a karo na farko ya ɗan kalleni. Sai kuma ya ɗauke idanun yuuu ya maida ga laptop ɗin. Nima nawa na ɗauke ina sake tsuke tawa fuskar na juya abina da nufin komawa inda na fito.
“Bani ruwa marasa sanyi”. Ya faɗa a dake babu alamar wasa a cikin silent voice ɗinsa. To amma tunda ba suna ya ambata ba bai shafen ba tunda bani kaɗai bace a falon ai. Cigaba da tafiyata nayi dai-dai da yunƙurawar Hayatu alamar zai bashi ruwan.
“Da ita nake”.
Ya katse hanzarin Hayatun cikin gizagonsa. Duk da naji abinda yace ɗin ban kula ba. Ganin na cigaba da tafiyata cike da girmamawa Hayatu ya ce, “Aunt yace da ke yake fa”. Wani irin ɓacin rai ne naji ya ziyarcen. Dan haka na juyo a fusace ina watsama Hayatun mummunan kallo. “Wai malam banace maka ka daina kirana da wannan sunan ba. In ce dai kasan sunana Samraah ai”.
Murmushi kawai Hayatun yayi yana mai rissinar da kansa ƙasa. Sai kuma yace, “Kiyi haƙuri bazan iya faɗa bane. Dan kina da kima da matsayin fiye ma da hakan a wajena”.
Cikin gatse na ce, “Saboda a gida ɗaya aka haifemu?”.
“A'a saboda kina tare da auren boss”.
Duk da furucin nasa yay masaifar tsargani sai na dake. Cike da masifa na ce, “Kaima kasan wani auren boss ai, kar kuma ka sake jinginani da abinda ku ya shafa bani ba”.
Baki ya sake buɗewa zai yi magana, sai dai hakan bai yiwu ba, dan kamar a ɗan fusace silent voice ɗin boss ɗin nashi ta daki kumnuwanmu.
“Hayat! Kaje zan nemeka”.
Abinda yay niyar faɗar ya haɗiye. Batare da wata jayayya ba ya miƙe zumbur. Takardun jikinsa ya tattara ya kai gabansa. Hakan yasa na watsa musu harara su duka na cigaba da tafiyata. Sai dai kafin nakai ƙofar har Hayatu yazo ya wuceni, yana fita ya wani rufo ƙofar. Ban damu ba na kama handle ɗin nima zan buɗe na jita gam. Wani irin takaici ne ya ratsa zuciyata. Dan na fahimci mutanen nan neman maida min rayuwa suke wata sha katafi. Shiru nayi tsaye a wajen har kusan minti ɗaya. Sanin banda wata mafita saita wajensa ɗin ya sani nufar dining room ɗin sa. A cikin haɗaɗɗen freight ɗin dake a wajen na buɗe na ɗakko goran ruwa masu sanyi sosai saɓanin wanda yace marasa sanyi. Batare dana ɗora a saman tray ba ko ɗaukar kofi na fito. Har yanzu yana a yanda yake hankalinsa a laptop ɗin. Ruwan na dangwarar masa kawai ina tura baki. Ganin yaƙi nuna yasan dani ma a wajen ya sani faɗin, “Ga ruwan nan zan tafi”. Shiru bai kulani ba. Baima ko motsa ba. Takaici ya sake riƙemin maƙoshi, sai dai nasan fushi na bazai haifar min da komai ba sai ma sake tunzurashi. Sassauta muryata nayi a hankali na ce, “Please ka bani key na fita”.
Nan ma shiru bai da niyyar kulani, tuni idanuna sun fara cika da ƙwalla. Kusan minti ɗaya sannan ya magantu ciki-ciki.
“Ban hanaki shiga cikinsu ba?”.
Da farko ban fahimci abinda ya faɗa ɗin ba. Sai daga baya na fahimci akan ma'aikatan gidan nan ne maza da ɗazun a compaund. Dan haka cikin son manna masa rainin wayo na ɗan duƙo kansa kaɗan duk da yanda zuciyata ke bugawa da sauri-sauri cikin dakewa na furta, “A matsayinka na wa?”.
Wani irin lumshe idanunsa dake yawo a fuskata yayi, yayinda ni kuma na yunƙura da nufin barin wajen kawai naji an bugi ƙafafuna. Gaba ɗayana na tafi, duk yanda nai ƙoƙarin son riƙe wani abu hakan bai yiwu ba sai da na faɗa kansa na zauna daram a cinyar tasa. Yanda na faɗo ɗin fuskokinmu suka kasance gab-gab da juna. Wani irin kallo yake min cikin tsakkiyar ido daya hanani iya koda motsi, kafin a hankali ya sake matso fuskar tasa gab da tawa. A take gaba ɗaya tsigar jikina ta mimmiƙe. Sai kawai na lumshe idanuna a hankali dan nagama sadaƙarwa akan nawa lips ɗin zai sauke nashin. Amma a maimakon hakan sai jin saukar yatsarsa nayi a saman lips ɗina ya shiga zagayawa a hankali, tare da sassanyar muryarsa cikin kunnena ya furta, “I'm not interested”.
Da sauri na buɗe idanun tare buge hannunsa dan har yanzu yana zagaya yatsarsa akan lips ɗin nawa. Bamma san sanda na watsa masa harara ba da ɗora hannayena akan ƙirjinsa na turashi baya. Ni kuma nai yunkurin tashi zumut. Amma tsabar mungunta sai ya sake taɗeni da ƙafar na sake komawa kan jikin nasa. Hannun na sake kaiwa jikin nasa zan turashi naji saukar nasa a bayana. Matsoni yay gaba ɗaya sai gani kwance a ƙirjinsa. A fusace na buɗe baki zanyi magana ya rufesa rufff da mitsitsin nashi. Waro idanun nawa waje nayi gaba ɗaya cikin tashin hankali da rikicewa, shima ya ɗan waro nasa kaɗan sai kuma ya kashe min ido ɗaya cike da salon iskanci. Ai ruff na sake rufe nawa idanun jikina na rawa.
Duk yanda naso ƙwace jikina hakan ya gagara, dan yayi masifar min irin riƙon da ban isa ƙwatar kan nawa ba. Da wani irin kalar salo yake sarrafa halshena cikin bakinsa. Duk mintsinin da nake masa babu alamar yana jina ma. Sai da yay mai isarsa dan ko kiran wayarsa da ake faman yi bai kula ba, gaba ɗaya jikina ya gama saki. Koda ya sakan sai kawai na duƙunƙune a jikin nasa