Showing 27001 words to 30000 words out of 44561 words

Chapter 10 - Bintu Diyar Bayi Ce 1 Complete Hausa Novel

06 Jan 2025

156

ki na yi’’

Bintu ta dai ba ta ce komai ba, ita kad'ai ta san irin fad’uwar gaban da ta ke fama da shi. Ita dai adduar ta Allah ya sa alkahiri ne yanayin da ta ke ji.

***** ****
Babban gida kuwa, Jakadiya ba ta yi k’asa a gwiwa ba, bayan ta gama shirya sarki cikin shirin bacci, Sarki na daga shingid’e, kafin ta raka shi wajan matar da ta za6a ma sarki kwana gurin ta ne ta ke bawa Sarki shawara akan lamarin da Gimbiya Binta ta sheda mata, ta k’are maganar na ta da
‘’watsi da al’amarin Sarki Abdulrahman barazanar rasa rayukan talakawa ne, sake dabara a nemi taimako wata masarautar talakawa za su ga kamar an fi san iyalan sarki akan lamarin rayuwar su, hakan ka iya kawo rabuwar kai cikin wanga masarauta wanda dama k'udirin Masarautar kenan. Tun da Sarki Abdulrahman be ji kunyar yada girman sa ba, da saka rayuwar mu cikin kunci, mu kuwa ba za mu kasa masa bita da kulle ba, dukan kabarin kishiya’’ shiru ta yi dan shan nufashi kafin ta k’ara da
‘’wannan dalili ya sa na yi bincike ta hannnun Gimbiya Binta, ta kuma amince da wannan batu, Allah ya ja da ran sa, idan na yi kuskure a yi min rai, ina tuba’’

Shiru ka je, Sarki na mai juya maganar cikin ran sa, in akwai abun da ya dame shi duk fad’in duniyar nan baya ya ke da farin da alumar shi ke ciki, idan kuma akwai abun da ya fi soyiwa a rayuwar sa, to ya bi bayan iyalin sa, musammam ma yaran sa mata guda biyu, hakan ya sa duk duniya babu wanda ya tsana, ya ke matsayin babban abokin gama kamar Sarki Abdulrahman na Fabarusa. Duk da batun Jakadiya lamari ne mai girma, ya tsinci kan sa ya na mai san yin tuntuntini akai.
Ya na duban Jakadiya ya gyara murya ya ce ‘’Jakadiya mun ji wannan batu na ki, duk dai ba mu gamsu ba, za mu yi tunani akai’’

Jin haka Jakadiya ta duk’a ta na mai d’unkule tafin hannun ta na dama yayinda ta d’aga sama ta na mai jinjina ga Sarki, fad’i ta ke

‘’Sukukun bakaka Jatau, mashin da wuta Jatau, idan mai sa6o bai daina ba mai horon ma ba zai fasa ba!lafiya Barden mahadi! Lagiya Sukukun bakaka! Lafiya Darzaza amalen sarakuna’’

********

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[5/5, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


©Khadija Sidi.....✍🏼

1⃣6⃣



Washagari kan Sarki ya zauna fadanci, yayi kiran Waziri da Hadiman sa guda hud’u, dan kuwa tun zantawar sa da Jakadiya, har ta kai shi ga d’akin Inna Salti Sarki be runtsa ba, shawarar Jakadiya ke masa yawo aka. Ai kuwa dai Waziri ma na’am yayi da shawara, a fad’ar sa ‘’karan ban shi an maganin zoman bana’’

Biyu daga cikin Mahadin Sarki su ne su ka banbanta batu, ana su zai fi ga kyau Sarki ya tsaya tsayin daka kan lamarin sa na gaskiya, dan ko da ba su ji ba, wanga magana hallo maganar mata ce. A wannan sanadin ne Sarki ya ce in su na biye da shi za su iya zama fada, in kuwa ba haka ba ya na mai d’aure su har sai hakin masarauta ya cimma ruwa, dan babu damar korar su daga fada su na amintattun Hadiman sarki, surrin fada babu wanda ba su sani. Da wannan su ka ja bakin su su ka yi shiru, su na mai Allah wadar da wanda ya bawa Sarki wanga shawara, dan kuwa Sarki idanu ya rufe madafa kawai ya ke nima, ya kuma sami bahaguwar madafa mai wuyar 6ullewa sai dai fa Allah shi kyauta da aikin dana sani.


Bintu na gyaran gadon Gimbiya Binta, ita kuma Gimbiyar na daga kishingid’e bisa tin tin ana mata danna. Sai ga Jakadiya ta shigo jiki na rawa daga gani kasan da magana a bakin ta. Bayi na ta gaishe ta, haka ma Bintu wacce tun shigowar Jakadiya ta ga ta kafe ta ido. Jakadiya na mai duban Bintu ta ce "ko da ban sani ba ke an Bintu’’

Gaban Bintu ne ya fad’i yayinda ta zube k’asa ta na mai fad’in ‘’Allah ya huci zuciyar Jadiya, Bintu na ke ba ki 6ata ba’’
Kallan ta ta ke cikin nazari, kafin ta juya ta dubi Gimbiya Binta, gudun kar sauran bayi su gane sakon da za ta fad'wa Gimbiya, sai cewa ta yi
‘’ta kan kwaba, ta kan kan ta, ta kan akwati mai taya, sai sid’if ta fad’a, sai sid’if na d’auka’’

Jin haka Gimbiya Binta ta saki k'awataccen murmushi, dama abun da ta ke jira kenan, kana ta ce
"zannuwa ishirin sun yi kad’an, aradu na k’ara mi ki goma har da kallabi goma’’
Jin haka Jakadiya ta rangwad’a gud'a ta na mai fad’in ‘’yaro wake tab'a mai uwa? Ba zai ci ba kayan kasuwa, sai ni Hindu jikar Baba Kilishi Jikar Nana, godiya na ke Gimbiya’’
Kana ta kai kallan ta ga Bintu ta ce "biyo ni yarinya’’

Gaba Bintu na fad’uwa duk dai ba ta fahimci zancen na Gimbiya da Jakadiya ba, ta bi bayan Jakadiya. Ganin haka wata Baiwa mai kaiwa Yerima Nuhu duk wani labari na game da lamarin Bintu ita ma ta ja kafar ta zuwa neman Yarima Nuhu, dan kuwa dai ita ma ba ta gamsu da wannan lamari ba.

Bintu na tafe bayan Jakadiya, ganin in da su ka dosa gaban ta sai faduwa ya ke, musammam da ta ga sun doshi turakar Sarki gadan gadan. Nan su ka tadda Sarki tare da Waziri da Hadimai, bayan su babu wani mahalik’i da ke wajan face amintaccen bawan sarki wanda ake kira Nahana. A bakin kofar turaka Bintu ta kasa d’aga k’afa ta shiga dan tsoro da kwarjini, tun da aka haife ta ko harabar wajan ba ta tab’a shiga ba, bare ace turakar sarki, ga ta ga sarki. Sai da Jakadiya ta d’an jawo ta, na mai mai mata shune da baki ta shiga.

Ganin ta gaban Sarki tuni ta zube k'asa ta na mai kwasar gaisuwa. Yau ga Bintu ga Sarki da waziri har da Hadimai, ko shakka babu dole k'awarta Cangwai ta ji wannan labarin.

Sarki zaune ya hakimce cikin rawani, ya dubi Jakadiya ya ce ‘’ba mu tarihin wanga d’iya’’

Zama Jakadiya ta gyara, kafin ta ce ‘’Allah ya ja daran Babban bijimi, wanga d’iya sunan marigayiya Baba Kilishi ta ci, hakan tsirar haihuwar ta da Gimbiya k’arama kwana d’ai ta, tare su ka tasa da Gimbiya k’ara, dad'in dad’awa makarantar su d’aya, bambacin su d’aya, wanga dai baiwa ce, kuma d’yar bayi, diya ce gun uwar bayi da kuma wannan bawa da ake kira Bala, eh Mahuta ba ,aradu ma kuwa’’

Waziri ya dubi Jakadiya ce ‘’ai fad'uwa ya zo daidai da zama, uban ta shi an babban bawa nai, ya ta ke da suna?’’

‘’Fatima, amma Bintu aka ce mata, kamar yanda ake kiran Gimbiya k'arama Binta’’ ta bashi amsa a takaice. Ita dai Bintu ta na nan kai durkushe daga can gefe amma daga tsakiya da ke ba shakka turakar ba dai girma ba, na gaske ma kuwa. Ko kwakkwaran motsi ba ta iyawa, bare ta d’an d’aga ido gudun kar ta had’a ido da Sarki, dan karshen kwarjini ya mata a yau da ta ke ga ta gashi.

‘’Fatima’’ muryar Sarki ta ji ya daki kunnan, tuni ta k’ara nutsuwa ta na mai rusunar da kai kamar wacce za ta shige k’ark’ashin k’asa. Ba mafarki ta ke ba, sarki da kan sa ya kira sunan ta, ina ma Cangwai ta na nan ta gani da idon ta, dan Idan ta ba ta labari sai ta ce k’arya ta yi.....tunanin da ta ke cikin ran ta kenan, jin Sarki ya ce
‘’a matsayin ki na baiwa a gare mu, shin akwai umarnin da za mu ba ki ki bi?’’
Bintu ta yi saurin duk’ar da kai ta ce "tir da bawan da bai bin maganar uban gidan sa, zan bi umarnin Mai martaba, ko da kuwa hakan zai zama sanadin rasa rai na, kwankwatsi ma kuwa’’

Kwalla na kad’ai Hadiman nan biyu ba su zibdawa Bintu ba, shi kuwa Waziri kai ya shiga kad’awa cike da gamsuwa, bare Jakadiya da ta ke ji kamar ta sab’a Bintu a baya tai ta rawa, Allah dai ya kawo mata tsuntsu daga sama gashesshe. Sarki na mai nazarin Bintu na wani d’an lokaci, daga bisani ya ce za ta iya tafiya. Ta na mai godiya ba tare da ta san abun da ake kullawaba ta fita.

Bayan tafiyar ta Sarki ya ce ya gamsu da komai na ta, amma ya na so Jakadiya ta sa ido kan ta na wani d'an lokaci kafin su gama zartar da hukunci. Da haka da haka har su ka wuce zaman fada.

Da yammacin ranar gaba d’aya walwalar Gimbiya K’amariyya ya dawo. Bintu na zaune gaban ta tana yanke mata farce wayar gida da ke aje d’akin ta ya fara k’ara. Cikin farin ciki ta d’aga, ganin haka Bintu ta tashi da niyar ba ta waje, amma Gimbiya K’amariyya ta d’aga mata hannu alamar ta yi zaman ta.

Maganar da Gimbiya ke fad’awa Yarima Barde ne ya bawa Bintu mamaki, ji ta yi ta na fad’in ‘’Takawa dai ya yanke hukumcin aurar da kauna ta Binta ga Mai Martaba Sarki na Fabarusa...’’

Gaba d’aya jikin Bintu yayi sanyi, cikin ran ta tausayin Gimbiya Binta ta ne ya kama ta, har fad’i ta ke
"Allah sarki Gimbiya ta ceto rayuwar ‘yar uwar ta, yanzu na gane dalilin maganar da sarki ya min, wato ina d'aya daga cikin bayin da za’a tura tare da Gimbiya Binta, kaiconi Bintu karatun mu kuma shikenan’’

Tausayin Gimbiya da ita kan ta shi ya gajiyar da ita ranar, ta kasa ta6uka komai har dare yayi ta koma gida.

Suna cin abinci da Inna, yau sun sami sauran biski daga gidan Sarki. Baba ya shigo babu sallama sai surutai ya ke kamar mahaukaci saban kamu, fad’i ya ke
‘’ta na ina ne wai ma?’’ ganin su a tsakar gida ya ja ya tsaya ya na mai fad’in
'’yo to ashe ku nan kusa ma’’

Inna ta yi kasake kafin ta ce ‘’Hallo Malam Lifiya? Yau ko sallamar babu?’’
‘’sallamar kenan ai uwar matar sarkin Fabarusa’’ cewar Baba ya na mai duban Bintu da sai saka lomar biski ta ke, hannu baka hannu kwarya. Inna na murmushin jin maganar Baba, ta ce ‘’Malam yau kuma raha a ke ji?’’

Cikin jadadawa Baba ya ce ‘’yo to wani raha bayan yanzu waziri ke sheda min, nan da d’an kwanaki za a tura a tsaida ranar bikin Gimbiya Bintu’’ ya k’arasa maganar ya na mai washe baki wanda daga Inna har Bintu sun kasa gane manufar dariyar ta sa.

Inna ce ta ce ‘’ayyo, Gimbiya Binta ko? Ai yanzu haka maganar da mu ke kenan, Wallahi yanzu ta ke sheda min’’

Baba na mai duban Bintu ya kai mata dak’uwa ‘’ungo nan yar jakar uba!’’ baki cike da biski Bintu ta tsaya ta na duban Baba. Ganin haka Inna ta ce "Allah sarki, aradu ba munahinci ta yi ba, hira ce ta kawo maganar....’’

Cikin k’ulewa Baba ya ce ‘’yo to na gaji da wannan rashin fahimta ta ki Yagana, gide ina nuna mi ki annabi hallo ki na runtse ido, wannan(ya nuna Bintu da yatsa) ita za a amrar ga Sarki Abdulrahman na Fabarusa a matsayin d’iyar Sarki....’’ tuni Bintu ta kwarai, ta wanke Inna da biskin bakin ta tsabagen tari.



🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.



©Khadija Sidi.....✍🏼


1⃣7⃣




Inna na mai rafka salati gami da dafe k’irji ta ce
‘’lahaila haillallahu mahammada rasulilahi! Bintu kuma Malam? Me ya had’a Bintu da masarautar Fabarusa saboda Allah da manzan sa? Yo to da haka a d’au wuk’a a da6a mana sai mu san kashe mu ake son yi da hujja!’’

Baba na mai nuna Bintu da d’an yatsa wacce ta ke hawaye d’aya na bin d’aya ya ce
‘’ga ta ga ki nan dai shegen biko’’

Kuka Inna ta sa yayinda ta rungumo Bintu ta na fad’in
‘’bar kuka Bintu, bar kuka d’iyar arziki, addua shi ya kamata mu yi, innalillahi wainna ilaihiraji’un’’

Ganin haka Baba ya sa kai ya fice ya na mai fad’in
‘’kwa dai k’araci munahuncin ku, bakin alk’alami ya bushe’’

Ranar sam Bintu ba ta sami bacci ba, kwana ta yi ta na kuka. Shi kan shi yayan ta Habibu ya tausayawa Bintu, zai ji dad’in zama yayan matar sarki, amma kasancewar auren hatsari ne ya sa shi girgiza da juyayin abun.

Washagari da ciwan mara Bintu ta tashi, kasancewa al’adar ta ta sake dawowa, ga kuncin zuci da ya addabi rayuwar ta ya sa gaba d’aya ta fita daga hayyacin ta. Ji ta ke dama motar bayi sun tafi sun bar ta a makaranta, in ya so Aisar ya tafi da ita ta huta da wannan rayuwa mara ‘yanci. In kuwa ta tuna shikenan fa ba ita ba komawa makaranta, ita da Aisar sai dai ta hange shi a akwaitin talabijin idan Allah ya sa an nuna shi sai ta k’ara saka wani kukan har da shasshek’a. Ko damar shiga babban gida ba ta samu ba, haka kuma daga Gimbiya K’amariyya har Gimbiya Binta babu wanda ya bi ta kan ta. Musamma Gimbiya da buri ya cika.

Ranar sarki ya tara iyalen sa a turaka bayan Jakadiya ta tabbatar ma sa da inganci da ilimin Bintu akan sarauta kasencewar ta tashi gidan sarauta, wanda su ke da yak’inin lamarin da aka k’ulla zai daidaita ba tare da an sami akasi ba.

Zaune suke gaban Sarki, Hajja Kilishi ce zaune ta 6arin dama, kusa da ita Gimbiya K’amariyya da Gimbiya Binta ne zaune. Sai Uwar fada da kuma Inna Salti, kusa da ita autan ta Yarima Nadir ne zaune daga 6arin hagu. Gaban su kuma ‘ya’yan Sarki ne maza, ciki har da babban d’an sa, dokajin Sa’ayra sa wato Yarima Inuwa, kusa da shi Yarima Nuhu ne. Sai kuma daga can gefe Yarima Hassan da Yarima Hussaini, Yarima Hamza, Yarima Abdallah da kuma Yarima Ahmadu su ka yi na su dairar.

Jin batun na Sarki, idan aka d’auke Gimbiya K’amariyya da Gimbiya Binta da dama ita ta kulla k’ulalliyar babu wanda be girgiza ba. Yarima Inuwa ne ya duk'ar da kai kana ya ce
‘’Allah shi ja da ran Sarki, shin an zatar da hukunci ne ko kuwa ana buk'atar shawara daga iyalan Mai Martaba?’’

Sarki na mai duban sa ya ce
‘’mun gama yanke hukunci, amma jin ta bakin ku ba laifi ba ne’’

Jin haka sai Yarima ya ce
‘’Allah shi kyautata lamarin Babban biji, komai ku ka zartar daidai ya ke, ina ga zai fi kyau a duba lamarin nan saboda gaba, ran Mai Martaba ya dad’e’’

‘’Allah ya ja zamanin Takawa, ni ma dai hakan zance, dan kuwa gaban ya fi baya yawa, muddin ba za mu iya yin yanda su ka tambaya ba, zai fi kyau a yi watsi da maganar gaba d’aya in ya so sai mu nemi taimako wani wajan daban ko kuwa a amra masa K’amariyya yanda ya buk’ata’’

Inna Salti ce ta ara ta yafa, dan kuwa kusan ta fi kowa jin d’acin maganar cikin matan Sarki, hakan ya sa ta kasa yin shiru. Tun da ta fara maganar Gimbiya K’amariyya da Gimbiya Binta ke hararar ta ta wutsiyar ido. Shi kuwa Yarima Nuhu tun da aka fara maganar ya ke son furta abun da ke ran sa, jin Yarima Inuwa tare da Inna Salti sun share masa fage be yi k’asa a gwuiwa ba ya ce

‘’Ran ka shi dad’e, ka gafarce ni, amma ni a nawa wautar wannan lamari ba shi ne mafita ba, shin ya za mu yi a warware wannan sak’ar idan har aka kulla? Menene makomar wannan baiwa idan Allah ya sa Masarautar Fabarusa su ka gano wannan lamarin? Menene mazaunin wannan Masarauta ta mu? Shin gaba ake san kawarwa ko kuwa wata gabar ake san kullawa? Wannan tunani ya sa na yarda da Inna Salti, mu yi yanda Masarautar Fabarusa ta buk’ata ba tare da wani sark’akk’iya ba, ko kuwa zai fi kawai mu hakura da batun gaba d’aya in ya so mu nemi taimako a wata Masarautar ko ma Gwamnatin tarayya duk da dai shugaban k’asa be da lafiya, da lafiya ya ke na san da ba a kai ga haka ba, kuma ba za a rasa wanda zai duba wanga lamari ba’’

Ko da Yarima Nuhu ya dasa aya, Gimbiya Binta ji ta yi kamar ta kurma ihu, ita kuwa Gimbiya K’amariyya har ta fara kwalla ganin Yarima Nuhu na neman dawo da gaba baya. Shiru ya biyo baya. Har sun fitar da rai da k'ara jin maganar Sarki, daga bisani ya numfasa ya na mai duban Hajja Kilishi ya ce

‘’wani shawara za mu ji daga gare ki? Shin kin amince mu aurar da d’iyar mu ga abokan gaba ko kuwa mu sake neman taimako wanda hakan jinkiri ne wanda ya ke barazana ga rayukan talakawan mu?’’

Hajja Kilishi na mai nusar da kai cike da kissa ta ce
‘’lafiya toya matsafa, lafiya waliyin Allah, lafiya baya goya marayu, lafiya adali! Hukuncin ka daida ta Saka Takura, mun ji mun kuma amince’’

Sarki na mai nuna jin dad’i da batun Hajja Kilishi, haka ya bi sauran iyalan sa kowa na fad’in na shi albarkacin bakin. Duk da Sarki ya san Su Inna Salti, Yarima Inuwa da Yarima Nuhu sun fi gaskiya, sai ya bi san ran sa tare da kafa hujjar an rinjaye su, dan haka maganar ta tsaya. Da wannan su ka watse kowa da abun da ya ke sak’awa cikin ran sa. Musammam Yarima Nuhu wanda ba tun yau ya ke da k’udirin mallakar Bintu ba, ko da kuwa a matsayin sad’aka ce, tin da wata baiwa ta kawo masu tsirkun abun da ta ji Gimbiya Binta da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login