Showing 15001 words to 18000 words out of 44561 words

Chapter 6 - Bintu Diyar Bayi Ce 1 Complete Hausa Novel

06 Jan 2025

154

hukunci daidai da yanda ta aikatawa yar uwar ta’’ ya na gama magana ya fice in da ya bar Malam Hashim ya na mai zubewa bisa kujera yayinda ya ke goga zufan da shi kan sa be san ya tsefo masa haka da yawan gaske ba. A waje Aisar ya tadda Bintu da Iya Dije tsaye suna jiran tsammani, be iya kallan in da Bintu ta ke ba tsabagen haushin kan sa da ya ke ji akan abun da ya jawo mata. Kana ya dubi Iya Dije ya ce ‘’ko zan iya samin Ciseaux da sabuwar reza gun ki Iya Dije?’’ Cikin fad’uwar gaba Bintu ta d’ago kai ta na mai duban Malam Aisar, sai a sannan ta lura da yanayin shi da ya canza gaba d’aya, ya zama kamar ba shi ba tsabar 6acin rai. Murya a sanyaye ta ce ‘’dan mai sama Monsieur (Malam) ayi hakuri a bar maganar ga, yo to menene dan an aske gashin niya?(menene dan an aske gashi na), in dai dan niya ne arudu na gafarce ta’’

Kallan ta Aisar yayi ba tare da ya tanka mata ba ya sake maimaitawa Iya Dije tambayar, ganin haka Bintu ta sawa bakin ta sakata, in da Iya Dije ta amsa da ta na da su duka, ya ce to ta kawo masa filin taron d’alibai(assembly ground) yanzu ba tare da 6ata lokaci ba. Ya wuce ya bar Bintu da bin bayan sa da ido. Ita kuwa Iya Dije jiki na b’ari ta nufi 6angaran su dan d’auko sak’on Aisar.

A wajan taron d’alibai(assembly), d’alibai da malamai babu wanda be hallara wajan ba, filin ya cika mak’il. Bayan sun yi abin da su ka sabayi kullum, wato na daga al’adar makarantar ne aka bawa Aisar filin. Gannin shi gaban su d’alibai su ka yi tsit, ita kuwa Marry zawo ne kad’ai be zubo mata ba, musammam ganin Iya Dije tsaye kusa da Aisar hannun ta ruke da almakashi. Kamar saukar aradu haka ta ji sunan ta bakin Aisar, bayan ya kira Bintu. Nan da nan d’alibai su ka shiga bud’a mata hanya, da kyar ta ke iya d’aga k’afa ta na takawa saboda tsabagen nauyin da k’afar ta yi mata, har ta kai ga Aisar da tun fitowar ta ya ke mata kallan hadarin kaji.

Jin umarnin da Aisar ya bata na da ta juya ta tsugunna bisa gwiwowin ta gaban d’alibai ya sa ta matsawa kusa da Aisar ta na magana a hankali dan kar a ji abun da za ta ce tace ‘’dan Allah Monsieur (malam) ka taimaka kada su raina ni’’ wani irin tsawa ya daka mata ya na mai fad’in ‘’matsa min daga nan in ba haka ba ina kishe ki a nanniya!(in ba haka ba ina dukan ki a nan)’’ da saurin ta ta ja baya, ba ta san sanda ta zube k’asa ba jiki na 6ari. Ba tare da wani dogon bayani ba, haka ma d’alibai ba sa buk’ata dan kuwa gaban su aka yi komai dan haka Ciseaux din hannun Iya Dije ya kar6a ya na mai mik’awa Bintu ya ce ‘’kyarbi ki mata abin da ta mi ki jiya!’’

Hannun Bintu na rawa amma ta kasa d’aga su ta kar6a, cikin magiya ba tare da ta iya furta wani abu ba ta ke kallan Aisar ta na mai girgiza masa kai. Ga mamakin kowa sai jin Aisar cikin rarrashi ya ce da Bintu ‘’kar6ar wanga Ciseaux tare da yiwa wanga azzalumar aski shi ne hukunci mahi(mafi) sauki a gare ta, idan ba haka ba barin wanga École nan har abada ba tare da ta gama jarabawar ta ba ya kamata, za6in na ki ne’’ jin haka tuni waje ya kaure da hayaniya d’alibai, masu tausayin Mary da masu Allah shi k’ara wanda su suka fi yawa, in da yan aji shida kuwa idan ran su yayi dubu ya 6aci, dama duk ajin Mary aka fi tsoro, ita ce mai kankaro mu su girman yau ga ta tsugunne gaban kowa kuma a wulk’ance, tsabagen d’ibar albarka ace yar aji uku ce za ta mata aski! Gaskiya sun zube ba nauyi. Sai ga hawaye sha6e sha6e a fuskar Mary.
Tuni zufa ya fara kyetowa wa Bintu, musammam da ta kai kallan ta ga Malam Hashim ya gyad’a mata kai dan kuwa dai ba kukan sa ba uwar kishiya ta mutu. Wata malama ce wacce dama ta dad’e da tsanar Mary ta k’araso kusa da su ta na mai fad’in ‘’ Monsieur ba ka san halin wanga d’ya ba ne (wannan yarinyar ba ne), in aka biya ta za mu shekara nanniya ba tare da an samu abun da ake so ba, bari kawai ni na taimaka mata da zab’in’’ ta na magana ne in da ta ke aikawa Marry da sako murmushin yayinda ta sa hannu ta cizge kallabin Mary, Mary ta yi saurin d’aura hannayen ta bisa kan ta domin 6oye cinyayyen gashin ta, ai ganin gashin sai ga d’alibai na darawa.

Muryar Mary na rawa ta ‘’in ki na yiwa Allahu ki yi hakuri Madame , kwankwatsi (rantsuwa) na tuba, dan Allah kada ki yanke min suma ta’’ cike da mamaki ta ce ‘’yo ba ki so a yanke na ki shine ki yanke na wata, aradu kwal kwabo zan mi ki ma kuwa, Iya Dije ruk’e min hannun ta’’ ganin Iya Dije ta yo kan ta, ta saurin sauke hannayen ta k’asa, ta na ji ta na gani Malama ta sai ta almakashi bisa d’an gunjin ta, ta daidaici rabin gashin cikin hikimar raba kan gida biyu, ta fara cire na sama sama. Dake Malamar ma ta na fama da mugun ta, sai da ta karb’i sabuwar rezar hannun Iya Dije, ta kwashe rabin gashin Mary tas sannan hankalin ta ya kwanta.
Fuskar Mary ba k’aramin muni ta yi ba da kai rabi kwakwaido rabi kwal kabo, ko da yake dama yaya bare sarki ya aiko. Dan kunya da takaici ta kasa ko da motsi bare ta iya d’aga idanun ta ta kalli jama’a, d’alibai ba su fasa ihu da sowa ba, musammam da malamar ta ce ayiwa Marry ihu, su ka d’auka ‘’ihu dube ta kwakwaido da kwal kabo’’ Malam Hashim ne ya matso gaba, in da ya kira Shedigyal da Sikanti, ya had’a har maryam ya kwace kallabin muk’amin su, ya kuma jaddada hukunci mai tsanani ga duk d’alibar da aka k’ara kamawa da makami ba tare da kwakkwaran daliliba, ko da kuwa reza ne.


Farin ciki gun d’alibai be musaltuwa, dan kuwa kurace ta mutu, sun huta. Gimbiya kuwa tuni ta sha jinin jikin ta ganin yanda Aisar yayi ruwa yayi tsaki bisa ga lamarin, batun akwai wani abu tsakanin Bintu d’iyar bayi da Malam Aisar tun daga wajan ya fara shawagi tsakanin d’alibai. Har aka sallame su Mary ba ta iya tashi daga tsugunnan da ta yi ba, sai da yan aji shida su tada ita, nan ta saki kukan da dama ya tsaya k’ark’ashin mak’oshin ta, ba ta ta6a jin ta tsani kan ta ba kamar ranar ba. Ko da ya ke ba ita kad’ai ba duka yan aji shidan ma hakan ta ke. Sauran d’aliban kuwa yau ta ke sallah, dan kuwa abin da aka yiwa Bintu gaba ta kai dan sun sami sakewa da wa tayawa, a ranar Bintu ta yi farin jini sai san barka ake yi mata, hatta Gimbiya a ranar sai da ta sarara mata.




🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪


ZUWA GA MASOYA "BINTU 'DIYAR BAYI" INA MAI NEMAN AFUWAN KU NA JINKIRIN SHAFI NA GABA DA ZA A SAMU, HAR ZUWA JUMA'A SABODA WANI UZIRI BABBA DA YA SHAFI WANI KARATUN DA NA KE. MADALLAH DA KU. SIDIYA CE KE MU KU FATAN ALKHAIRI🤝


©Khadija Sidi.....✍🏼

0⃣9⃣




Ranar da su ka gama jarabawa da yammaci, ana gobe za su tafi gida, Gimbiya Binta ta ce da Bintu ta raka ta wajan Aisar, dan ta ga idan su na tare ne kad’ai ya ke d’an sakar mata fuska. Sanye ta ke cikin doguwar riga ta alfarma kalar ja, dake Gimbiyar fara ce ba karamin kar6ar ta kalar ta yi ba, ita kan ta Bintu sai da ta yaba da kyawun Gimbiya cikin ran ta. Bintu kuwa kayan su na bayi ne jikin ta, kan ta tufke da kallabi, jin Gimbiya ta ce za su gun Aisar ya ta ware kallabin dan ya dan rufe mata jiki, amma duk da haka iya ka wuyar ta ya ya tsaya, gashi ita ba mayafi gare ta ba.

Gimbiya tafe Bintu na biye da ita ba su zame koina ba sai ofishin malamai. Malaman duka ba sa nan, daga Aisar sai wani malami da su ke kira Malam Sunusi, shi ma d’in su na shiga ya na fita. Malam Aisar da ke zaune bisa kujera ga teburi gaban sa ya na rubuce rubuce, sanye cikin wannan shigar ta sa dai, ko da ya d’aga ido ya ga su Bintu sai ya dakatar da rubutun da ya ke ya na mai aikawa Bintu murmushi. Ita kuwa ta kau da kai karda Gimbiya ta gani ta shiga uku.

‘’assalama’alaikum warahamatullah’’ sallamar Gimbiya kenan gare shi, ya amsa da ‘’wa’alaikum salam’’ Bintu kamar munafuka sai 6uya ta ke bayan Gimbiya ma sallamar ta masa a tak’aice, ya amsa ya na mai k’arawa da ‘’Bintun Sa’ayrasa, ya ki ke 6uya ne, fito sarari mana’’ Gimbiya ta juyo ta watsa mata harara. Jiki a sanyaye, kan ta sunkuye Bintu ta fito sarari. A sannan Malam Aisar ya lura da shigar da ta yi, sai dai duk sanda ya ke ganin ta da irin shigar be tab’a ganin ta sa riga k’arama wacce ta kama ta kamar ta yau ba, gashi zani ne d’aure jikin ta kuma ya fi fitar da surar mace, dad’in dad’awa kuma gashi Bintu ba kad’an ba duk da dai yarinya ce.

Nan da nan su ka nemi fara’ar da ke fuskar Aisar su ka rasa, har sai da Bintu ta tsargu ta d’an ja da baya, Aisar na mai d’auke kai da barin kallan ta ya ce ‘’dole ki 6uya mana, tin da kin hito(fito) yawo ba mayafi da irin wanga shigar!’’ Bintu ta sunkuyar da kai ta na mai tunanin ko dai ya manta da tsayuwar Gimbiya a wajan ne ko me? Allah ya sa kar ya ja mata jaraba. Gimbiya na kallan ikon Allah cikin ran ta fad’i ta ke ‘’aikin banza kyaramuwa tsaftar yaye!’’, Aisar be gushe ba ya k’ara da ‘’kul kar ki k’ara hita(fita) haka ko da a masarautar ku ne!’’ Bintu ta amsa da ‘’toh’’

Gimbiya ya ce ta ce "Monsieur Ina wuni’’ ba tare da ya kalle ta ba ya ce ‘’lafiya’’ ganin haka ta ce da Bintu ‘’Gide hita (fita) waje ki yi jira na....’’ be jira amsar Bintu ba yayi saurin katse Gimbiya ta hanyar fad’in ‘’idan kin hita ki wuce d’aki kar ki tsaya waje da wanga shiga ta ki, idan kin gama kya same ta ca’’
Cikin sauri Bintu ta bar wajan ta na mai hamdalar ceton ta da Allah yayi. Bayan fitar Bintu maimakon ya tsaya ya saurari Gimbiya sai ya cigaba da rubuce rubucen sa, kamar be ma san ta na wajan ba. Kamar za ta juya sai dai ta d’aure ta ce ‘’Malam gobe za mu koma gida’’ ba tare da ya d’ago ya kalle ta ba amsa mata ‘’sai aka yi yaya?’’ Gimbiya ta d’an cije le6e kafin ta ce ‘’dama zuwa na yi na maka sallama, na kuma gayyace ka zuwa masarautar mu idan da hali’

‘’na gode da sallamar, sai dai masarautar ta ku ce ban da lokaci’’ amsar da ya bata kenan. Kana Gimbiya ta dad’a gwada sa’ar ta ta hanyar fad’in ‘’dama wai ina nufin in ka sami lokaci.....’’
‘’ban da wannan lokacin’’ ya katseta ya na mai kafe ta ido. Ganin haka Gimbiya ta cije le6e ta na mai hamdalar korar Bintu da ta yi da yanzu gaban ta Aisar zai mata wannan cin fuskar. Fuuu ta juya ta fice ba tare da ta sake tankawa ba. Sai da ya ga ta fita ya aja rubutun ya na mai jan tsaki, takaicin sa na ganin ta na masa yawo da Bintu haka babu mayafi, ko wani kare da biri ya kalla! ‘’ba dan karancin shekarun wangad’iya ba, wallahi ba d’iyar bayi, ko d’iyar bola ce sai na aure ta! Amma ba komai lokaci ne ni Aisar mai hakurin jira ne’’ furicin Aisar kenan azahiri ya na mai jadda batun kawo kanwar sa Maryam makarantar ko ba komai ta ke saka Bintu a hanya. Tsaki ya sake ja ya na mai tura rubutun da ya ke gefe dan kuwa lamari in dai akan Bintu ne ya na jagula masa lissafi.

Komawar Gimbiya Binta d’aki kan Bintu ta sauke takaicin ta, laifukan na Bintu da yawa ciki har da ta na sane ta bita gun Aisar babu mayafi tsabagen ta na so ta yi masa tallar jikin ta, an fad’a mata shi d’an iska ne? Ta ji dad’in yanda ya yiwa Bintu kurar kare, da kuma ta ce ta jira ta waje shi ne ta bi umarnin uban ta ta koma d’aki.

Aiki tuk’uru ta saka ta wanda tun da Bintu ta zo duniya ba ta tab’a yin irin shi ba, hatta kayan ta da ke wanke a goge sai da ta sa Bintu dad’a wankewa da guga, dare yayi kuma ta tura ta lungu cikin sauro, nan Bintu ta kwana ta na mai adduar Allah ya sa iya haka hukuncin Gimbiya ya tsaya, ba za ta aiwatar da alkawarin sakawa a cire ta daga makarantar ba.

Washagari da ruwan sama aka tashi, motocin Sa’ayrasa na d’aya daga cikin motocin da su fara isowa. Sai da ruwa ya d’an tsaya sannan bayi da fadawa su ka taimakawa Bintu wajan kwasar kayan Gimbiya, har ya rage akwaitin karfen Bintu kad’ai ya rage a d’akin. Ita kuwa Gimbiya yar sarki mai dole kuma ta na jira a take mata baya zuwa mota, haka Bintu ta na ji ta na gani ta bar akwatin na ta su ka takawa Gimbiya.

Ta na shiga mota ta juya da niyar komawa ta d’auk akwaitin na ta, Gimbiya ta tsiyar da ita ta hanyar daka mata tsawa ‘’gide ina kuma za ki?’’ dan a zatan ta wajan Aisar Bintu za ta. Ko da Bintu ta fad’a mata cewar akwatin ta za ta d’auko, minti gama kacal Gimbiya ta bata idan ba haka ba za ta taka zuwa Sa’ayrasa da k’afar ta. Hanyar da za ta kai ta ga d’akin na su Bintu ta kalla, ko zuwa bakin kofar b’angarn sai ya fi minti goma bare kuma ga hawa bene ga nauyin kaya. ‘’ki nan tsaye ne? idan kin fasa ma iya tafiya’’ furucin Gimbiya cike da tak’ama.
Cikin hanzari Bintu ta ce ‘ tuba na ke ran Gimbiya shi dad’e’’ kafin ta tafi da sauri, sai da ta tabbata ta wuce ganin su Gimbiya sannan ta arta a na kare. Ta na ji wasu na ‘’fad’in ku kauce ta fara gudun na ta na masifa’’ har dariya ake mata ita kuwa ba ta san suna yi ba. Haurawa ta yi ta d’auki akwaitin ta bisa kan ta. Ta fito daga sashin kwanan na su kenan kamar daga sama ta ji an d’auke ma ta akwatin daga kayin ta.

A tsorace ta juya sai ga Aisar sanye dai da shigar nan nasa, amma yau fara ya sa, idanun sa rufe da gilashi, hannun sa ruk’e da wata leda mai d’an girma cikin nuna damuwa ya ce ‘’wanga ya yiwa d’iya mace nauyi’’ cikin kokawa Bintu ta ce ‘’dan Allah ka yi min rai ka bani na tafi, aradun Allah minti goma kacal Gimbiya ta ba ni’’ maimakon ya bata, sai ma dad’a ruk’e akwaitin yayi kafin ya ce ‘’idan kuma ki ka k’ara fa? K’ak’a za ta yi?’

Idanun Bintu na mai kawo ruwa ta ce ‘’aradu tahiyar su za su yi su bar ni a nanniya (wallahi tafiya za su yi su bar ni a nan)’’ Aisar na mai murmushi ya ce ‘’idan su ka tahi shikenan sai na tahi da ke gidan mu hankali kwance’’ ganin za ta sa masa kuka ya ce ‘’shhh..wasa na ke mi ki’’ akwatin ya aje k’asa sannan ya ciro zoben hannun sa ya mik’a mata ya na mai fad’in ‘’kan ki tafi ga ajiya ta Bintu, ina so ki aje min duk sanda mu ka sake had’uwa zan kar6a’’

Cikin saurin ya bar ta tafi, ba tare da ta kawo komai cikin ran ta ba ta sa hannu ta karb’a ta na mai k’ok’arin cusa zuben cikin zanin ta,ya ce ‘’ah ah a yatsar ki na ke so ki saka, nan ya na iya fad’uwa’’ ba musu ta fara k’ok’arin zira zuben, duk da ya so ya mata yawa ta samu ya shiga yatsar tsakiyar hannun ta na dama. Ta yunk’ura za ta d’au akwatin kenan Aisar ya riga ta cikin zafin nama, ya wuce gaba abun sa, da sauri ta bi bayan sa ta na mai fad’in ‘’ Monsieur ka bani akwatin dan Allah’’ shiru ya mata, dake Aisar mutum ne mai kuzari, nan da nan su ka isa ga motocin Sa’ayrasa. Bintu sai karanto adduoin da ta koyo makarantar allo ta ke dan neman tsari daga masifar Gimbiya, dan ba ita kad’ai ba ma kallo da zund’e da ta sha wajan sauran d’alibai ma sai Allah, musammam yan aji shida da dama sun gama tsanar ta, yau ga Aisar Gaddafi Nur yayi dakon akwaitin d’yar bayi. Shi kuwa gogan na ta ko a jikin sa wai an mintsli kakkausa.

Suna isa ya sakar mata murmushin da ita kan ta Bintu ba ta san na menene ba, ita dai ta na ganin sabon salo kiran sallah da husir, kana ya ce ‘’wata motar Gimbiya za ta shiga’’ Bintu ta amsa da ‘’ai Gimbiya ta na cikin waccar motar’’ ta masa nuni ga motar da Gimbiya ke ce. Aisar ya kai kallan sa ga motar, ko da yayi ido hud’u da Gimbiya, duk da 6acin ran da ta shiga ganin Aisar d’auke da akwatin Bintu, sai da ta tsinci kan ta ta na mai sakarwa Aisar sakon murmushi. Yayi saurin maido da kallan sa ga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login