Showing 3001 words to 6000 words out of 44561 words

Chapter 2 - Bintu Diyar Bayi Ce 1 Complete Hausa Novel

06 Jan 2025

146

ha a mata ruwan wanka. Wajan cin abunci ba ta isa ta zauna cikin yan uwan ta alibai ta ci abunci ba,sai dai ta jira Gimbiya ta gama,ta raka ta aki ko aji sannan ta dawo ta ci na ta. Kuma a duk in da su ke sai ta tabbatar kowa ya san Bintu iyar bayi ce, shi ya sa ma ta hana ta sa kaya in dai ba shigar bayin Sa’ayyarasa ba idan ranar sa kayan su na gida yayi.

Allah ya yiwa Bintu wani abu wai shi tsayi da diri,dan kuwa jikin ta ya girmi shekarun ta. A shekarun ta tana da zubin cikakkiyar budurwa idan ba fuskar ta aka kalla ba ba wanda ba ya b'oye shekarun na ta.

Bintu baka ce,irn bakin nan na wayayyun matan nan da ba sa shafa man da zai sake mu su kala. Doguwar fuska gare ta,amma ba mai tsayi sosai ba,ta na da manyan idanu ga hanci har baka,sai wushirya da ke mata kyau duk sanda ta dara ko ta bu e hakora. Ta na da suma matuka,ko ta aure kan ta da kallabi yawan sumar be b’oyuwa.

Daga ita har Gimbiya Binta aji uku suke. Ba ta da buri da ya wuce su kai aji shi da su gama makarantar ko ta huta da jarabar Gimbiya,dan kuwa ko k’awaye Bintu ba da shi a makarantar.

Aisar Gaddafi Nur

Aisar saurayi ne mai kimanin shekara talatin a duniya. Aisar ya da e cikin aikin sa da ya ke matuk’ar so tun kan mahaifin sa ya zama shugaban kasan jamhuriyyar Nijar. Aiki ne wanda ake mu su lakani da mutan b’oye,wato masu bincike da kula da kasa amma ta k’ark’ashin k’asa. Tin hawan mahaifin sa kujerar shugaban k’asa ya na ji ya na gani dole aka dakatar shi saboda yanayin aikin na su na sirri ne hatta sunan da ya ke amfani da shi cikin aikin da ban ya ke da sunan sa na yanka,ba zai yiyu a ha a da siyasa ba dan ba mamaki ma wata rana aiki ya bi ta kan gidan na su. Amma shi ba haka ya so ba. Hakan ya sa sam Aisar ba ya san shiga sabgar gidan gwamnati ko abun da ya shafi harkar siyasar baban shi. Ko zama gidan shugaban k’asan ma be cika yi ba,in ka gan shi ciki toh wajan iyayen sa ya je gaidawa ya tafi,in da Allah ya taimaka ba shi ka ai ba ne ya na da yayye ba laifi, dan ba kowa ba ne ma ya san shi a matsayin an shugaban kasa. Hakan be sa kungiyar Aisar janye dakatar da shi da su ka yi ba,har ma ya fidda rai ya hakura har sai baban shi ya sauka kwatsam ya ji kiran aiki na wani bincike da ya bi ta kan wani kamfani da ke kusa da makarantar su Bintu. Yayi murna kwarai duk da kuwa aikin ba nasa ba ne,shi kawai taimako zai yi shi ya sa sai dai ya rab’uke daga gefe har sai lokacin taimakon yayi. Kungiyar ta su ce ta ba shi izinin neman koyarwa a nan makarantar ta sovereign girls secondry school,su ka kuma ce ya je da sunan sa na ainihi tun da hawan baban sa mulki an fara ya awa cewa ya na kungiyar,kasancewar shi cikin makarantar shi zai ba su damar yin basaja,yanda wancan kamfanin ba za su yi zargin su ake bi ba har su gama binciken su.

2/01/2000
Zaune su ke cikin aji. Kamar yanda ta saba kujerar ta na bayan na Gimbiya Binta. Ta doka uban tagumi in ban da k'ugin yunwa babu abun da cikin ta ya ke dan kuwa raban ta da abunci tin na dare da ke yau sun makara, hakan be sa Gimbiya ta aga mata k’afa ba ta bari ta ci abunci lokacin da ta ke cin abunci,kafin ta gama kuma aka shiga aji. Ta na ji ta na gani sai hakura ta yi.

Duka duka ba su kai talatin ba cikin ajin amma gaba aya sun ciki ajin da surutu. Hirar abubuwa masu tsada da k’asashen da su ka tab’a zuwa kowa ya ke. Ita kuwa Bintu da hirar ta su ko hankali ba ya bata sai hamma ta ke,ta kalli agogon bangon ajin,awa aya ya rage a fita gajeran hutu dan cin abunci. Malamin da ya kamata ya shigo kuma ya ki shigowa, sai kawai ta kifa kan ta bisa teburi.

Shirun da ta ji anyi ya tabbatar mata da Malam ya shigo aji. Ta yi sauri ta ago kan ta sai gashi kowa ya tashi tsaye ita ka ai ce zaune,baki bu e ganin wanda ya ke tsaye gaban ajin. Kamar yanda ta gan shi jiya yau ma bak’ak’en kaya ne sanye jikin sa,idanun sa rufe da bakin glass. Da kyar ta sa mu ta ja jikin ta ta tashi.

Gaishe su yayi cikin harshen turanci nan da nan su ma su gaishe shi. Ya umarce su da su zauna. Da zaman su da jin wani abu ya sauko mata lokaci guda ne,ta yi kasake ta na tunanin wannan wani irin saban lamari ne? Can dai ta yi tunanin dan wannan abun da ya saba zubo mata lokaci lokaci ne.

Malam ya gabatar da kan sa a matsayin saban malamin su na fannin zaman lafiya da sulhu [peace and conflict resolution" ta re da fa a ma su sunan sa wato Aisar Gaddafi Nur. Ko da jin sunan aji aka fara kus kus, daga fa in

"Gaddafi Nur shugaban kasa?’’
sai mai fa in
"haba da ma ni na ga yayi min kama da wanda na sani,ashe dan shugaban kasa ne’’
wata kuma
"toh me zai yi da koyarwa kuma?ba mamaki su nan ne ya zo aya dan kuwa an shugaban kasa ya fi karfin koyarwa’’

Ita dai Bintu ta saki baki ta na kallan sa,shi ko lura da ita be yi ba. Gashi ta na fama da wani saban lamari da ke zubo mata har ta na ji ta an fara jikewa. Tun ta na gane abun da ya ke fa a har ta zo ta dena dan kuwa ta fita hayyacin ta. Har fitar sa be lura da ita ba,ita kuwa gaba aya hankalin ta a tashe ya ke ganin abun da ya b’ata ba kayan makarantar ta ba hatta in da ta ke zaune.

Aisar na fita jiniya ta yi k’ara,lokacin fita hutun karamin lokaci yayi,dalibai su ka fara fita domin cin abunci da sauran su. Amma tashi ya gagari Bintu. Jaka Gimbiya Binta ta cilla mata yanda ta saba,wato ta auka ta biyo bayan ta. Murya na rawa Bintu ta furta

"dan darajar Allah Gimbiya ki yi min rai ki gafarce ni,na tuba’’

cike da mamaki ta juyo ta na duba ta,yan aji tuni kowa ya watse daga ita sai kawayen ta biyu masu masifar girman kai,Ruqayya da Zahira.
Zahirar ce ta ce
"kun ga shashashar banza,me ki ka yi da za ki hau magiya kamar iyar marok’a?’’
Ruqayya ta amsa da
"to menene banbamcin iyar bayi da ta marok’a?’’

Cike da nuna b’acin rai Gimbiya Binta ta ce ‘’jakar tawa ce ba za ki sami damar auka ba ko kuwa tashin ne ya gagare ki?’’

Bintu na kuka ta ce
"Allah shi taimake ki,wani abu ne kamar jini ya zubo min.......’’

‘’JINI!’’

Ruqayya da Zahira su ka ha a baki yayin da su ka ja gefe cikin nuna kyamkya mi. A wulakance Gimbiya ta ce
"duk sanda jinin ya dena zubo mi ki kya tashi,dan Allah ku zo mu tafi ko na dai na ganin wannan k’azantar’’

Zahira ce ta auki jakar na ta su ka tafi su ka barni. Tini duk wata yunwa ta dena jin ta,ta aura kan ta bisa taburi ta na hawaye,ta rasa in da za ta sa kan ta.
Ba ta jima a haka ba ta ji wani sanyayyen kamshi ya bakonci hancin ta,a hankali ta ago. Hannun sa ruk'e da bakin gilashin sa,fuskar sa auke da alamar tambaya, ya ce

‘’wannan fuskar ina na san ta ne?’’

Bintu ta yi saurin kau da kai gefe ta na mai adduar Allah kar ya tuna. Ai kuwa dai adduar ta ba ta karb’u ba jin ya ce

"Sa’ayyarsa,tabbas. Dama ke daliba ce a makarantar nan?me ya same ki ki ke kuka?ko dama ke kullum cikin tashin hankali ki ke? na wucewa na hango ki kai kife kan tebur bayan yan uwan ki dalibai suna can suna cin abunci’’

maimakon ta bashi amsa sai ta yi ka sake ta na kallan sa yayinda hawaye ke zuba daga idanun ta. Ya ce

"ba da ke magana ba?ba kya ji ne?’’ rasa abun da za ta ce masa ta yi sai hawaye kawai. Nan fa ya k’ule be sanda ya daka mata tsawa ba ya na mai fa in

"tashi tsaye na ce!’’

Ba ta san sanda ta tashi tsaye a gigice ba,nan idanun sa ya sauka bisa kujerar da ta ke zaune,sannan ya dawo da kallan sa ga kayan makarantar ta da ya b’aci.
®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪


©Khadija Sidi.....✍🏼

0⃣3⃣



Tausayin ta ne ya lullu6e shi,dan daga ganin yanayin ta ka san fararriya ce.
‘’zauna ina ki jira ina zuwa’’

Ya fad'a a sanyaye,kafin ya juya ya fita ba tare da ya jira ta amsa masa ba,dama ko ya jira in ma ba amsawa za ta yi ba. Cike da da kunya da takaicin yanayin da ya gan ta, ta koma ta zauna, gaba d’aya ji ta yi ta tsani kan ta,kan ta ta kifa bisa teburi. Jim ka d’an ta ji muryar d’aya daga cikin masu kula da d’akin kwanan dalibai,wacce su ke kira iya Dije,ta na fad’in
‘’wacece ne? d’ago kan ki na gan ki’’
Bintu ta d’ago kan ta a hankali ta dube ta. Ganin fuskar Bintu ga idanun nan na ta ya yi jajur dan kuka Iya Dije ta ce
‘’aw Bintu da ke ce?yo menene na kukan har haka? Ai girma ne ya zo,maza ungo wannan zanin ki d'aura mu je ki gyara kan ki’’
Ta mik’a mata zani,hannun Bintu na rawa ta kar6a da saurin ta. Ta tashi a hankali ta d’aura zanin ta na mai bin kujerer da ta 6’ata da kallo.
‘’kar ki wani damu da wannan, Shatu na nan tafe za ta gyara,ke dai mu je ki fara gyarawa tukun’’
Fad’in Iya Mairo yayinda ta d’auki jakar Bintu ta wuce gaba,Bintu na biye da ita. D’akin kwanan d’alibai su ka wuce, d’akin su Bintu ta zauna ta yi jiran ta bayan ta koya mata yanda za ta yi ta gyara kan ta. Sai da ta yi wanka ta shirya sannan ta wanke kayana da zanin da Iya Dije ta bata.
Bayan ta gama ne ta je ta sami Iye Dije zaune ta na jiran ta. Kamar wacce ta yi laifi ta d’an ra6e daga gefe,kan ta sunkuye ta ce
‘’Iya Dije na gode da kulawar ki,wallahi ba da sani na ba ne,ban ta6’a ganin irin haka ba’’
Murmushi Iya dije ta yi jin maganar Bintu,kana ta dafa kafad’ar ta tana mai fa’d’in
‘’Yaro dai Yaro ne,dama kowa akwai ranar da ya ke farawa,kuma kowace cikakkiyar budurwa ta na yi,auta ta ma ba ta dad’e da farawa ba’’
Da sauri Bintu ta d’ago kan ta ta ce "Allah? ita ma ta yi kuka?’’
‘’ah ah’’
Iya Dije ta amsa mata,sannan ta k'ara da
‘’da ke ta tashi cikin mata kuma ta na zuwa islamiya toh ta san komai,kawai dai ta shiga damuwa na rashin sabo,da fatan ki na dai zuwa islamiya a masarautar ku’’
Bintu na mai girgiza kai ta ce
‘’ah ah makarantar allo na ke zuwa,shi ma kuma sai idan babu aiki sosai a fada,da aka sani wannan makarantar ma sai na dena zuwa gaba d’aya’’
Iya Dije ta ce
"assha ai makarantar islama na da muhimmanci ga rayuwar d’iya mace, kin ga da kina zuwa da yanzu kin san duka hukunce hukunce da ya hau kan ki, lalle idan an yi huta ki ce da gyatumar ki ta sanya ki cikin islamiya, ba a tsufa da neman ilimi bare ke da kuruciyar ki kin ji ko?’’

Bintu ta gyad’a kai. Kana Iya Dije ta kara da
‘’yanzu hukunci babba ya hau kan ki tunda kin balaga, yanda za a rubuta wa mahaifiyar ki ko ni kai na hukunci haka ke ma za a rubuta mi ki dan kuwa yanzu mu da ke duk d’aya ne har ga Allah, kin tashi daga yarinya. Dan haka ki kula ki kyau ta ta rayuwar ki ta duniya da lahira, ki ruk’e mutunci ki da na iyayen ki. Ba ruwan ki da maza muddin ba da kwakkwaran dalili ba,kin dai san mai wasa da maza karya ce ko?’’
Kai sunkuye Bintu ta jinjina kai alamar ‘’eh’’ Iya Dije ba ta gushe ba ta k’ara da
‘’yauwa, wannan sabon Malamin da ya zo yayi kira akan ki, menene dangantakar ku?’’
Nan fa Bintu ta fara kame kame, ta ce
"iye? na’am? Wai wannan d’in nan? wallahi ni ma ban san shi ba Iya Dije,yau ya fara koyar da mu fa"
Cikin nazari Iya Dije ta kura mata ido kafin daga bisani ta nisa ta ce
‘’kar ki saki jiki da kowane d’a namiji muddin ba muharramin ki ba ne, wato wadda babu auratayya tsakanin ku, kar ki sakarwa kowa fuska ko hannu kar ki yarda wani ya ta6’a ruk'e mi ki idan ba haka ba mutuwa za ki yi,kin ji ko?’’
A tsorace dan ta ji batun mutuwa ta amsa da
‘’Toh, wallahi dama ni ba ruwa na da maza, ko a masarautar mu ma ba na sakar mu su fuska, yaya Ubaliya ma sheda ta ne’’
Kai Iya Dije ta jinjina alamar gamsuwa. Nan ta cigaba da bawa Bintu shawarwari. Ko da ta zo tafiya har ta kai ga k’ofa ta ce
‘’Bintu ya batun turare ina fatan dai ki na da shi, dan yanayin da ki ke ciki sai fa da turaren’’
Bintu na d’an soshe soshe ta ce "Iye?dama dai Inna ta ta bani garin alimun ta ce ina had’awa da leman tsamin sai na ke gogawa a hammata ta’’
‘’eh toh wannan ma ba laifi,amma ki na bukatar turare,dama wannan Malamin ya ce na fad’a masa idan ki na da bukatar wani abu,na fad’a masa. Kuma kar ki manta ki na canza wannan audugar da na baki a kankari, ban da k’azanta dan Allah idan ba haka ba kuwa za ki ji ki kina wari na gaske’’

Cike da jin kunya su ka yi sallama, Bintu ta mata godiya sosai. Bayan fitar ta ne ta ji yunwar da take ji ya dawo ma ta, saboda haka sai ta bu6e akwatin k’arfen ta,ta fito da ajiyar garin kwakin ta da kuli ta sha ta k’oshi. Ta na gamawa da saurin ta ta gyara wajan dan kar Gimbiya Binta ta gani ta zubar mata da ragowar. Ko da ta ga ta sami nutsuwa,ta shifid’a tabarmar ta, ta yi kwanciyar ta kafin lokaci ya cika ta koma aji. Gaba d’aya kunyar Malamin nan ne ke damun ta musammam yanzu da Iya Dije ta fed’e mata daga bindi har wutsiya na game da sabon rayuwar da ta shiga,ga shi shi dai kullum ba ya sa’ar ganin ta cikin hayyacin ta. Da wannan tunanin bacci mai dad’in gaske yayi gaba da ita.

Saukar marin da ta ji ya sa ta yi firgit ta tashi zaune hannun ta bisa kuncin ta ta na mai murzawa. Ba ta bari ta gama wastsakewa ba ta rufe ta da zagi, fad’i ta ke
‘’dan uban ki wannan bawan har ki zo ki kwanta ki na barcin asara kin manta bauta ya kawo ki makarantar nan? k’azama wawuya!’’
Da sauri Bintu ta d’urk’usa jika na b'ari ta ce
‘’Allah ya huci zuciyar gimbiya, tuba na ke, ban san sa’in da baccin ya sace ni ba, ki min aikin gafara’’
A wulak'ance Gimbiya Binta ke duban Bintu,kafin ta furta
‘’ga wanki can na su diras d’ina,bayan kin gama ki min guga. Kuma ki sani yau bazan iya kwana d’aki d’aya da ke ba cikin wannan k’azantar da ki ke. ki d’au k’azamar tabarmar ki ki aje daga can lungun,kuma ki san abun da za ki ce da su Iya Dije su ka gan ki a nan kwance dan idan ki ka kuskura ki ka kira sunana wallahi sai na lahira ya fi ki jin dad’i’’
Cike da ladabi Bintu ta duk’a ta na mai fad’in
‘’Godiya na ke ran ki shi dad’e’’
Gimbiya Binta ta k’ara da
"wallahi na tsane ki,duka cikin bayain fada babu wanda na tsana kamar ke,wai amma a rasa wacce za a had’u ni da ita sai ke!’’
Ta shure Bintu ta wuce ciki,kan gado ta nufa ta zauna d’ai-d’ai abun ta. Kai sun kuye Bintu ta tashi, ta nad’e tabarmar ta sannan ta kwashe wankin Gimbiya. Gaba d’aya a takure ta ke yin komai musammam yanda tafiya ma mai kyau da kyar ta ke gudun kar ta sake b’aci.

Sai da la’asar sakaliya ta gama wankin,bayan ta yi shanya ta na shirin fara guga su Zahira su ka shigo d’akin. Nan fa su ka zauna in ban da maganar Aisar babu abun da su ke.
‘’Aisar Gaddafi Nur ai ba k’aramin had’uwa yayi ba’’ fad’in Gimbiya,ta k’ara da
‘’ni abun da ke ban mamaki ganin shi a matsayin malami’’

"ko ni ma na yi mamaki gaskiya’’
Zahira ta taya ta.Ajiyar zuciya Gimbiya Binta ta saki kana ta ce

"ni fa k’awaye na wallahi na kamu, gaba d’aya ya shiga rai na’’

Maryam da Zahira su ka sa shewa, Maryam ce ta amsa mata da

"ai dama ni tuni na d’ago jirgin ki,kar ki damu ai jinin sarauta ba sa nema su rasa’’
‘’ko ba dan jinina ba ai na isa a soni,ba ku lura da yanda ya ke kallo na ba ne?’’
Fad’in Gimbiya cike da tak’ama, wanda hakan ya sanya k’awayenta yi mata kirari su na dad’a wasa ma ta kai. Bintu da ke jiyo su daga can gefe ta murmusa cikin ranta fad’i ta ke "Malam Aisar ya cika jarumi tinda har ya shiga ran Gimbiya’’ ajiyar zuciya ta saki ta na mai fatan Allah ya tabbatar da alkhairi.

*******
Kamar yanda Gimbiya Binta ta ce,ranar a d’an wani lungu cikin d’akin Bintu ta samu ta ra6’e. Da kyar ta iya samun bacci saboda sauro. Da asubar fari Gimbiya Binta ta tada ita,kuma ba ta bari ta yi amfani da band’akin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login