Showing 30001 words to 33000 words out of 44561 words
Jakadiya su na kullawa ya kasa sukuni. Ya had’a goma na arziki ya nemi amintacciyar baiwar sa, ya ce ta kaiwa Jakadiya, wato na sharan fage kenan kafin ya je mata da buk'atar sa.
Su Gimbiya kuwa ko da su ka koma na su 6angaran mamakin yanda Yarima Inuwa, Nuhu da Inna Salti su ka nuna k’iyayyar su k’iri k’iri ta hanyar k’in amincewa da wannan lamarin, a nasu tun da su ne su ke ciki d’aya su ya fi dacewa ace sun yi na’am da lamarin, amma ga mamakin su waccan da su ke kira yan bakin gida su ne su ka fi nuna kauna gare su.
Yarema Nuhu kuwa kai tsaye 6angaran sa ya nufa rai 6ace, babban takaicin sa shi ne a rasa baiwar da za a sa cikin wannan hatsari sai Bintun shi ta arziki, Bintu da ya dad’e ya na saka buri akan ta, gaskiya dole ya san yanda zai yi wannan maganar a rusa ta. Bakin kofa ya ci karo da Baiwar da ya tura gun Jakadiya, hannun ta nik’i nik’i da kayan da ya bata ta kaiwa Jakadiya. Da ganin sa ta zube k’asa ta na mai gaishe shi. Cike da mamaki ya ce
‘’ba ki kai mata sak’on ba ne?’’
Kai duk’e Baiwa ta ce
‘’Allah shi taimaki Yarima, Uwar baka ta sake hali, da na kalle ta sai dak'uwa ta min, kasan Jakadiya gara ce, ga tsiya ga rana, tsiyar ta ya fi ranar ta yawa’’
Jin haka ya gane me ya faru, ma’ana dai Jakadiya ta yi tsiyar ta, ta kuma k'i kar6ar tsarabar sa wanda hakan ya na nufin ba zai sami kowani taimako daga gare ta ba. Cikin zafin rai Yarima ya ce ‘’kya iya tafiya da kayan’’
Sannan ya tsallake ta ya shige ciki ya na mai bugo k’ofar. Yayinda baiwa ta had’e kaya ta yi gaba, Allah ya kashe ya bata.
A wuni guda Bintu ta rame ta lalace kamar wacce ta shekara ta na ciwo. Da Baba ya dawo da daddare ya ke sheda mu su an fa aika Fabarusa, zance ya tabbata nan da wata d’aya za a amrawa Sark’i Abdulrahman aure da Binta d’iyar Sarki Sule na Sa’ayrasa. Inna na mai d’aure fuska ta ce
‘’yo to tun da ba da Bintu aka ce ba ai can da su gada, ni dai d’iya ta ba sunan ta Binta ba, Bintu an sunan ta, haka kuma ba d’iyar sarki ba ce d’iya ta ce’’
Baba na mai duban ta ya saki murmushin takaici, kana ya ce
‘’ke kuma d’iyar wacece? Ko in ce ke wacece a Masarautar nan da ga ke har d’iyar ta ki?’’
Inna ta yi shiru, ganin haka Baba ya k'ara
'’shirun da ki ka yi ya tabbatar min da kin tuna ashefa ku bayi ne, dan haka ba ku da ‘yanci, ki ma godewa Allah da ya sa amrar da ita ya ce zai yi ba bada ita zai yi sadaka ko sad’aka ba, gide ke dai kin cika butulu. Toh ki saurare ni da kyau gobenan za a zo a tafi da Bintu ga babban gida, hallo dangin ki d’aya ba a yarda kin shedawa ba, yo to ina bayi ina wasu dangi ma in ban da ba'a"
Kuka Inna ta saka ta na fad’in ‘’wannan zalinci da ke shirin aikata min da wanga yarinya Allah shi isar mana’’
Ciki Baba ya shige kafin ya lek’o da kan sa ta assabari ya furta ‘’je ki tari Magajin Gabasawa ki sheda masa, yo to ba ni na kar zoman ba, rataya aka bani’’
Ita kuwa Bintu da ke jiyo su daga d'aki zuciya ne kad'ai ba ta had'iya ba, tunani ta ke ina ma Aisar ya na kusa ya kawo ma ta d'oki yanda ya [truncated by WhatsApp]®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣8⃣
Kamar dai yanda Baba ya ce, da sassafe sai ga Jakadiya da amintaccin bayin Hajja Kilishi sun dokowa Inna sammako. Dan takaici Inna d’auke kan ta yi dan kuwa ta kasa bud’e baki ta ce da Bintu ta fito ta bisu.
Tun da Bintu ta ji sallamar su ta shige bayan kofa ta yi zaman ta, duk da ta ji buk’atar Jakadiya amma k’yememe ta k’i fitowa. Ana haka Baba ya fito ya rufe Inna da fad’a
‘’Magajin Gabasawan za ki yi wa musu ko kuwa Jakadiya? Iye Yagana? Gide ban san tsaurin idanu fa! Yo to yau ko ke Magajin Gabasawa ya ce zai aura sauki zan yi bare ma wanga d’iya, aikin banza aikin hofi! Ta na ina wai? Gide Bintu hito ki bi su in ba haka ba ina make ke! kwankwatsi ma kuwa!’’
Jakadiya na murmushi ta ce
"Mahuta bi su a hankali, ai tsakanin uwa da d’iya sai Allah bare kuma ace za a raba su rana a tsaka, bi su a sannu Mahuta, in ban da ke da abin ki Uwar bayi wanga lamari ai alheri ne aka yiwa d’iyar ki, wanga abu abin san barka?’’
Idan Inna ta tanka ko shakka babu dutse ma ya tanka, ganin haka Baba ya wuce su izuwa d’akin Bintu, ya tadda ita bayan kofa ta had’a zufa da hawaye. Fad’a ya hauta da shi, ta in da ya ke shiga ba ta nan ya ke fita ba. Amma kyememe Bintu ta k’i motsawa bare ta fito. Aikuwa da Baba ya fusata sai ya hauta da zagi, jin haka Inna ta shige d’akin da sauri dan ta san daga nan kuma abun da zai biyu baya.
Ilekuwa shigar ta kenan ta ga Baba ya d’aga hannu ya na shirin kaiwa Bintu bugu, nan da nan ta shiga tsakani, ta ce
‘’haba Malam! Ai ka ji tsoran Allah abin ga ai sai yayi yawa maye da hauka!’’
Nan fad’an Baba ya koma kan Inna, ai lalle Inna ke d’aurewa Bintu, dan haka zai fita ya dawo, in dan ya dawo ya ga Bintu gidan nan sai na lahira ya fita jin dad’i. Dan masifa da bambami ko sallama be yiwa su Jakadiya ba ya sa kai ya fice ya na kumfar baki.
Bayan fitar sa Inna ta ja hannun Bintu su ka fito tsakar gida. Inna na mai duban ta ta ce
‘’Bintu idan har ni na haife ki, toh na baki umarni ki bi su ku tahi Babban gida’’
Bintu na jin haka ta zube k’asa, hannayen ta biyu ta sa ta ruk’o k’afar Inna ta na fad’in
‘’Inna na tuba, Inna ki gafarce ni, Inna ki min afuwa, Inna kar ki ce na bisu, Inna kar ki yarda a raba ni da ke, kwankwatsi na dena 6ata mi ki rai, idan na k’ara aratta kashe ni’’
Inna na mai janye k’afafun ta daga ruk’on da Bintu ta yi mata ta ce
‘’na yafe ki duk da ba ki ta6a sa6a min ba, ke d’iya ce ta gari, dan haka ki sa Allah a ran ki shi ne kad’ai ka iya mi ki, tashi ki bisu, Allah shi fisshe ki alkairi...’’
Ta na gama fad’ar haka ta shige ciki ta na hawaye. Nan fa Bintu kuka har da birgima. Su Jakadiya su na nan suna gani sarautar Allah duk da dai su ma kukan na Bintu ya so ya d’an ta6a su.
Habibu ne ya shigo, ganin abin da ke faruwa ya shiga rarrashin Bintu, har ya samu ta yi shiru. Ya ce da su Jakadiya su yi gaba gasu nan biye da su, bara ya had’o kayan Bintu. Jakadiya ta ce ah ah ba a bukata, ita d’in ta kad’ai ake buk’ata.
Gaba su ka yi, hannun Bintu ruk’e da na Habibu, su na tafe ya na bata baki da nasiha har su ka isa kofar Babban gida. Nan ma Bintu ta ce ba ta san zance ba, Habibu be isa ya koma ya bar ta gun su Jakadiya ba. Jakadiya ta fusata ta hau Bintu da fad’a
‘’yau ina ganin walele gi6in takwaru! Gaskiya ne komai girman d’an mara kabo be isa aure ba! 'Yar tusa wacce ba ta san arziki ba! Ki na baiwa d’iyar bayi har kya wa mutane kwawarniya shiga rumbun k’ore, yo to sai ki ma Babban Bijimi musu da kwarnato in ya so a tsire ki ma ga me asara!’’
Bakin Bintu na rawa, ta saki hannun Habibu, wanda d’acin maganar Jadiya ya sa shi juyawa da sauri dan gudun kar ya maida mata ya jawowa Bintu da ma gidan su baki d’aya, ya na jiyo Jakadiya na masife Bintu yayinda ta ke hankad’a kafad’ar ta zuwa ciki, babu yanda zai yi haka ya tafi ba tare da ya sake ko waiwaye ba.
'Dakin Jakadiya aka aje Bintu, nan ta sha kukan ta, ta k’oshi dan kan ta ta yi shiru sai ajiyar zuci kawai.
Jakadiya ta shigo kana ta ce ta saka mayafi ki biyo ta, Babban bijimi na jiran zuwan su. Kallabin ta ta ware ta yafa bisa kan ta, babu musu dan kuwa taji tsoran maganar Jakadiya na za a tsire ta, ta bi bayan Jakadiya ba su zame koina ba sai turakar sarki.
In da Jakadiya ta tsaya daga waje, Bintu ta shiga daga ciki. Nan ta tadda sauran ilayan Sarki. Gimbiya Binta ba ta fasa watsawa Bintu kallan wuk’anci ba, ita kuwa Inna Salti tsabar tausayin Bintu ne cikin ran ta. Yarima Nuhu kuwa Allah kad'ai ya san tashin hankalin da ya shiga, musammam yanzu da ya ga Bintu gaban Sarki, babu makawa ya na ji yana gani Bintu za ta si6ice ma sa. Tin shigowar ta ya sa saka idanu akan ta, k’irik’iri be damu da ba shi kad’ai ne ba, bare ya damu da fassarar da za a iya masa. Ita kan ta Gimbiya Binta ta lura da irin kallan da ya kewa Bintu, har zunguran K'amariyya ta yi dan ita ma ta ganewa idon ta, bare kuma su Hajja Kilishi har da murmushin mugunta, dan kuwa ta k’i jinin Yarima Nuhu.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣9⃣
Muryar Bintu a shak’e tsabar kukan da ta yi ta kai gaisuwar ta ga Sarki. Hankali kwance, idan Sarki ya lura da sauyin yanayin da aka samu game da Bintu tsakanin ranar da ta fara zuwa gareshi da kuma zuwanta a yau, bai nuna ba don kuwa ko a jikinsa ya amsa, kafin ya k’ara da
‘’Masarautar mu na godiya ga wanga d’iya ta arziki, kasancewarki baiwa, mun baki ‘yanci, mun ‘yanta ki a yau kin tashi daga baiwa kin zama d’iya mai ‘yanci...’’
A firgice Gimbiya Binta ta kai kallonta ga Sarki ta na mai fiddo ido waje dan kuwa ba ta yi zato ba, kar dai danasani za ta yi, abun da ya fara zuwa zuciyarta kenan yayinda gaban ta ke dukan uku uku. Haka ma kowa na wajan ke kallan Bintu, wacce ta rasa me za ta yi, murna za ta yi na samin ‘yancin rayuwar ta bayan shekara goma sha biyar ta na baiwa, ko kuwa kuka za ta yi ta tashi daga baiwa, amma iyayenta na nan a bayi, tabbas ta tabbata d’iyar bayi. Hawaye ne d’aya bayan d’aya ke gangarowa daga idanun ta, murya na kakkarwa ta ke fad’in ‘’Godiya na ke ranka shi dad’e, godiya na ke Allah shi ja da ran Sarki, Alkhairin Allah ya tabbata a gare Mai Martaba’’
Yarima Nadir da ke jikin Inna Salti ne ya ce " Inna Salti me ya sa Bintu ta ke kuka?"
Hannun Inna Salti bisa le6enta ta amsa da
"Shhhh"
Wato ya yi shiru, shirun ko yayi.Yarima Nuhu wanda shi kansa ya rasa shin wai me ya ke ji a lokacin ji yayi kamar ya isa ga Bintu ya sa hannu ya share mata hawayen idanunta, ji ya ke kamar ya rok’i Sarki a bar ma sa Bintu, ko da kuwa shi ne abu na k’arshe da zai tambaya gun Sarki ya amsa masa. Yau ga Bintun arziki an zama ‘yantacciya, wannan fa shi ake kira ga k’oshi fa ga kuma kwanan yunwa.
Sarki bai gushe ba ya k’ara da ‘’Nan da mako hud'u za mu amra miki aure ga Masarautar Fabarusa, da an amra za a ba mu bashin da mu ka buk'ata, hallo tarewar ki can sai nan da mako hud'u kan nan kin sami shiri mai kyau. Ba mu amince ba sai da mu ka tabbatar de ke baiwa ce mai tarbiya, dattako da kuma sirri,kasancewar kin iya zama da d’iyar mu lamun lahiya ba tare da ta ta6a kawo mana kukan ki gare mu ba’’
Gimbiya Binta aka zagayar da kwayan ido ta cikin mayafi, cikin ranta fad’i ta ke ‘’Yo to ba girin girin ba d'iyar bayi, ta mai......’’
Jin Sarki ya ce ‘’Hajja Kilishi ga wanga d’iya za ta dawo gare ki ina fatan ke da Jakadiya za ku sa ta hanya, cikin surri ku koyar da ita dabarun Masarauta duk dai yanda Jakadiya ta sheda mana yarinyar dama mai sani ce, mu na so duk kan nan ku sani ba mu yarda ko da wasa wani ya k’ara kiran wannan d’iyar arziki da baiwa ba, haka kuma ban amince a yi mata yanda ake yiwa bayi ba, ku sani wanga d’iya d’iyar mu ce, dan haka a daraja ta’’
Gimbiya ta cije le6e, ita dai kam wannan lamari ba ya mata dad’i, ya Takawa ya ke san mata sakiyar da ba ruwa ne, ko da yake ma ita ina ruwan ta k’arshen ta ajali ne ke kiran Bintu, dan kuwa girman Masarautar Fabarusa ko jinin saraki sai sun shirya zaman ta bare baiwar da za ta je a matsayin Gimbiya, tun da dai ta ci nasarar sa min Aisar, ga shi Gimbiya K’amariyya ta sami Barde ai hutatai. Abunda ta ke jaddadawa zuciyar ta da ta ke nemen fashewa tsabagen bakin cikin kalaman Sarki kenan, bilhakki danasani ta fara, dan kuwa ba ta yi zato ba.
‘’Za mu mayar da d’iyarmu Binta kasar Nigeria, in da za ta je can ta cigaba da karatu kan mu biya bashi ga Masarautar Fabarusa komai ya warware........’’
Gimbiya Binta ba ta san sanda ta tashi tsaye a zabure ba, ta na mai girgiza kai. Nan kallo ya koma gare ta har sai da Yarima Inuwa ya daka mata tsawa ya na mai fad’in
‘’Gide kin manta gaban wa ki ke ne! ko ma ki zauna kar ki mana sakarci a nan’’
Gimbiya K’amariyya ce ta jawo hannunta, yayinda ta koma ta zauna a gajiye, tuni idanunta su ka kawo ruwa, ba ta san sanda ta furta.
‘’Tuba na ke Takawa, Allah ya ja da ran Sarki a min rangwame tuba na ke kar a bari na yi nisa da Mai Martaba’’
‘’Ko kuwa dai ba kya so kiya nisa da Aisar Gaddafi Nur ba’’ Fad’in Gimbiya K’amariyya kenan wacce ke rike da hannun kanwarta ta, cike da tausayi ta ke dubanta, dan kuwa ita kad’ai ta san zafin da ta ji jin za a raba ta da masoyinta Barde, yau kuma gashi ‘yar uwarta na shirin rasa na ta masoyinta sakamakon taimakonta da ta yi. Kana ta kada baki ta ce
"Allah shi ja da ran Sarki, dan Allah a duba lamarin nan, Binta har yanzu yarinya ce, za ta cutu muddin ta yi nisa da mu.’’
Yarima Nuhu na dubansu, bakinshi kunshe da murmushin mugunta ya ce
'’Kar ki fad’awa Takawa wanga yashashen zance haka K’amariyya, idan har wanga d’iya( ya nuna Bintu da yatsa) za ta iya taran aradu da ka ta shiga Masarauta mai girma a cikin badda kama, duk da k’aranci shekarunta, ban ga dalilin da zai sa Binta ba za ta iya zuwa wata k’asar ba domin rufawa masarautar ta asiri ba, yo to menene nan da makwafta Nigeria, ai Nigeria da Nijar d’aita, ko kuwa ki na nufin za a aurar da Bintu matsayin Binta ne kuma jama’a na ganin Binta a k’asar nan, dole sai ta tafi’’
Ya k’arasa magana ya na mai duban Gimbiya Binta da ta ke kuka bilhakki.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
2⃣0⃣
‘’Nuhu ya yi gaskiya, kamar yanda wanga d’iyar arziki ta mana biyayya, mu na fatan ke ma haka za ki kasance me biyayya a gare mu, saboda haka sai ki zauna da shirin ki na bulaguro nan da mako hud'u, komai za a yi jiyo shi cikin surru, kar ku yarda da kowa sai amintaccun bayin ku. Mun yi magana, Mun sallame ku’’
Cewar Sarki kenan ya na mai kawar da kai daga kallan Gimbiya Binta gudun kar ta karya masa zuciya, dan kuwa shi dai yaransa su an rauninsa.
Komawarsu d’aki nan Gimbiya K'amariyya ta ga kuka da daru gun Gimbiya Binta, ba shiri Inna Salti da Hajja Kilishi su ka sallami bayin da ke cikin 6angaran gudun yad’uwar maganar. Wanda kuma su ka riga su ka ga halin da Gimbiya Binta ke ciki, Jakadiya ce ta tara su, cikin hikima ta mu su kashedin ko da wasa kar su yarda a ji halin da Gimbiya Binta ta shiga jin Mai martaba ya ba da amran ta ga Sarkin Fabarusa, duk wanda aka ji a bakin sa sai dai uwar sa ta haifi wani. Ai kuwa dai ba su fasa yad’awa ba, ta yanda Allah ya so ma maganar Jakadiya su ke yad’awa ba asalin zancen gaskiya ba.
Dakyar aka samu Gimbiya Binta ta sarara da kukan da ta ke, ita sam ta manta da azanci a maimakon ita za a aurar da Bintu, kasancewar haka ita ma sai an 6oyeta na wani d’an lokaci. Gashi Mai martaba ya ‘yan ta Bintu, wacce ta ke baiwar ta tin tale tale. Bauhaushe dai yayi gaskiya, in za ka gida ramin