Showing 18001 words to 21000 words out of 44561 words

Chapter 7 - Bintu Diyar Bayi Ce 1 Complete Hausa Novel

06 Jan 2025

151

Bintu ya na mai fad’in ‘’ba Gimbiyar ki na ke magana akai ba, Gimbiyar Aisar na ke nufi, wata motar za ki shiga?’’

Cike da mamaki Bintu ta amsa masa da ‘’iyye? Na’am? Ni Bintu?’’ kai ya girgiza mata, jiki a sanyaye ta masa nuni dai ga motar da Gimbiya ke ciki, kana ya ce da direba(driver) ya ce ‘’Aboki na bud’e min bayan motar na aje kayan ko’’ jin haka Bintu ta yi saurin fad’in ‘’waccar motar ta baya za a aje kayan’’

Aisar ya ce ‘’toh gidan gaba ko baya ina ki ke zama?’’ ta na hango Gimbiya ta na girgiza kai har da kwafa, ta na mai duban Bintu ta ce ‘’a juri kai zuga gabas, wataran ta zo da ruwa’’ maimakon Bintu ta bashi amsar sai kawai ta kai hannun ta ga murfin motar da niyar bud’ewa, yayi saurin tsaiyar da ita, ya b’ud’e da kan sa, Bintu ta shiga, ita kan ta ta san ta wuce gona da iri. Ledar ya aje bisa cinyar ta, ba tare da ya rufe motar ba ya ce da direban ya fito kai akwaitin Bintu cikin motar da ake ajewa. Direban ya so yi masa musu, amma ko da suka had’a ido da Aisar ya ga waye gaban shi tini ya fito yayi yanda aka saka shi.

Aisar ya ce ‘’ki gaida gida ki gaida yan gidan Bintu, sai kin ji daga gare ni’’ kai kawai Bintu ta iya gyad’a masa, yayin da ya mayar da murfin mota ya rufe. Direba ya dawo ya tada mota har su ka fita be dena kallan motar da Bintu ke ciki ba, ji ya ke kamar ya bi bayan su.

Da fitar su, ta baya ta ji Gimbiya ta kifa mata mari, ta na mai fad’in ‘’shegiyar kaya!dama wajan shi ki ke san zuwa sai da jiki na ya ban!’’ kuka Bintu ta saka, fad’i ta ke ‘’ki yi min rai Gimbiya, tuba na ke, ba wajen shi na je ba a hanya mu ka had’u, idan karya na kai arratta kashe ni’’
Tas! Ta dad’a kwashe ta da mari ‘’shi ne har da d’aukar d’an akurkin ki ko? Kai direba tsayar motan nan! Direba ya ja ya tsaya, sauran motocin ma tuni suka faka gefe guda ganin na Gimbiya ma ya faka. Ledar hannu Bintu ta fizge ta na bud’e, mayafai ne manya masu kyan gaske har guda goma. Tsaki Gimbiya Binta ta ja yayinda ta sauke gilashin motar ta na ji ta na gani ta wulga mayafan waje, kan idanun Bintu haka su ka sauka cikin ruwan sama da ya kwanta a gefen titi, sannan ta ce ‘’Direba mayar da d’iyar bayin nan cikin bayi sa’annin iyayen ta’’ Direba ya dubi Bintu da ke faman kuka ya ce ‘’yo to ai sai ki hito ko?’’
Bintu na k’ok’arin fitowa ta ji Gimbiya ta ce ‘’ke da wanga ecole har abada! aradu ma kuwa!’’ da ma dai ko ba ta fad’a ba Bintu ta san ta faru ta k’are ramamme ya zagi maye. Haka ta na mai fad’in ‘’ina tuba’’ amma Gimbiya ta mata kunne uwar shegu, yayinda direba ya raka Bintu izuwa motar bayi a wulak’ance. Nan su ka d’auki hanyar masarauta Bintu na mai bakin ciki da fad’uwar gaba.

🐫🐪🐫🐪🐫🐪🐫
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
Cool novel, makeup and kitchen1⃣
AND
Cool novel, makeup and kitchen2⃣)

WHATSAPP NO:
+2347039625239
®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



©Khadija Sidi.....✍🏼

1⃣1⃣


Bayan Bintu ta ci abinci, ta watsa ruwa, Inna ta shiga ta same ta kwance ta na hutawa. Ganin Inna ya sa ta tashi zaune, Inna na murmushi ta ce "Gide na aza kwana ki ke(na zaci bacci ki ke)’’

Kai Bintu ta girgiza mata, cike da farin cikin yau ga ta da Innarta, ta ce ‘’A falke na ke Inna (ido na biyu Inna)’’ Nan ta zauna kusa da ita in da ta fara mata tambayoyi game da makaranta kamar dai yanda ta saba. Jin Bintu ta ce komai lahiya lau, bai hana Inna fad’in ‘’Ki dai k’ara hakuri da takwarar ta ki, na ce dai lafiya lau ku ke zaune ko?’’
Da har Bintu za ta fad’a mata halin da ake ciki, sai ta fasa don kuwa ta san halin Inna da sa abu a rai, sai cewa ta yi ‘’Lahiya lumi.”

"Ngla zauro, Ala barraaz3( da kyau Allah ya yi albarka)" Fadin Inna ta na mai dafa kan Bintu. Bintu ba ta gushe ba ta yiwa Inna tambayar da ya tsaya cikin ranta, ta ce
‘’Inna me ke faruwa ne?’’ Kai Inna ta girgiza sannan ta ce ‘’Wannan annobar ta duk shekara ita ta sake bayyana Bintu.’’

Gaban Bintu ya fad’i ta na mai dafe k'irji ta ce ‘’Fari?’’(Annobar yunwa, sanadiyar k'arancin ruwan sama)

‘’Aradu ma kuwa, wanga ma ai tafi ta kowacce shekara, talakawa mu na cikin wani hali, dussa ma da za a bawwa awaki gagaran mu yake, hatsin da ki ka ga ina tankad’ewa na gidan sarki ne, Allah ya sa ya shigo ta hannuna, na sami dussar ko ba komai ma sami na karin kumallo, na dare kuma ma ci ragowar babban gida.’’ Cewar Inna.

‘’Innalillahi wainna ilaihi rajiun’’ Fad'in Bintu kenan yayinda zufa ya shiga keto mata. Inna na mai girgiza kai ta ce ‘’Abunda mu ke ta fad’a kenan ‘yar nan’’
kana Bintu ta ce ‘’Yo to Inna me zai hana mu nemi taimako wajan sauran masarautar? Ai na ga ba laifi k’asar mu dai akwai abinci ga taimakon juna’’

Inna ta ce ‘’Uhum ina ne ba a nema ba? Su ma ai sun gaji, yau da gobe ya wuce gaban wasa ai, ridda karya kuka tatsa’’ Zuciyar Bintu d’aya ta furta ‘’Fabarusa fa.....’’

Da sauri Inna ta doke bakinta, hannun Bintu bisa bakinta, Inna na mai zare ido ta ce ‘’Kul ashirni zanne(rufa min asiri), shiga uku takabar sarakuwa!(sirika) Kar ki sake ambatan yankin ga dan Allah, kin manta bakar gabar da ke tsakanin mu, ahir ba da ni ba saka lallen kaza!’’

Ajiyar zuci Bintu ta saki tare da fad'in "Yo to Inna ai dalili ne ke sa a kama kaluluwar sarakuwa...(Dalili ke sa a kama kaluluwar sirika)"

Inna na girgiza kai ta ce "Na ce ki bar maganar ga Bintu, ba na kwawarniya shiga rumbum k'ore."

Ta na mai jinjina kai ta bar maganar, fatanta Allah ya kawo musu d'auki, Inna ta amsa mata da amin. Ranar har Bintu ta kwanta ba ta ga dawowar mahaifinta ba, dama dai idan ana cikin fari har kwana ya kan yi can fada.

***** ******
Washegari da sassafe, Bintu na bacci wata baiwa daga babban gida ta yiwa Inna sallama. Inna da ta yi zatan kiran na ta ne ta ce ‘’Allah sarki, hallau kun ji ni shiru ko?’’

Jin haka baiwa ta ce ‘’Gide kiran ga ba na ki ba Uwar bayi, wannan kira na Bintu ne daga Gimbiya Binta’’

Kafin Inna ta bata amsa, mahaifin Bintu ya fito a fusace, in da ya hau Inna da fad’a ‘’Yanzu ki na nuhin(nufin) wanga d’iya ta na nan ta na kwana(bacci) har k’arfe bakwai na safe ba ki tashe ta ba tsabagen lalacewa! Yagana anya kuwa?’’

Cikin sanyin murya Inna ta furta ‘’Ayi hakuri na ga jiya ta dawo shi ya sa...’’

‘’Yo to da hakurin ya mutu nawa ki ka biya kud’in sadaka?’’ Jin haka Inna ta ja bakinta ta yi shiru, ba ta ankara ba sai ganin Baba ta yi ya shige d’akin, haka kuma be fasa fad’an da ya ke ba, har ya iske Bintu ta yi d’ai-d’ai ta na baccin ta cikin kwanciyar hankali. Be yi la’akari da rabon da ya sa ta a ido watanni uku kenan ba, ya rufe ta da fad’a da zagi. Ita kuwa Bintu kamar a mafarki ta ke jin muryarsa, a hankali ta bud’e ido, ko da su ka had’a ido cikin magagin bacci ta furta ‘’Baba?’’

A fusace ya yi mata dak’uwa ‘’Baban ubanki! Hegiya kin saki la66a da su k'a66a ki na ta kwanan asara! Tashi maza ki wanke ido ki tahi babban gida!"

Nan da nan Bintu ta wartsake, ta na mai raribar hijabinta, ta ce ‘’Yi hakuri Baba, jiya na dawo ban ganka ba.....’
‘’Yo to ai gashi kin ganni, yar tselan uwa mai kama da kuliya’’

Ko a jikin Bintu haka ta fito Baba na biye da ita, dan kuwa idan da sabo ta saba, dan ba dan Baba shi ya haifeta ba da sai ta ce ya ma tsane ta ne gaba d’aya. Har yanzu mita Baba ya ke, ita dai Inna d’auke kan ta ta yi, ta shiga wasu sabgogin gaban ta. Baba ne ya ce da baiwa mai jiran Bintu ta je ta ce ga Bintun nan ta tafe. Ta na fad’in ‘’Madallah’’ ta kama hanyar ta tafi.

Buta Bintu ta d’auka ta kewaya bayi, da ta fito ta sa dakakken gawayi da gishiri ta wanke hakoran ta, sannan ta wanke fuska. Baba da ke tsaye gefe ya na jira ya ce ‘’Maza kama hanya ki yi gaba’’

‘’Malam na ce a bari ta yi karin kumallo ko?’’ Fad’in Inna cike da nuna damuwa’
‘’Kayya! Wani kari kuma Gimbiya ta yi kira? Ke rabu da ita, idan kin dawo kya yi karin, wuce ki tafi’’ Cyewar Baba.
Silifa ruwan d’orawa ta sanya a k’afar ta, har za ta fita Inna ta ce ta tsaya su tafi tare. Amma Baba ya ce babu wannan maganar, karshen ta ma ya yanke hukuncin raka Bintu da kan sa. Haka ya sa ta ta gaba, ya na biye da ita, duk wanda su ka gani a hanya sai ta tsaya sun gaisa da Baba, a haka har ya kai ta ga filin sukuwa, sanna ya juya ya koma gida.

Tafiyar Baba ke da wuya Bintu ta hangi Yerima Nuhu tare da tawagar sa bisa doki, ganin su ya sa Bintu d'aga k’afa ta na mai adduar Allah Ya sa kar su cimma ta, amma ina Allah bai amsa addu'arta ba, domin kuwa ganinta ya sa Yerima dukan bayan dokinsa da dorinar hannun sa a hankali, hakan ya sa dokin k’ara sauri haka tawagar ta shi wanda ya kunshi abokan sa guda hud’u, nan da nan sai ga su gaban Bintu su na mai tada k’ura yayinda su ke jan linzamin dawakan dan su sami su tsaya.

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



ZUWA GA K'AWATA HYK, SAKON KI NA ARZIKI YA ISO GARE NI, NA KUMA CE AMEN HAR DA KE. NA GODE KWARAI, MADALLAH DA KE, SIDIYA CE KE MIKI FATAN ALKHAIRI🤝




©Khadija Sidi.....✍🏼

1⃣0⃣



*WAIWAYE ADON TAFIYA*

Wanene Sarki Sule Inuwa Magaji?

Shi ne Sarki na ishirin bisa gadan mulkin Sa’ayrasa. Ya hau kujerar mulki a shekara ta (1984), bayan Sarki Inuwa Magaji mai rasuwa, lokacin ya na da shekara arba’in a duniya. Allah ya azurta shi da ‘ya’ya goma sha takwas, ya birne takwas saura goma a raye, maza takwas, mata biyu.

Mata hud’u ya aura, uwargidansa marigayiya Hajja Fatima Abdu, wacce ta rasu bayan shekara d’aya da hawar sa mulki, wajan haihuwar Gimbiya Binta. Haka kuma ita ta haifawa sarki yara takwas, kasancewar auren saurayi da budurwa su ka yi da Mai martaba, ‘ya’yan ta su an manya duk da dai yawanci ba su yi tsahon rai ba dan sai da ta birne hud’u kafin ta samu masu zama guda hud’u. Yerima Inuwa mai shekara talatin, yayi aure har da yara uku, Yerima Nuhu shekara ishirin da biyar, Gimbiya K'amariyya mai shekara ishirin da haihuwa sai kuma Gimbiya Binta .

Sai kuma matar shi ta biyu Hajja Salame wacce ake kira Hajja Kilishi, ita Allah be nufe ta da haihuwa ba. Sai ta uku Hajja Maimunatu ana kiran ta Uwar fada, yaran ta biyu, Hassan da Hussain wanda su ke sa'annin Gimbiya K’amariyya sa kuma amaryar wacce ta ke kanwa ce gun Hajja Fatima Abdu, aka d’aura masa bayan rasuwar sa mai suna Masarriya, ana kiran ta da Inna Salti(wacce za ta haihu da yawa), yaran ta hud’u, duka maza. Sun had'a da Yerima Hamza wanda shi ne babba mai shekara goma sha uku, sai mai bin sa Yerima Abdallah dan shekara goma, na ukun Yerima Ahmadu, shekara takwas sai autan ta Yerima Nadir mai shekara biyar a duniya.

Kasancewar ‘ya’yan sa mata biyu kacal a duniya da kuma soyayyar da ya ke yiwa uwar su, ya d’auki san duniya ya d’aura ma su, musammam K’amariyya wacce kamar ta d’aya da mahaifiyar ta kamar kabo da kabo. Hakan shi ya zame babban rauni ga Sarki Sule.

***** ******
Sai da su ka shige tsaunika da duwatsu, suna mai ketare yankuna da dama ta sahara, kafin su hau mik'ak'k'iyar hanyar da za ta sada su da Sa’ayrsa. Ta babbar kofar wanda ake yiwa lak’ani da kofar Magaji Babba su ka shiga yanki. Rana ne sosai kwallewa a yankin daga gani ka san ruwa be sauka baw, kamar ma ruwan sama be sauka a yankin ba bana. Jama’ar gari kowa sabgar gaban sa ya ke, daga masu zuwa ko dawowa daga kasuwa, sai masu zuwa gona, mata wasu da goyo wasu da yara a hannu su na ta hidimar su, ya yara su ma ba a bar su a baya ba, su ma da na su sabgar irin ta yara.

Babban abun da Bintu ta lura da shi, shine rashin annushuwa da kuzari na jama’ar yankin, ba kamar yanda ta saba ganin jama’ar yankin cikin farin ciki da annashuwa ba.

‘’Shin ko dai akwai wani abu da ke faruwa wanda ba mu da masaniya akai?’’ Tambayar da ta ke yiwa kan ta kenan, amma gudun magana ya sa ta kasa kada baki ta tambayi sauran bayi ‘yan uwan ta, har su ka kai ga kofar fada.

Ta k’ofar gabas su ka shiga fada, wanda dama in dai iyalan sarki ne ta nan su ke shiga.

Nan da nan jama’ar fada su ka fito tarban Gimbiya, ciki har da k’annan Gimbiyar wato Yerima Hassan da Yerima Husaini, Yerima Abdallah da kuma Yerima Hamza. Murna da farin ciki gun su kuwa ba a cewa komai.

Ana cikin wannan yanayin ne Bintu ta fito ta, bayan ta d’au d’an akwatin k'arfen ta, ta ja gefe babu wanda ya lura da ita bare a damu da halin damuwa da ta ke ciki. Ganin Gimbiya ta fito, da sauri ta k’arasa cikin bayi yan uwan ta, in da su ka zube domin kai gaisuwa ga su Yerima, sannan bayi su ka taka mu su baya su ka shege izuwa fada.

Bintu na durk’ushe ba ta tashi ba ta ji an tab’a kafad’ar ta, a hankali ta d’aga ido, tuni murmushi ya maye fuskar ta yayin da ta tashi tsaye ta na mai rungume yayan ta Habibu. Cikin farin ciki ya ce ‘’Kauna(kanwa) mu na ta ke kewan ki, tin ba ma Inna ba, yo kawo akwaitin na ki mu tahi ko?’’

Saboda murna Bintu kasa magana ta yi, sai kawai mik’a masa akwaitin ta yi. Akwaitin ya d’auka, ya na ruke da hannun ta su ka wuce sashin su na bayi. A hanya ya ke tambayar ya yaga idanun ta sun yi jajur haka? Ta ce da shi idanun na ta ke ciwo shi ya sa. Ya ce da ita ta dai sha magani dai ko? Ya kara da Allah ya sauwake.

'Bangaran su na bayi b’angare ne mai d’auke da sashi-sashi na gidajen bayi. Gidan su Bintu wanda ya ke na uku cikin jerin gidajen bayi, gida ne ginin k’asa, mai d’auke da d’akuna uku da falo, sai kuma d’akin dafa abinci da kuma 6and'aki guda d’aya.

"Dakunan biyu a cikin falo su ke, na ukun kuma tsakar gida ya ke kusa da dak’in girki, in da 6and'aki ke daga can gefe daf da soro. Ba wani girma ne da tsakar gidan ba haka zalika d'akunan, idan ana zafi da kyar su ke iya bacci, musammam yanayi irin wanda su ke ciki a yanzu, ruwa be sauka a yankin ba. Falon na su kuma babu komai ciki daga daga ciminti sai tabarma.

A tsakar gida su ka tadda Inna ta na tankad’en hatsi, kasancewar ta bababbariya baka ce wulik, doguwa ta na da dogon hanci, fuskar ta d'auke da zane da fashin goshi irin na al’adar barebari. Duk da Bintu ba ta kama da ita, akan ce tsayi da garin jikin Bintu na Inna ne, haka ma gashin kan ta wanda idan ta ware ya na saukar mata har gadon baya.

Da gudun ta Bintu ta je ta rungume ta, Habibu na mai fad’in ‘’Gide ga autar ta ki na kawo mi ki Inna’’

Cike da farin ciki ita ma ta rungume d'iyar ta ta, fad’i ta ke "Usoo am morantiye, wushe k3shero, is3maa?? Nda zawol?"(sannu yan boko, sannu da zuwa, an dawo? Ya hanya?)

‘’Lahiya limi Alhamdulillah, mun same ku k’alau?’’ Cewar Bintu. Inna na mai duban ta cikin nazari ta amsa da ‘’lahiya limi, Gide ya na gan ki da idanu haka jajur?’’

Bintu na fara'a dan gudun kar Inna ta gane halin da ta ke ciki, ta ce idanun ta ke ciwo. Ita ma sai a sannan ta lura da yanda Inna ta rema ta lalace, d’aga idan da za ta yi ta kalli Habibu sai ta ga ashe gwara Inna ma akan shi. Cike da alamar tambaya ta dawo da kallan ta ga Inna, kana ta ce "lafiya kuwa Inna? Ya na gan ku a rame haka? Ina Baba?’’

"Ya na fada.’’ Amsar da Inna ta bata kenan a takaice. Kana Bintu ta ce ‘’Yo to lafiya na ganku haka?’’

Inna ce ta amsa mata da "Yanzu dai ba lokacin tambaya ba ne, Habibu maza k’arasa mata da kayan d’aka, sai ke kuma ki watsa ruwa ki ci abinci ma yi maganar ko?’’

Cike da fargaba Bintu ta gyad’a mata kai kafin ta shige d’akin ta wanda ya ke d’aya daga cikin na falon, Habibu biye da ita.

Shigar su ta bi d’akin na ta da kallo, d'an karamin d’aki ne mai d’auke da gado na k’arfe mai (spring)na daidai kwanciyar mutum d’aya, sai kuma wani k’atan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login