Showing 39001 words to 42000 words out of 44561 words
halartar d’aurin auren ba, in zan sami dama ina so na zama d’aya daga cikin wanda za su wakilce ka’’
Jin haka Junaidu ya san hakan nan yanda Aisar ba ya san duk wani abu da zai had’a shi da siyasa, ya san banza ba ta kai zomo kasuwa, ya ce
‘’ah ah ka manta ranar za ku koma Ingila domin duba jikin Baba? Ka bari an hutasshe ka ni na je’’
Duk da yayi maganar ne cike da zolaya, sai da Aisar ya tsuke fuska, dan kuwa gani ya ke yanda ya ci burin ganin Bintu, duk wanda zai hana shi ganin Bintu shi an mak’iyin shi, jin za a je Masarautar su ya san tun da d’iyar bayi ce ko shakka babu zai gan ta, ko dan ya sami daman ganin iyayen ta, ya ji ya za su yi da karatun Bintu tun da dai ita Gimbiya Binta aure za a mata, kuma ya rok’e su da kada su cire ta daga makaranta, idan ya kama ne ya d’au nauyin ta, zai yi.
Ya na mai tsuke fuska ya ce
‘’zai fi kyau dai kai ka koma Ingila, tun da Baba ya ji sauki, duba shi kawai za a yi ina ga babu amfanin zuwa da ni’’
Shugaba Gaddafi ya ce
‘’to tsakanin ku, idan dukan ku biyun ne ma za su d’aurin auren daidai ne, ina jin sauki sosai, ba na buk’atar rakiyar ku’’
Murmushin jin dad’i Aisar ya saka, cikin ran sa ya na mai fad’in
‘’Bintu na ina nan tafe, ki kwantar da hankalin ki babu mai cire ki daga karatun ki’’
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[5/15, 7:22 PM] +234 703 962 5239: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
🕊Special shoutout to all the Atikus🙋🏽🙋🏽 onelove💞😘😘
©Khadija Sidi.....✍🏼
2⃣4⃣
Kallon Bintu Yarima Nuhu ya ke cike da so da k’auna, murya can k’asa ya kira sunan ta
‘’Bintun arzki, dama haka ki ke da kyau? Anya kuwa Bintu zan juri rashin ki?’’
Kanta a k’asa ta d’an ja da baya, dan kuwa ganin Yarima Nuhu durkushe gabanta ba k’aramin takura ta yi ba, dad’in dad’awa yau kuma ya zo mata da saban salo na magana. Ai kuwa sai ta yi kamar ba ta ji ba. Kana ta ce
‘’Allah shi taimaki Yarima, Barka da yammaci, Jakadiya ce ta ce Yarima na da buk’atar gani na’’
Hannunta da ke rawa ya bi da kallo, in da idanunsa suka sauka bisa zoben hannunta, sai kyalli da shek’i ya ke, ba tare da wani tunani ba ya d'aura hannunsa bisa hannun lta mai d’auke da zoben. Jin sabon salo hannun Yarima Nuhu bisa na ta ya sa Bintu janye hannunta a firgice cikin sauri kamar wacce aka d'aurawa garwashi, nan ta shiga yarce hannun tana ka6ewa kamar wanda wani abu ya mak’ale. Gaba d’aya ta firgice idanunta na shirin kawo ruwa.
Cike da mamaki Yarima Nuhu ya ke dubanta, kana ya ce
‘’Haka ki ke k’yank’yamina Bintu? Duk wannan d’aga hankalin da yarfe hannun dan na ta6a ki ne?’’
Sai a sannan ta farga da abun da ta ke, tuni ta zube hannayen nata a k'asa, idanunta na fidda kwallar da dama su ke mak’ale cikin kwayar idanunta, fad’i ta ke.
‘’Na tuba, kamin rai, na tuba, ba na so na mutu Yarima, aradu ba na san na rasa raina.’’
Ya na mai jinjina maganar cikin ransa, cike da mamaki ya ce da Bintu
‘’Wa ya ce za ki mutu?’’
Zuciyarta d’aya, har ila yau ba ta fasa hawaye ba ta ce
‘’Iya Dije ce’’
‘’Iya Dije?’’
Yarima Nuhu ya maimaita. Bintu na mai gyad’a kai ta ce
‘’Eh Iya Dije, ta ce idan har na sake na bari namiji ya ta6a ni mutuwa zan yi, kwankwatsi ma kuwa.’’
Ga mamakinta sai gani ta yi Yarima Nuhu ya jefa kansa baya ya na mai saka dariya mai sauti. Cikin rashin fahimta Bintu ta duk’ar da kai jiki na rawa.
Tashi ya yi, ya koma wajan zamansa na fari, yayinda ya zauna ya na mai kishingid’a bisa tintin cike da mulki da sarauta. Har a lokacin idanunsa kanta ya ke, fuskarsa kunshe da murmushi bayan wasu d’an dakik’ai ya ce
‘’Bintu d’ago ki kalle ni.'’
A hankali ta d’ago kanta, cikin bin umarni ta kai kallonta gareshi, fuskarta cike da hawaye. Gefansa ya mata nuni da shi sannan ya ce
‘’Dawo nan ki zauna.’’
Ta na fidda kwayen idanu ta ce
‘’Iye?’’
Kai ya gyad’a mata cikin jaddadawa, bai kuma fasa mata murmushi wanda ke k'ara masa kyau ba. Cike da shakku Bintu ta tashi a hankali, inda ya mata nuni nan ta je ta zauna, amma can nesa da shi.
Ya na mai jin dad’in maganar Bintu, duk da yayi mamaki ace baiwa kamar Bintu batasan komai ba har haka, sakamakon shaidar rashin kamun kai da ake yiwa matasan bayi irinta. Kana ya nisa tare da fad’in
‘’Iya Dije ki ka ce kowa? Ko shakka babu ta yi gaskiya’’
A tsorace Bintu ta d’ago ta kalleshi ta na mai fad’in
‘’Shikenan ni Bintu mutuwa zan yi, na shiga uku na lalace.’’
Dakyar Yarima ya iya kunshe dariyar da ta kusa cin k’arfinsa, ya na mai k'ok’arin d’aure fuska ya ce
‘’Banda yanzu, ba za ki mutu ba tunda ni ba ta6a ki, hallo na yi ba gangan ba, zoben hannunki na ta6a, amma kar ki yarda wani ya ta6a ki muddin ki na so ki yi tsayin rai, musamman idan aka kai ki wannan Masarauta na Fabarusa, ko da kuwa Sarki Abdulrahman ne da kansa.’’
Ta na mai tunani yo dama me zai sa Sarki Abdulrahman ya ta6a ta, ta yi saurin amsawa da
‘’Aeadun Allah ba zan bari ba, hallo ni ma ba na zuwa kusa da maza, Inna ta ta hana’’
Yarima na mai duban zoben hannun ta wanda hakan nan ya ji ya tsole masa ido, ya ce
‘’Wagga zobe na hannunki, wa ya baki?”
Zuciyar Bintu d’aya ta amsa masa da
‘’Monsieur Aisar ne ya bani ajiya.’’
Wani bakin kishi ne ya ta so masa jin sunan namiji bakin Bintu, nan da nan ya sha mur ya na mai kausasa murya ya ce
‘’Akan wani dalili zai baki zobe ajiya? Shi waye d’in ki? Ashe dama ki na soyayya?’’
Cikin k’ok’arin kare kai ta ce
‘’Wallahi ba na soyayya, ban ta6a yi ba, idan k’arya na ke aratta kashe ni, Monsieur ne a École ya ce na ajiye masa.’’
‘’Ciro zoben ki bani’’
Ya ba ta umarni. Har ga Allah ba ta son cire zoben, idanunta na fidda kwalla yayinda ta ciro zoben daga yatsanta, maimakon ta bashi sai ta dunk’ule shi cikin tafin hannunta. Ganin bata da niyar mik’a masa, ya mik’o hannunsa gare ta, a hankali ta d’aga ido ta kalle shi, ya na mai gyad'a mata kai ya mata nuni da hannunshi. Hannunta na rawa, ta aje zoben bisa tafin hannunsa, ba ta ankara ba sai gani ta yi yayi wulgi da shi gefe. Da sauri ta bi inda ya jefa da kallo yayinda ta ji zuciyarta na mata rad’ad’i, sai a sannan tasan ashe zafin da zuciyarta ke mata ba na rabata da iyayen ta kad’ai ba ne, har da na rashin Aisar har abada, gashi idan aka d’auke turarukan da ya bata, zobenshi ne kad’ai ya rage mallakin sa a gunta, ta na ji ta na gani Yarima Nuhu ya raba ta da shi kamar yarda ‘yar uwarsa ta rabata da shi, idan ita dan ta na son Aisar ne, shi kuwa Yarima Nuhu menene na shi azancin? Tambayar da ta yiwa kanta kenan, wanda nan ta ke kuwa ta ji amsarta, Yarima Nuhu na mai duban ta ya kira sunan ta da kakkausar murya
‘’Bintu’’
Hakan yasa Bintu dawowa da kallonta gareshi. Bai gushe ba ya cigaba
‘’Soyayya gaskiya ce, soyayya halal ce muddin ba a tsallake iyakokin Ubangiji ba, ba laifi ba ne don kinyi soyayya, amma ki sani duk duniyar nan da ni ya dace ki yi, Bintu ni mai kaunarki ne, ni Nuhu ni masoyinki ne da ni ya dace ki yi soyayya ba da wani tsoho da ake shirin amra mi ki ba, ko kuwa wancan sokon Monsieur da ya bawa d’alibarsa ajiyar zobe!’’
A tsorace Bintu ta fara ja da baya, ta na mai girgiza masa kai, tsabagen firgici ta kasa magana. Da sauri ya rik’o hannunta, ya na fad’in
‘’Karki guje ni Bintu, ni mai k’aunarki ne, kimin alkawarin za ki aje min kanki amana, ah ah kawai ki shirya mu gudu, duk k’asar da ki ke so aradu zan kai ki Bintu, kar ki yarda a amra mi ki wannan tsohon.’’
Cikin sauri Bintu ta fizge hannunta daga nashi, har lokacin ba ta fasa girgiza kanta ba, yayinda ta ke hawaye d’aya na bin d’aya, tunda ta ke a rayuwarta babu wanda ya ta6a furta kalmar so a gareta, kuma ba ta ta6a zaton zata ji shi daga bakin ko da ‘yantaccan d’an adam ba ne, bare kuma Yarima, Yariman ma na Sa'ayrasa. Hankalin Bintu bai dad’a tashi ba, sai da ta ga kwalla cikin idanun Yarima Nuhu na gangara a hankali bisa kuncinsa, nan ta mik’e tsaye da sauri yayinda kuka ya ci k'arfinta tana mai tattare kasan doguwar rigarta, ta juya da niyyar tafiya, hakan yasa Yarima Nuhu tashi da sauri, ya na mai rik’o kallabinta ya ke fad’in.
‘’Karki tafi ki barni Bintu, aradu zan iya rasa raina, ki tausayamin.’’
Sakar masa kallabin ta yi, gashin kan ta lub lub ya sauko har bisa wuyanta maimakon gadon bayanta da ya saba saukar sakamakon askin da ta sha gun Marry, tana mai tafiya cikin gudu gudu, sauri sauri, ta d’au hanyar fita daga lambun.
Yarima Nuhu rik’e da kallabinta ya shiga doka mata kira
‘’Bintu! Bintu!! Bintu!!!’’
Ina ko waige ba ta yi ba bare ta tsaya har ta fice daga cikin lambu, in da ta bar Yarima Nuhu rungume da kallabin na ta bisa k’irjin sa, ya zube gwiwowi biyu k’asa zuciyarsa na bugawa kamar za ta tsage ta fito.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[5/15, 7:26 PM] +234 703 962 5239: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
DA BAZARKU NI NA KE TAKA RAWA FIKRA WRITERS ✌🏽
Ummuabdoul
Ummu Hannan
Rashida Kardam
Sanah Matazu
Aysha Kura
Batul Maman
Bingel
Farida Abdullahi
Da uwa uba Rufaida Umar, ba zan mance da ke ba. Allah ya bar zumunci.
©Khadija Sidi.....✍🏼
2⃣5⃣
Kai tsaye 6angaran Jakadiya da ya zame mata sabon wajan kwana ta shige, ta tsallake bayi biyu wanda ke ta faman had’e sababbin kayan da aka d’inko mata, ta shige d’akin Jakadiya ta na mai doka k’ofar gudun kar Yarima Nuhu ya biyota. K’uryar d’akin ta shige ta k'udundune ta na mai mayar da numfashi. Ba ta yi minti biyar da shiga ba bayin su ka biyo ta su na mai tambayar lafiya? Ko ta yi gamo ne?
Baki na rawa Bintu ta ba su amsa da ‘’Don mai sama ku rabu da ni, ko shakka babu na kusa rasa raina, na shiga uku ni Bintu na lalace, wayyo Allah Inna ta!’’
Kallon junansu su ka yi, su na mai gyad’a kai cikin jaddada zatonsu na Bintu ta yi gamo, har an fara jifanta daga Masarautar Fabarusa tun kan ta shiga Masarautar, su ka juya jiki a sanyaye su ka fito suna mai rufo mata k’ofa.
Daga waje baiwa ta dubi ‘yar uwarta ta ce
‘’Gide k'ak'a kenan, kinga har an fara yiwa wagga d’iya ture ko? Babu mamaki wani bakin aljanin aka fara mata ture da shi don ta fita hayyacinta ta ce ta fasa amran ga, wagga sharri sai kishiyoyi, maza je ki shedawa Jakadiya tun kafin abu yayi tsamari.’’
Cike da jimamin abun baiwar ta amsa mata da
‘’Wagga batu gaskiya ta, aradu wagga d’iya gamo ta yi, inda kin lura har launin idanunta ya sauya, bara dai na je ga Jakadiya, mutum hege ne, mutum ba imani.’’
Tana mai ta6a kafad’arta, ta ce
‘’Maza Ladiyo, ni bara na tsaya daga rariya ko da wani abun zai faru.'’
Jikin baiwar na rawa ta fara tafiya, tana fad’in
‘’Eh tsaya Kyallu, bara na ruga na dawo, Allah shi fisshemu daga sharrin mahassada.’’
Ta fice, inda ta bar Ladiyo da tsaron k’ofar Bintu. Ita kuwa Bintu ita kad’ai tasan abinda ke damunta, yau ta ji ta kuma ga abinda ba ta ta6a tsammani ba, ko shakka babu tasan rayuwarta ce ta zo k’arshe, ko kuwa dai Yarima Nuhu ya soma shaye-shaye kamar yanda wasu samari daga cikin bayi su ke yi. Abinda ke d'agawa Bintu hankali shi ne sake rike hannunta da Yarima Nuhu ya yi, ita tasan rayuwarta ce ta zo k'arshe.
Jin Bintu ta fara yin gamo tun ba aje ko'ina ba, nan da nan Jakadiya ita ma ta had’o kayan tsubbuce tsubbucenta, haka ma Hajja Kilishi, wacce dama ita aka damk’awa Bintu a hannu. Suna mai jan kunnan bayinnan biyu, Ladiyo da Kyallu, akan kar su sake aji maganar a waje.
A gaba Jakadiya da Hajja Kilishi su ka sa Bintu, tambayar duniyarnan sun mata akan gamon da aka ce ta yi, amma shiru Bintu ta kasa ce musu komai don kuwa muddin ta fad’i gaskiya to kashinta ya bushe. Ganin haka su ka yanke hukuncin fara kare ta tun daga yanzu don babu mamakin sammu da aka fara mata har da na d’aure baki. Bintu na ji ta na gani aka fara mata lalas da siracen magunguna, har da na sha da wanka, kan ka ce me tuni ta fita hayyacinta in banda attishawa babu abinda ta ke yi, ko iya haka aka barta ta san ba k’aramin masifa ganin Yarima Nuhu ya jaza mata ba.
Bayan siracen da ta sha, sai da Jakadiya ta bi duka ga6o6in jikin Bintu ta na d’aura mata laya, wai gudun kar a zo mata cikin dare, nan ko ba su san in ma akwai aljanin ba zai wuce Yarima Nuhu ba, kai Allah shi fisshe mu aikin jahilci.
Saida su ka tabbatar sun gama kafe Bintu kaf, Hajja Kilishi na mai duban Bintu da gaba d’aya ta jigata saboda siracen da ta sha, gashi cikinta har juyawa ya ke tsabagen had’aka na magunguna da Jakadiya ta afka mata duk da sunan makarin sammu da kafiya, Hajja Kilishi ta ce
‘’Ni ko Jakadiya d’iyarnan na shan maganin da’a kuwa(maganin mata)?’’
Jakadiya na mai susa k’eya ta amsa da
‘’Yo to wani maganin da’a za a bawa wagga d’iya za a amran da ita ga tsoho ank’i rami? Ai ni a tunanina tunda dai Sarkin Fabarusa an tsufe ban ji zai damu da abubuwa irin wagga, ko k’ak’a kin ka gani?’’
Hajja Kilishi na mai murmushi ta ce
‘’Tsoho ba mutum ba Jakadiya, yo to maza ma ai ba sa tsufa, kar ki so ki ga yanda Takawa ke ji dani duk farin gemun nan nasa, yauwa tun da magana ta kawo magana, Jakadiya ina mai buk’atar zuwan Takawa gare ni a yau ma, hallo zannuwa da kallabi har guda goma na nan tafe izuwa ga d’akin Jakadiya nan ba da dad’ewa ba’’
Dama dai maganar kenan, ta 6ige da Bintu gudun kar Jakadiya ta ga kamar ta cika naci, don kwana hud’u kenan ita Jakadiya ta ke kai wa Sarki, kasancewar hatta kwanan matan Sarki sai wacce Jakadiya ta za6a tsabagen matsayi irin na Jakadai a fada.
Jakadiya kuwa mai idon cin naira, jin zannuwa na tafe tuni ta kada baki ta ce
‘’Yo to menene, in ma sau goma ki ke san zuwan Babban Bijimi aradu gun ki ya ka kwana, an gama ranki shi dad’e, sai kin ga zuwan mu.''
Hajja Kilishi na mai jindad’in yanda Jakadiya ke damawa da ita, duk da dai ta san na d’an k’ank’anin lokaci ne, in dai Jakadiya ce bakin ganga ta ke, arzikinka shagalinka. Ta mata sallama in da ta barta da Bintu ta mai mata jawabin yanda za ta yi ta kare kanta a Masarautar Fabarusa. Ita dai Bintu jinta kawai ta ke, amma ko yaya ta rufe idanunta fuskar Yarima Nuhu ta ke gani yayinda ya ke furta kalmar so a gareta, haka zalik’a maganganunsa ke mata yawo cikin kwakwalwarta. Ko shakka babu Bintu ta yi gamo, amma fa da Yarima Nuhu, mutuwarta kad'ai ta ke jira kamar yanda Iya Dije ta ce muddin namiji ya ta6a ta.
Zoben Aisar kuwa d’aya daga cikin bayi ne, wanda saurayi ne, mai kula da lambu ya tsinta yayinda ya ke shara. Ganin zobe mai matuk’ar tsada yayi saurin 6oyewa cikin aljihunshi, don jira ya ji ko mai shi zai nema, idan kuma ba a yi cigiya ba ya kai kasuwa ya siyar ya sami kud’i.
********
Kwanaki uku ya rage auren Bintu. Da hantsi Inna Salti ta kawo ziyararta ga Bintu. Daga ita sai Bintu da ke d'urkushe gabanta ne a d'akin. A sannu cikin lallami Inna Salti ke mata magana, in da ta ce
‘’Bintu ki sani wannan lamari jarabawa ce daga Allah, saboda haka ki kasance mai biyayya sai ki ga kin ci jarabawar. Wagga amre za a yi shi ne cikin surri, duk wanda ki ga ya san wani abu na game da gaskiyar wagga amre to amintaccen fada ne, hallo sai sun rantse ake ba su amanar ga, dan haka kema wagga al'amari ya kasance amana a naki 6angaren, idan ki ka kuskura gaskiyar al’amari ya hito, rayuwarki za ta kasance cikin hatsari Bintu, wanda ba na fata. Daga sanda aka amra miki amre za ki tashi daga Bintu, za ki fara amsa Gimbiya Binta.’’
Numfashi ta ja, sa’annan ta cigaba
‘’Kin dai ga yanda sarauta ta ke, a fada aka haife ki ciki ki tashi har rana ita yau da ake shirin amrar da ke. Hallo sai kin yi takatsantsan da rayuwar da za ki shiga, zaki shiga rayuwar amre hallo a fada, akwai wuyar ganewa. A fada ba kowa ne zai 6ud’i hak’ora ya miki dariya ya kasance masoyi gareki ba, wani sa'in ma mak’iyinki ka iya nunawa kin fi kowa soyuwa a gareshi, haka zalika ba kowani mai 6ata miki ba ne mak’iyi a gareki, ta iya yiyuwa kauna ke kawo 6acin ran, don haka ki