Showing 39001 words to 42000 words out of 84091 words

Chapter 14 - Babu So Book 1 Hausa Novel Complete

06 Jan 2025

257

ganin amarya a kicin irin wannan ranar kema kin san bamai yuwuwa bane”.
      Da hausa yay maganar, dan haka ba komai ta fahimta da ƙyau ba. Amma sunan amarya kawai daya shigo ciki ya saka yanayinta ƙara canjawa. Sai dai bata sake cewa komai ba, ta ɗauka tunkuyar daya fiddo mata domin dafa shayin ta ɗauraye, ruwa ta zuba dai-dai shan mutum ɗaya, tana ƙoƙarin rufewa taji tsaiwarsa a bayanta, kafin tayi wani yunƙuri ya janye hanunta da sake buɗe murfin ya buɗe fanfo ya ƙara ruwan.
      “Nadai bazan dafama wata ƙatuwa shayi tana kwance tana barci ba”.
  Karon farko ya saki murmushi, sai dai komai baice ba ya rufe mata tukunyar. Zata sake magana ya dakatar da ita. “Zakimin abinda na saki ko tsiwa? Trouble maker!”.
      “Ga babbar Trouble maker can ka bari a ɗaki”. Tai maganar ƙasa-ƙasa yanda bazaiji ba. Da kansa ya kunna mata gas ɗin, ta ɗaura tukunyar sannan ta ɗiba kayan ƙamshi da lipton da duk ya fiddo da kansa ta zuba. Flask daya fiddo a kwali shima ta ɗauka ta ɗauraye tare da kofi duk yana tsaye yana kallonta. Baiyi mamakin yanda take komai a tsaftace da kuma tsari ba, dan sai dai ya bama wani labarin Mamie badai a bashi ba, yasan kuma hakan duk tarbiyyar data samune daga gareta. Yana kitchen ɗin harta kammala komai, ya sake ɗaukar kofuna uku ya ɗauraye da kansa ya haɗa da wanda ta wanke. Bata tanka masa ba, ta ɗauka flask ɗin kawai ta fita. Shine ya ɗauka sauran kayan ya fito da su, samunta yay tanama Ikram masifa akan ta tashi su wuce gida, ashe da wayarsa ya haɗata shi ya tafi neman magana kitchen..
      “Sai kun karya, tunda tace bakuyi breakfast ba kuka fito”.
    Ranƙwashi takaima Ikram ɗin, amma sai ta kauce tana dariya da faɗin, “Wlhy Yaya ita a barci ma aka tasota gara ni nasha tea”. Wani ranƙwashin zata sake kaimata ya zuba mata hararar data sata dakatawa, sai dai tayi gefe da kanta tana ƙunƙuni.
       “Oya zauna ki haɗamin yunwa nakeji”. Ya faɗa yana ajiye ledar dake ɗauke da kayan tea da abokansa suka rako shi da su a daren jiya tare da kaza. Batai magana ba, shima kuma bai sake maganar ba ya nufi ƙofar fita yasa key sannan ya wuce kitchen. Harara ta dinga zubama Ikram tana haɗa tea ɗin, tsabar mugunta ta zabga masa sugar. Ikram ta mikama nata tana faɗin, “Makwaɗaiciya kawai, daga zuwa gidan mutane”.
     Ikram tace, “Ni banyi kwaɗayiba tunda gidan Yaya ne”. Fitowarsa ta hanata bama Ikram ɗin amsa, ya dire babban plate dake ɗauke da kaza sai turiri take alamar ɗumamata yay. Zata miƙe yace, “Koma ki zauna.” babu wasa a lamarinsa dole tabi umarni, sai dai idonta harya fara tara ƙwallar takaici. Hanyar corridor ɗin da take ƙyautata zaton bedrooms ne ya nufa, cikin jin haushin da babu dalili ta raka bayansa da harara. Wayarta ta ɗauka ta cigaba da daƙila, kusan mintuna uku sai gashi ya fito, zama yay a ƙasan carpet ɗin shima kamar yanda take zaune. Yace, “Bani tea”.
    Batai magana ba, ta ɗauka flask ta zuba masa ruwan zafin akan kayan tea ɗin data haɗa a kofin. Sai da ta juya ta tabbatar sugar ɗin ya haɗe sannan ta miƙa masa. Duk da yaga bata haɗa nata ba sai baice komai ba yaja nasan gabansa da ƙyau, kaɗan ya ɗiba a cokali yakai baki dan yaji yaya test ɗin. “Ya ALLAH!”. Ya ambata da sauri. Tasan tsiyar da tai dan haka taƙi ɗagowa. “Kina hankalinki ƙuwa zaki saka min wannan sugarn?”.
     “Toni Yaya nasan yanda kake so ne?”.
   Idanu ya zuba mata kawai tsahon wasu sakanni. “Idan ma mugunta ce harda kanki zaki mawa, ba wadda take cikin gidan kawai ba, dan duk dodo ɗaya zaku yima tsafi”. Komai bata fahimta a zancensa ba. Wani kofin ya ɗauka ya raba shayin biyu, ya ƙara kayan tea ɗin banda sugar ya sake zuba ruwan zafi. Ikram dake ta faman latsa waya tana shan nata tea ɗin yace ta sakko.
     Duk yanda Anam ta so nuna ta ƙoshi bai saurareta ba. Haka ya tilasta mata karyawa tare da shi da breakfast ɗin da suka kawo da kazar daya ɗumama. Sai dai ita taƙi cin kazar ko sau ɗaya. Ikram kam komai sai da taji yakai mata sannan tai hamdala. Tayi niyyar suna gamawa su wuce, amma sai taga babu dacewar barin kwanikan, ita ta kwashe komai zuwa kitchen, ta ɗauraye kwanikan da suka ɓata. Koda ta fito bata samesa a falon ba, tacema Ikram ta tashi su wuce gida.
       “Lah aunty Anam Yaya yace mu jirashi zai fito muje tare”.
     Harara ta zuba mata, “Shi kuma driver daya kawomu fa yake zaman jiranmu?”.
      Fitowarsa ta hana Ikram bada amsa. babu abinda ya canja a jikinsa sai key ɗin mota daya ɗakko, ta ɗauke kanta gefe harya ƙaraso ya amsa wayarsa a hanun Ikram. Suna gaba tana binsu a baya har wajen mota, bataga driver ba, ba kuma ta tambaya ba. Ganin Ikram ta shige baya itama tai yunƙurin shiga....
        “Waye driver ɗinku?”.
   Fuska ta tsuke tana hararar Ikram kamar itace tai maganar. “Malama koma gaba”.
     “Ni dai aunty ki barni anan nafi son baya cikina ya cika da yawa zan kwanta”. A fusace ta ƙara yunƙirin yin magana ya dakatar da ita. “Bana son shirme fa kina ɓatamin lokaci nabar matata tana barci kowane lokaci zata iya tashi, ganina kusa da itane kuma abinda tafi buƙata a yanzun”.
      Tamkar saukar aradu haka furucinsa ya daki ƙirjin Anam saboda da yaren malay yay maganar yanda zata jisa ta fahimta da ƙyau. Idanunta ta rumtse ta buɗe motar ta shiga batare datace masa komai ba. Shima bai sake cewarba ya harbar motar zuwa waje dan maigadi dama ya wangale masa gate tuni........✍

    *_🚶🏻🤕😣askiya kuyima ƴar mitsilarnan taku kashedi ta fita sabargar angonmu.😚_*
     

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
0913484810_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107 ko



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*
[10/18, 8:00 PM] Mariyamah: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*




*_14_*


..........Ko parking bai gamayi ba da ƙyau a ƙofar gida ta buɗe motar ta fice. Ya bita da kallo harta shige gida. Ƴar ƙaramar ajiyar zuciya ya saki tare da murmushi. Ikram ta fito tana masa bye-bye. Hanun shima ya ɗaga mata har lokacin da murmushin a fuskarsa. Motarsa ya tada tare dayin reverse yabar anguwar dan baizo da niyyar shiga ko'ina ba tunda ko wanka baiyiba. Ga Fadwa dake buƙatar taimakonsa ya baro tana barcin gajiyar daya tara mata a daren jiya wadda shi kansa barcin bawai ya ishesa bane ba, kawai dai sawun giwa ne ya take na raƙumi.

       Anam batai magana da kowa ba ta haye sama, tasan ɗakinta zai yuwu su Amrah na ciki yanzu, na Mamie ma tana jiyo maganar mutane a ciki. Dan haka tai wucewarta falon Abie. Nan kam kowa bata samuba, hakan ya bata damar kwanciyarta ta saki kuka mara sauti. Kuka tayi sosai bana wasa ba har barci ɓarawo yay awan gaba da ita batare data sani ba. Wajen sha biyu Abie daya shigo ya ganta ya shiga taɓa goshinta da tunanin ko zazzaɓin nata ne ya dawo. Amma sai yaji babu zafi jikinta. Idanu ta buɗe da suka maita nauyi dan kukan data sha. Ta dubi Abie ɗin dake mata murmushi. “Sleeping beauty na ta tashi”.
      Murmushi tai da tashi zaune. “My Abie good morning”. Ta faɗa a marairaice. “Morning Darling duk gajiyar bikince ta saki zuwa nan ɓuyan barci?”. Fuska ta ɗan ɓata. “Abie su Amrah basa barina nai barci mai ƙyau dan surutunsu. Gashi ƙasa nake kwana dan bana son kwana da kowa ɗakin ma ya mana kaɗan”.
    Murmushi kawai yay da shafa kanta. Sai kuma ya dubi idanunta da suka sake fitowa da ƙyau. “Mamana idanun nan kamar anyi kuka da su?”. Da sauri ta girgiza masa kanta. “Abie rashin barcine fa”. Bai gamsu ba. Sai dai baice komai ba. Itama mikewa tai da faɗin, “Bara naje nayi wanka”. Tai maganar da zuwa ta kama hanunsa ta sumbata. Da kallo kawai ya bita, dan yasan tayi hakane dan karya cigaba da tuhumarta akan kumburin idonta daya tabbatar kukane ya sakasu komawa hakan tunda ba yau ya santa ba.

        Ta fito wanka tana shafa mai Amrah ta shigo ta sanar mata tayi baƙo. Da mamaki take kallonta sai dai batace komai ba. Amrah ma ta juya ta fita abinta. A nutse ta ƙarasa shirinta ranta fal tunanin wanene?. Ba ta da mai bata amsa dan haka ta fesa turare da ɗaukar wayarta ta fito. Tayi ƙyau sosai cikin wando da rigar jikinta, sai siririn mayafi data yana a kanta. A wajenta wannan shigace normal saboda a inda ta tashi, sannan rigar bata kama jikinta ba ta kuma sakko har kan mazaunanta. A falo ta samu su aunty Mimi, har zata zauna Mamie ta harareta. “Bake naji ance anzo nema ba?”. Cikin ɓata fuska tace, “Ni banyi da kowaba fa zai zo Mamie”.
     Aunty Hamida tai dariya. “To ɗiyata kika sani ko a ƴan biki ne wani yay sau da baya?. Tashi kije dan da alama mun kusa dawowa wani shagalin insha ALLAHU”.
       “Hu'um aunty ALLAH ya kiyaye ni karatu ma zan koma”.
    Daƙuwa aunty Hamida tai mata. “Karatun gidan ku, a wannan shekarun naki ai aure ne ya dace ko dan kina ganinki ƴar ficika da ƙaramin jiki? Maza tashi kije ana ɓata masa lokaci”.
     Badan taso ba ta fito, Mamie na kiranta tazo tasa hijjab bama taji ba dan a fusace take da taikaicin koma wanene.
    
       Dr Jamal dake daƙilar waya ya ɗago fuskarsa ɗauke da murmushi yana kallonta. Itako kallo guda tai masa ta kauda idonta. Kujerar dake gefensa ya gyara mata, ta ƙaraso fuska babu walwala tana masa sallama. Amsawa yay murmushinsa na sake faɗaɗa. “Barka da fitowa gimbiyar mata”.
       “Ina yini”.
Ta faɗa a takaice.
  “Lafiya lau. Bismillah ki zauna mana”.
          Kamar zatace a'a sai kuma ta zauna.
    “Kiyi haƙuri nazo babu izini. Sai dai karki manta dama nace zan zo dubiya”.
     Ɗan murmushin yaƙe tayi, a taƙaice tace, “Babu damuwa”.
    Idanu ya ɗan kafeta da shi, a ƙasan ransa yana tattaro abinda ya dace ya faɗa. Ɗagowa tai ta dubesa itama fuska a murtike. Ya kauda nasa idon. Cikin zolaya yace, “ALLAH ni sai ma naji ina jin tsoronki kamar”.
      Haka kawai yanda yay maganar ya bata dariya, ta shiga ƙyalƙyalawa shiko ya kafeta da idanu yana murmushi. A dai-dai nan aka buɗe gate ɗin gidan mota ta shigo. Su duka sukabi motar da kallo har lokacin kowanne da dariyar kan fuskarsa. Dr Jamal ya faɗaɗa tasa ganin Shareff, itako haka kawai sai da gabanta ya ɗan faɗi.
      Ya kai kusan mintuna huɗu bai fitoba idonsa kafe a kansu, sai dai shi basa ganinsa kasancewar tinted glass ne da motar. Murfin motar ya buɗe ya fito da nufin shigewarsa ya nuna bai gansu ba kawai. Sai dai Dr Jamal daya taso fuska ɗauke da murmushi ya hana hakan. Fara'ar dole ya ƙaƙaro yana mika masa hannu kamar yanda shima ya miƙamasa. “Ango! Ango!! Ƙyallinka dabanne”.
     “Haka dai kace”.
Shareff ya bashi amsa hankalinsa nakan Anam data ɗauke kai kamar bata gansa ba.
    “Haka ɗinne ma abokina. Dan ko kamshinka yau ya sake bunƙasa fiye da kullum. Muma dai gamu nan fara kafa foundation mukai matsayin nan naku haka nan”.
         Gabansa ne ya fadi, amma sai ya dake ya saki gajeren murmushi. “ALLAH yasa haka to.”
     “Insha ALLAH wannan karon da gaske nake abokina”.
   Nan ɗin ma murmushin yayi kawai da faɗin, “Bara na shiga na gaida su Mamie”.
       “Okay to a fito lafiya”.
Ido suka haɗa da Anam ya wulla mata wani mugun kallo data jima bata gani daga garesa ba ya wuce. Dr Jamal daba lura yay ba ya dawo ya zauna yana dariya. “Kinga Yayan nan naki da gaske angwancin nan fa ya amshesa. Kwana daya kacal harya canja kamar bashi ba”.
       Ƙin cewa komai tayi, sai dai tayi ƙaramin murmushi. Shima murmushin yayi yanaji kamar ya haɗiyeta. Sallamar Amrah ta katsesa daga kallon da yake mata. Duk suka dubeta. Gaishe da Dr Jamal tai, ya amsa cike da fara'a da tambayarta gajiyar biki. Tace masa Alhmdllhi tana maida kallonta ga Anam. “Anam Yaya Shareff yace yana jiranki zai amshi ajiyar daya baki”.
      Kallon Amrah take cike da mamaki da rashin fahimta, sai dai ta rasa abin cewa. Sai Dr jamal dake kallonsu ne ya katse shirun da faɗin, “Inaga jeki kawai ki basa saƙon sai na jiraki. Dan da muhimmiyar magana nazo”.
          Kamar zatace ita babu wani saƙonsa a wajenta sai tai shiru kawai. Ta mike zuciyarta na mata kaikawo da mamakin Yah Shareff ɗin. Yaushe ma har suka fara shiri dazai bata wani ajiyar abu..? Ita kaɗai ta nufi hanyar falon, dan Amrah fita tai dama cikin gida zata ya bata saƙon. Ta shigo ɗan lungun dazai sadata da ƙofar falonsu ya kuma zama hanyar dake tare data garden taji an fusgota. Ihu tai niyyar yi yay azamar rufe mata baki. Sai da ya maida ƙofar ya rufe sannan ya saki mata baki yana binta da wani shegen kallo data kasa fahimtar na minene.
     Baki ta tura tana gyara mayafinta. Ya sake harararta da binta da kallon sama da ƙasa fuskarsa a tsananin ɗaure. “Daga yau na ƙara ganinki da wannan banzar shigar gaban kowane ɗan iska ki tabbatar saina ɓaɓɓalaki na zubar. Ki kuma koma ciki, kona haɗa k da shi na zafafa. Tashi min anan kona kashe fuskarki da mari stupid”.
      Da gudu tabar wajen hawaye na silalo mata. Yaja tsaki mai kauri yana furzar da zazzafan huci daga bakinsa. Fitowa yay daga garden ɗin ya nufi falon shima dan dama ko shiga baiyi ba. Zama yay suna gaisawa da su aunty Mimi da ƴan uwan Mamie dama Abie ɗin. Kasa haƙuri sukai sai da suka tambayesa ko lafiya? Dan yanayinsa ya nuna ransa a ɓace yake. Ya kaƙaro murmushi yaƙe yana shafa kansa. “Bakomai fa auntys karku damu. Gajiya ce kawai da bata gama sakinmmu ba”.
      Mamie dake fitowa a kitchen tai yar dariya.  “To banda abun babana aida basai mun gankaba yau, sai kai zamanka ka huta sosai a gida ko”. Kansa ya shafa yana ƙara risinarwa. “A'a Mamie gara dai nazo na dubaku kuma hankalina zaifi kwanciya ai”.
     “To shikenan ALLAH yay maka albarka yaya ɗiyar tawa itama?”.
    “Lafiya lau tana gaisheku da muku bangajiya.”
          “Duk muna amsawa”.
Bai wani jima sosai ba ya fito, a waje ya sake samun Dr Jamal. Ya nufesa fuskarsa kadaran kadahan. Shiko Dr Jamal tasa kawace da murmushi. “A'a ango mijin amarya Fadwa har ka fito kenan?”.
       “Eh, ina so na ɗanje na sake hutawa kasan gajiyar biki. Kaima nayi mamakin ganinka anan kai da ya kamata ace kana can kana kwasar barci”.
       “Tab barci ai sai ku angwaye. Muko kwanciya mutum yayta rungumar fillos ai da gajiya. Gara mu fito farautar namu kayan kamar zaifi”.
            “Hakane, amma sai naga baka tafi farautar ba ai”.
     “Kajimun ɗan iska mi kazo kaga inayi? Inama take? Tunda kai akace kana kiranta”.
              Fuska ya ƙara tsukewa da ƙyau yana kallon Dr Jamal ɗin. “Yaka kafeni da idanu kamar naci bashinka?. Tunda kace babu ruwanka ni nazo da kaina na kafa gwamnatina”. Kansa ya kauda yana jan karamin tsaki. Kafin ya dawo da kallonsa garesa. “Jamal amma kasan bana son jan raini ko? Duk manyan mata dake garin nan da suka amsa sunansu mata karasa wa zaka so sai wannan ƴar abar haihuwar jiya”.
      Dariya sosai Dr Jamal keyi, “Oh badai an haifeta jiyan ba? To ni wlhy ko yanzu aka haifota ina son kayata a haka. Yarinyarnan ta haɗa duk abinda nake so ga matar da nake fata ta zama abokiyar rayuwata. Ni bana ganin waɗancan manyan matan sam a idona. Kai dai tunda ka ɗauka taka barni nima lokacina ne”.
     Tsaki yaja mai karfi da barin wajen. Dr Jamal ya bisa da kallo yana murmushi. “A gaishe da amarya sai munzo cin cin-cin”.
     Bai tanka masa ba, bai kuma juyoba ya shige motarsa ya fice. Agogo shima Dr Jamal ɗin ya kalla. Ganin lokacin da Anam taci babu alamar zata fito yay tunanin bara kawai ya wuce ya dawo anjima da dare. Yaran Aunty Hindu dake can gefe suna wasa ya kira babban. Leda dake dauke da kayan ciye-ciye na kwaɗayi ya bashi yakaima Anam ɗin shi kuma ya nufi motarsa.....

______________________________

Washe gari monday Anam ta koma aiki, Abie da kansa ya kaita. Hakan ya mata daɗi, ya kuma sakata a farin ciki har fuskarta ta kasa ɓoyewa. Da Yaseer ta fara cin karo, wanda rabonsa da zuwa aiki tun randa ya kaita gida. Kallon kallo suka tsaya yima juna, farin cikin da take ciki ya sata fara sakin murmushi. Cikin harshen turanci da mutsukka idanunta take faɗin, “Ko aljani ne kemin gizo”.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login