Showing 69001 words to 72000 words out of 84091 words
waiwayo ƙasarnan ba har abada balle ita karan kaɗa miya”.
A take fuskokinsu suka washe da murmushin jin daɗi. Fadwa tace, “Amma ni dai gaskiya ayi da sauri. Dan wlhy idan ina ganinta a gidana ji nake kamar na shaƙeta ta mutu. Bana son Soulmate ya dawo ƙasar nan tana gida na”.
“Batun kafin ya dawo ƙasar nan bazai yuwuba. Domin kin ɓata komai ga shirin yin hakan kuma ai. Dolene muyi ɓadda kamar da zasu cire ɓaranɓaramar da kikai a ransu gaba ɗaya daga nan har zuwa lokacin bikin Maheer, so nake da bikin idan sun zo su tattara ƴarsu su wuce yanda bazasu sake dawowa cikinmu ba har abada. Idan kuma kika ƙara yin wanu shirme to kiyi kuka da kanki bani Hannatu ba kuma”.
Baki Fadwa ta tura gaba sai dai batace komai ba. Nan su Mommy suka shiga jadadada mata ta kiyaye kar kuma a sake samun wata matsalar kamar yanda Gwaggo ta faɗa. Idan tai haƙuri komai zai zama labari dan suma basu da burin daya wuce Anam ta bar gidan ai. Miƙewa Gwaggo tayi, “To bara nayi nan karma wani ya shigo ya ganni. Shima kuma Mustapha kar wanda ya kirasa akan maganar mu jira muga ko wani zai sanar masa a cikinsu”.
Duk sun gamsu da hakan. Daddy dake bakin ƙofar yaja da baya a hankali yana ƙoƙarin danne ɓacin ransa. Dama yazo ne dan ya sake kwantar ma da Fadwa hankali da nuna mata tabar zargin kowa akan zubar cikin ta ɗaukesa matsayin ƙaddara. Amma sai gashi yaji ainahin abinda ma ke faruwa. Bai bari Gwaggo data fito tana murmushi ta gansa ba, sai ma ya juya yabar wajen ya fasa shigar...
Washe gari Daddy ya sakasu komawa can gidan Fadwa na ɗacin ran kasancewa da Anam. Khaleel ne ya ɗauke su su huɗu har mai aikinta dan maigadi shi tun jiya ya koma. Anam tai murmushi tana kauda kanta gefe ganin uwar hararar da Fadwa ke zuba mata kamar idanunta zasu zubo ƙasa. Sosai murmushin ya ƙular da Fadwa, sai dai batai magana ba har suka iso.
Kiran da Abie yay ma Anam a waya ne ya sata dakatawa su suka shige su uku. Itako ta tsaya anan jikin motar Shareff dake lulluɓe tana amsawa. Ta jima tana wayar kafi. ta nufi ciki itama fuskarta ƙawace da murmushi. Matar gidan kawai ta samu a falo zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya tana jijjigawa da yanka apple. Sai mai aikinta dake gyaran falon. Yi tai kamar bata ganta ba tai ƙoƙarin wucewa........✍🏻
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[10/26, 6:10 PM] +234 813 060 4664: *_Typing📲_*
*_❤🔥BABU SO....!!❤🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*
https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718
*_27_*
..........A hankali ta ajiye wuƙar tana murmushi, ta miƙe cike da isa da izza tana magana da shan gaban Anam, “To ƴar wasa da biri, ya akai ke kika zama birin kuma a hannun ƴan wasa?”.
Idanunta dake cikin gilashi ta ɗago tana kallonta, ta saki ɗan murmushi da kauda idanun kamar bazatace komai ba. Sai kuma ta hurar da numfashi da sake maida kallonta gareta. “Mi kikeci na baka na zuba Madam. Da Juwairiyya kike tare fa, _Juwairiyya Anam Usman MD Shareff_ bana gaggawa akan al'amarina, sai dai ina bama maƙiyi damar da zai sharemin hanyar fagen isar da saƙona. Su kin faɗa musu ni na zubar miki da ciki right? Tom ki jira shi kuma mai cikin yazo ya ɗaura bincikensa akan yanda akai na zubar ɗin, daga haka game ɗin zai fara ok!”. Ta ƙare maganar da kashe ido ɗaya ta rabata ta wuce tana dariyar rainin hankankali.
Wani irin bugawa ƙirjin Fadwa ya shigayi da sauri-sauri, tabita da kallo harta shige. Juyawa tai ta kalli mai aikinta, ganin aikinta take hankalinta baya kansu tai saurin barin wajen ta nufi bedroom ɗinta. Kai kawo ta shigayi cikin tashin hankali, dan da gaske kalaman Anam sun mugun dukanta, kanta ya kulle harma ta rasa kalar tunanin da zatayi. Tayi waya da Shareff a daren jiya amma bai nuna mata komai ba akan maganar rigimar zubda cikin balle tace ko Anam ɗin ta sanar masa ne. (To mi yariyarnan take nufi?) ta tambayi zuciyarta batare da tasan ta inda amsa zata fito ba. Ganin ta rasa ina zata kama ta yanke shawarar kiran Sima, dan tana da basira sosai, tasha warware mata ƙulluka da ita ta gaza kuncesu musamman da abokan hamayyarta irin su Anam ɗin......
Sima tazo, sai dai Fadwa ta jata sun fita can garden ɗin gidan dake bayan sashen maigidan saboda kar a ƙara maimaita irin na ranar. Acan suka tattauna. Har Sima ta wuce Aysha da Anam basu ma san da zuwanta ba dan suna can suna kwasar barci. sai yamma sosai suka tashi saboda saurayin Aysha daya kira ta zai zo.....
*******************
Tun daga waccan ranar Fadwa bata sake shiga sabgar Anam ba. Itama Anam ɗin bata shiga tata ba aikinta ma ya ɗauke kaso mafi yawa na hankalinta. Babban burinta tayi ta kammala tabar Nigeria ta huta. Bata sake waya da Shareff ba tun waccan ranar shima. Sai dai taga sunayi da matarsa wadda in ta gama Aysha kawai take cewa Shareff ɗin na gaidawa. Takanyi murmushi a duk sanda hakan ta faru, duk da kuwa a ranta tanajin zafi da haushinsa. Sai dai takan ce inma baice yana gaida tan ba sai me.
★A ranar wata alhamis da tai dai-dai da zubewar cikin Fadwa Daddy yay kiran Aysha da Anam akan su samesa a gida. Daga wajen aiki Anam ta wuce, inda ta samu Aysha tuni tana can. Basu sami zama dasu Daddy ɗin ba sai bayan sallar isha'i. Cikin kulawa su Abban ke tambayar su babu wata matsala dai ko?. Murmushi Anam tayi, dan kai tsaye tambayar tafi ƙarfi a kanta ne. Tace, “Babu wani damuwa sai na zafi”. Dariya Daddy da Abbah sukai mata.
Bayan sun sarara Daddy ya dubesu a tsanake, “Yauwa kun san miyasa muka kiraku nan?”. A tare sukace a'a. Daddy ya jinjina kansa da cigaba da faɗin “Magana ce mai muhimmanci akan aure, yanzu dai kunga kun kammala karatunku, babu abinda ya kamaceku sai aure inba so kuke mu zuba muku ido ku tsufa a gabanmu ba, dan haka muna mai baku umarni ba shawara ba, kowaccenku ta bama wanda yake zuwa wajenta dama yazo mu gana da shi”.
A ɗan tsorace Anam ta ɗago tana kallon daddy, ganin shima kallonta yake ya sata maida kanta ƙasa. Aysha kam murmushi ne ya suɓuce mata, dan kuwa dama Junaid nata damunta akan hakan, itace taƙi bashi dama saboda ganin yanxu ta Yaya Maheer akeyi ba suba.
“Mamana yaya dai?”.
Abba ya katsema Anam dogon tunanin data tafi. Kanta ta girgiza idonta na cikowa da ƙwalla. “Abba babu komai, kawai dai....” sai kuma tai shiru.
“Kawai dai mi? Faɗi kanki tsaye kinji Mamana. Maganar aure ba maganace ta wasa ba, shiyyasa muka zaɓi baku damarku duk da hakkinmu ne zaɓa muku mazan aure matsayinku na ƴammata”.
“Tabbas babu wanda zuciyarta ta aminta zata iya tsaidawa, sai dai kuma bata iya jayayyaba, koda wasa bazata iya ƙin bin umarninsu ba dan batun yanzu ba Abie yasha sanar mata su ɗin kamar shi suke a gareta, idan har taja da su akan koma minene na rayuwa dabai zama saɓama UBANGIJI ba tamkar tayi jayayya da shine. Sannan wani ɓangaren ta sani babu abinda iyayenta ke buri a yanzu tamkar ganin tayi aure, kuma itama a karan kanta tana son taga wannan rana kamar kowace ɗiya mace duk da zatai matuƙar kewar iyayenta a kusa da ita. Abu na gaba kuma burin Abie ɗinta ta fidda miji a ƙasarsu ta haihuwa Nigeria, ta tabbata kuma hakan zaisa su dawo kusa da ita suma duk da can yafi musu kwanciya hankali fiye da nan... A hankali taja numfashi, batare data yarda ta kallesu ba ta gyaɗa kanta alamar amsa umarninsu. Daga Abba har Daddy sunji daɗin hakan, dan haka suka sallamesu akan suna jiransu.
Gaba ɗaya Anam rasa sukuninta tayi a kwanakin da suka gabata, musamman akan wanda ya kamata ta tsayar matsayin miji a tsakanin samarin dake faman mata kaikawo su biyu. Wato Muzzaffar da Dr Jamal. Daga ƙarshe da ta fahimci zata saka kanta cikin wani hali sai kawai ta kira Mamie domin neman shawararta. Mamie uwace, sai dai ta raini tilon ƴarta da matsayi kala daban-daban bana uwa kawai ba. Shiyyasa Anam bata da wata ƙawa ko aminiya a duniya sama da Mamie, dan ko shawara zatai da Aysha ko Amrah sai ta gama da Mamie, koda abun mai nauyine a gareta tanajin kunya zata rubuta ta bama Mamien a rubuce. Yanzun ma hakan tayi, dan haka koda Mamie ta gama karantawa sai tai murmushi, Abie dake zaune a kusa da ita ta nunawa, shima dai murmushin yayi harda ƴar dariya. Ya amsa wayar yana faɗin, “Nine zan bata amsar daya dace da ita”.
Mamie tai dariya da fadin, “Uhhm nidai naga yanda zaku ƙare a wannan rana”. Dariya kawai Abie yayi, ya tafa saƙon ya turama Anam da dama zaman jira take. Shiru tai tana kallon saƙon, zuciyarta cike da wasiwasi. Sai dai kuma a ganinta tunda Mamie tace mata yayi to itama koda son sa bai kai mata har can cikin zuciya ba zata aminta da shi kuwa watarana zata so sa da izinin ALLAH. Sai dai kuma kamar yanda Mamie tace kartai masa magana da kanta bazatayi ba, tunda dama ya jima bai zo wajenta ba bai kuma kira wayarta ba sai lokaci-lokaci sukan ɗan gaisa a chart, shima kullum cikin cemata uzirine ya riƙesa yake.
★Kwana takwas dayin wannan magana abin al'ajabi ya sauka a MD Shareff family, ba komai bane kuwa sai baiko da saka ranar Anam da Muzzaffar, Aysha da saurayinta Junaid, za'a haɗe biki tare dana Maheer.
Su Mommy kasa magana sukai dan mamaki, duk da wani sashe na zukatansu sunji tamkar an musu rahama ne, amma kuma sunajin ɗaci da zafin ganin Anam ɗin zata auri wanda shima ba baya ba, dan mahaifinsa akwai kuɗi, shima kuma Muzzaffar ɗin a karan kansa akwai kuɗin dan wani babban gwaska ne a kamfanib MTN. Duk yanda suka so kuma danne abin a rayukansu kuma kasawa sukai har saida suka haɗu suka tattauna, sai dai a ɓangaren Fadwa ranar har ruwa ta zuba ƙasa tasha. Jitai kaso talatin cikin ɗari na tsanar Anam ya sauka a zuciyarta harta kasa ɓoye hakan. Ita Anam ma data lura da ita sai abun yay matuƙar bata dariya........✍
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[10/26, 6:12 PM] +234 813 060 4664: *_Typing📲_*
*_❤🔥BABU SO....!!❤🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*
https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718
*_28_*
...........A haka aka shiga shirye-shiryen bikin Maheer, Anam da Aysha. Yayinda kwanakin dawowar Shareff da ba'a sanar da shi komaiba ke kusantowa. Asabar ɗin daya rage saura sati uku biki Anam da Aysha acan gidan suka yini ana shirye-shirye da tsare-tsare. Anam dai ba shiga sabgar duk wani shirye-shirye take ba, su Fadwa ne dai ƙirjin biki keta kaiwa da kawowa duk da ango Maheer bawai yana ko leƙowa yaji yanda abubuwan ke tafiya ba ne, dan shi ƙiri-ƙiri nunawa yake baya son auren nan.
Haka itama Anam Muzzaffar yayi tafiya dan tunda aka fara maganar auren ma bata gansa ba, a wayama sai jefi-jefi dan baya ƙasar yaje wani aiki mai muhimmanci a yankin larabawa.
Washe gari lahadi Khaleel ya dauketa ita da Aysha kamar yanda yay mata alƙawari zuwa wajen tela. Kayanta takai na ɗinki, Mom ce ta bata su takai ɗinki kusan kala goma sha biyar. Kayane masu ƙyau da tsada har tana mamakin miyasa aka banbantata da Aysha, dan telan nata ma na musamman ne saboda Mommy taƙi yarda Aysha ta kawo nata nan. Bayan sun zaɓi ɗinkunan da take so ya gwadata ya faɗa misu bill ɗin kuɗin. Accaunt number ɗinsa Khaleel ya amsa, ya saka masa rabin kuɗin rabi yace sai ya kammala aikinsa. Daga nan gidan wata ƙawar Mom suka nufa ƴar sudan. Har Khaleel ɗin suka shiga ciki, yanda aka tarbesu ya bada tabbacin Khaleel ɗan gida ne. Sun ƙara tabbatar da hakanne lokacin da wata ƴar budurwa ta kawo musu abinsha tana ta faman sinne kai na kunya, yayinda Khaleel ke faman jifanta da wani kallo. Cikin yanayin tuhuma Anam ke kallonsa tana murmushi, yay murmushi kawai da ɗauke kansa gefe.
“Uhm to lallai ALLAH ya sanya albarka Yaya Khaleel, amma auntyn tamu fa tayi dan kun dace”.
Salute ɗinta yayi, hakan ya sakata kwashewa da dariya Aysha na tayata, dan ita ta kasa cewa komai tunda ba wasa yake da su ba. Fitowar matar hamshaƙiya ƴar gayu ya saka Anam haɗiye dariyarta. Suka gaidata cike da girmamawa itama tana amsa musu da kulawa cikin hausarta da bai gama nuna ba. Khaleel dake faman sinne kai ta kalla, “My son wacece a cikinsu?”.
Anam ya nuna, kansa a risine yace, “Itace wannan Mama”.
“Masha ALLAHU, ALLAH ya sanya albarka. Kace mata insha ALLAH bazai gagara ba, nima zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zan shigo dan maybe zuwa laraba mu fara, kaga zamu samu kwana goma sha bakwai kenan”.
“To shikenan insha ALLAHU zan sanar mata”.
Daga Anam har Aysha babu wanda ya fahimci inda zancen ya dosa. Sai dai ganin akan Anam ɗin ake magana ya tsaya musu a zukata. Ƙagara sukai su fita suyi tambaya. Amma sai matar ta tsaresu akan sai sunci wani abu. Su kaɗai suka ɗanci snacks. Shi dai Khaleel ruwa kawai yasha dan kunya. Ganin haka tasa budurwar nan mai suna Suhaima tai musu packaging ɗinsu dan harda gasashshen nama.
“Yaya Khaleel mufa kun samu a duhu.” Anam ta faɗa dai-dai suna shiga mota. Murmushi yayi yanama motar key, cikin basarwa yace, “Akan mi?”.
“Komai ma”.
“To kuyi addu'a ALLAH ya haskaka muku”. Daga haka yaja bakinsa yay shiru. Duk yanda sukaso jin ƙarin bayani bai basu fuska ba har suka iso gida. Kasa haƙuri Anam tayi sai da ta tambayi Mom. Kai tsaye Mom tace mata gyaran jiki na bikin amare za'ai mata dan taga duk tayi duhu. Murmushi kawai tai dan da gaske itama ta fahimci tayi duhun ko dan fitar da take kullum ne oho. Daga haka bata sake bin ta gyaran jiki ba.
*_Yau litinin_* da tai dai-dai da saura kwanaki goma sha ɗaya biki. A yau ake saka ran saukar su Mamie Nigeria sai dai Anam bata san da hakan ba. Hasalima ta tashi ne da ɗan zazzaɓi. Wajen ƙarfe sha biyu Muzzaffar yay kiranta a waya. Yanda yaji muryartane ya sashi ruɗewa yace zai zo ya kaita asibiti. Amma sai taki acewarta tasha magani. yata lallaɓata amma taƙi yarda dole ya barta dan yasan mutuniyar tasa ƴar tutsu ce. Koda sukai sallama ma sai ta kashe wayar gaba ɗaya ta gyara kwanciya. Wani barcin ne ya sake awon gaba da ita saboda maganin da Aysha ta bata tasha. Bata farka ba sai kusan uku. Alhmdllhi zazzaɓin ya sauka dan hakata samu tai wanka ta ɗanci abinci. Bayan sallar la'asar tana waje zaune ita da Aysha sai ga kiran Muzzaffar, kai tsaye ya sanar mata gashi a ƙofar gida. Murmushi kawai tai ta yanke wayar, dan zuwa yanzu kam Muzzaffar ya samu wani gurbi na musamman a zuciyarta duk da sun jima nesa da juna dan baifi kwana uku da dawowa ƙasar ba. Yau ne ya fara zuwa gidan suyi hira, dan haka sai da Aysha ta fita tayo masa iso, anan inda suke zaune da Aysha saman kujerun roba ya zauna. Aysha ta shige ciki ta kawo musa ruwa ta koma domin basu dama...
“Da alama zazzaɓin nan yaci amanar ango da yawa harfa kin rame dama gaki ba auki ba”.
Veil ɗinta taja ta ƙara rufe fuskarta tana murmushi. Shima ya murmusa cikin ƙara sanyaya murya yace, “ALLAH da gaske nake madam. Kodai aje asibiti?”.
“A'a ni naji sauƙi fa”.
“Kin tabbata?”.
Kanta ta jinjina masa. Murmushi ya sakeyi mai faɗi da shafa sajen fuskarsa. “Alhmdllhi ALLAH ya ƙara lafiya to”
“Amin ya rabbi.”
Shiru sukai na wani ɗan lokaci kafin ta saci kallonsa. Ganin ba ita yake kallo ba ta maida idanunta ƙasa ranta fal mamakinsa, dan babu rawar kan nan tasa, kuma bai kirata Beauty ba ko sau ɗaya. Murmushi yayi da gyara zamansa. “Madam nifa da magana nazo a bakina yau”.
Fuskarta ta ɗan buɗe sai dai bata kallesa ba. Ya cigaba da faɗin, “Juwairiyya gaskiya nima aure nake so”. A karan farko ta ɗago kai ta zuba masa dukan