Showing 78001 words to 81000 words out of 84091 words

Chapter 27 - Babu So Book 1 Hausa Novel Complete

06 Jan 2025

273

tana zuba masa hirar wahalar da taci lokacin da ta samu miscarriage. A ransa yana jin rashin daɗin rasa ɗan tayinsa, amma ya barma ALLAH tunda dama shine ya bashi bada wayonsa ba. A fuska kam tausayintane sosai sai dai baice komaiba. Rashin maganar tasa yasa ta sake yarda da maganar su Sima lallai da gaske baya buƙatar cikin a yanzu daman. Ta godema ALLAH data farga da wuri ta ɗauka mataki gashi yanzu farin cikin dake neman kufce mata na dawowa gareta.
        Basufi awa ɗaya da yin breakfast ɗin ba ya miƙe ya shiga bedroom, babu jimawa ya fito cikin shirin fita. Kallonsa take da mamaki. “Soulmate badai fita ba ko?”. Yi yay kamar baijita ba, ya kai zaune da ɗaukar wayarsa ɗaya, danne-dannensa yay yakai kunne alamar kira, hakan ya sata yin shiru tana kallonsa har ya kammala. Sake dubansa tai a shagwaɓe. “Dan ALLAH Soulmate fita zakai wai?”. Wayar daya gama ya ajiye gefensa, batare daya kalleta ba ya bata amsa. “Dama munyi dake bazan fita ba?”. Baki ta tura da dawowa kusa da shi ta zauna ta narke masa a jiki. Zata fara shagwaɓa sallamar Khaleel ta dakatar da ita. Kai tsaye ya bashi umarnin ya shigo, maimakon ta tashi a jikin nasa saita sake narkewa har Khaleel ya shigo. Kallo ɗaya yay musu ya ɗauke kansa tunda indai taɓarar Fadwa ce ba yau ya fara gani ba.
       Shareff daya fahimta bata da alamar tashi ɗin, ya dubeta yana ɗan tsuke fuska. “Gyara mana”.
   Baki ta ƙara tura masa, sai kuma ta tashi fuska a murtuke tabar falon ko amsa gaisuwar Khaleel batai ba dan har yanzu haushinsa na jiya na ranta ya mata addu'ar kishiya. Baibi takanta ba shi dai ya gaida Yayansa. Suka mike a tare suka fice dan motarsa Khaleel ɗin ya amso wajen wanki da yakai tun sassafe. Khaleel ne ke driving ɗin, yana gefensa suna hira da gaba ɗaya ma akan company ne. Sai ɗai-ɗai data shafi zamansa a gidansa wanda duk shine ke masa tambaya akan wasu abubuwan.
      Sun fara shiga sashen Daddy inda suka sami iyayen nasu uku zaune suna shan hira. Dan in har Abie na gari to bazaka taɓa rabasu ba sai dai in sun fita aiki, yau kuma babu aikin shiyyasa har breakfast tare sukayi. Bayan ya gaisheasu su duka suke masa fatan alkairi akan abinda yaje yayo cikin kulawa. Yaji daɗin addu'oin iyayen nasa dan su duka yana matuƙar jinsu a ransa. Ya ɗan jima anan tare da su suna hira har Khaleel ya fice ya barsu, sai da aka kira sallar zuhur suka fito suka nufi massallaci. A lokacin Anam nacan cike da farin ciki. Dan bata jima da tashi a barci ba Fawwaz ke sanar mata su Mamie sunzo. Da farko bata yarda ba su Husna harda Mom nata mata dariya. Ganin haka yasa ta mike ta nufi gidansu, tun a gate maigadi ya sanar mata, aiko da gudu ta shiga tana ƙwala kiran Mamie!! Abie!!. A lokacin Abie na can tare da su Shareff zasuje massallaci.
     Bayan an idar da salla koda ya shigo gidan sashin Mom ya fara shiga, suka gaisa har da ƙannensa sannan ya shiga wajen aunty Amarya. Daga can sai sashen Gwaggo data tsaresa yaci birabisko data dafa. Baici ba, amma yace ta saka masa a kula zaije dashi gida yaci. Taji daɗin hakan har cikin ranta, ya fito yana murmushin tsokanarsa da take. Sashen Mommynsa ya nufa inda anan ne ya zauna sukasha hirarsu har take kawo masa ƙarar Maheer da yay biris kamar ba shirin aurensa ake ba. Haƙuri ya bata da tabbatar mata zai kira Maheer ɗin a satin nan zai taho gida insha ALLAH. Taji daɗin hakan har a ranta. Yay mata sallama akan zaije gida sai zuwa dare zai sake leƙowa.
       Daga nan gidan su Anam ya shiga. Inda ya sameta nanuƙe da Mamie da Abie tana zuba surutu tana cin abinci. Suko sun biye mata sai dariya suke cike da farin cikin kasancewa da abarsu. Shigowarsa baisa ta daina surutunta ba. Sai dai taƙi yarda ta kallesa ko sau ɗaya dan tunda taji sallamarsa tai gefe da kanta. Shima kallo guda yay mata ya ɗauke kansa, ya maida hankalinsa gasu Abie. Tayin abinci Mamie ta masa babu musu yace zaici. Kasa haƙuri Anam tai sai da ta kallesa. Ya wulla mata harara ta tura masa baki da ƙyaƙyƙyafta idanu. Fuska ya sake tsukewa cike da gargaɗi a gareta ta taɓe baki. Duk abinda suke Abie na lure da su sai dai yayi kamar baya gani har Mamie ta dawo da abincin. Mace ce da sam bata da son jiki, yau da safe suka iso ƙasar amma bata zauna jiran wani ya basu abincin rana ba bayan na safe da suka samu Mom ta shirya musu. Tayi girkinta kodan farin cikin Anam, dan abinda tafi sone ta girka. Abincin ya faraci a nutse suna hirar China da su Mamie, itako ta daina hirar tana cin abincinta a shiririce tana saurarensu, sai dai sai balla ma Shareff harara take ta gefen ido.
        Sai da aka kira la'asar suka fita da Abie massallaci. daga can ya wuce gida dan tun ɗazun yake ganin kiran Fadwa na shigo masa yaƙi ya ɗaga, saima wayar da yasa a silent.........✍



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[10/31, 1:43 PM] +234 813 060 4664: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_32_*



...........Itama Aysha a ranar ta dawo gida da dare, shine ma ya kawota tare da Fadwa. Anam najin sanda suka shigo gaida Mamie ta maƙale a ɗaki har suka fita bata leƙo ba. Washe gari Mom tazo da mai gyaran jiki. Ba hajiyan bace zatai mata da kanta, ma'aikatan ta ne, amma saboda Mom tai alƙawarin shigowa kullum ayi a gabanta insha ALLAH. Ita dai Anam bata damu da wannan zancen gyara ba tun amsar da Mom ta bata a waccan ranar, dan haka koda suka korata a falo da zasuyi magana ko'a jikinta tama nufi can cikin gida wajen Aysha dake fushi da ita ta barsu. Da wannan damar su Mamie sukasha hirarsu dan Hajiyar Sudan tasan Mamie ɗin sukan haɗu idan ta shigo Nigeria.
      

_________________

       Tun daga wannan ranar aka farama Anam gyaran jikin mai inganci. Yayinda a cikin gida aketa shirin biki gadan-gadan babu wasa. Ita da Shareff dai haɗuwa ta gagara. Da zaran taji ya shigo gidan zata bar falo idan har tana zaune ne ma. To yanzu ma gyaran da ake mata babu dare ba rana yasa bama zaman falon take sosai ba saboda dokar Hajiyar sudan. Randa Maheer ango ne dai ya iso ta kasa haƙuri sai da ta fito cike da farin ciki suka gaisa. Sai dai yanayinsa ya saka mata sanyin jiki dan duk ya ɗan rame gashi babu fara'a tattare da shi.
    Washe garin da Maheer ya dawo biki na saura kwanaki goma sha biyar da daddare Shareff yazo gidan ya samu iyayensa a falon Daddy. Sune sukace yazo sunada magana da shi. Bai wani damu ba dan duk zatonsa maganar dai bata wuce akan Maheer ba daya kasa kwantar da hankalinsa akan auren nasa.
Bayan ya gaishesu Daddy ya fara bayani kai tsaye kamar haka. “Shareff mun kiraka nanne matsayinka na Babba ga duk yaran gidan nan. Da farko dai akan maganar auren ƴan uwanka ne, Maheer ya samemu jiya akan yanada wadda yake so ba wannan da ake shirin masa aure da ita ba, sai dai mahaifiyarku tace bazai aureta ba, hasalima ta haramta masa auren yarinyar. Munyi-munyi da shi yaƙi ya sanar mana wacece, sai dai ya roƙemu mu roƙa masa ita ta amince masa dan ALLAH. To kai tsaye dai mun amsa wannan roƙo nasa, sai dai munce yayi haƙuri a ɗaura wannan ɗin tunda an riga an gama magana karmu kasance ƙananun mutane, munga rauni a tare da shi, duk da baiyi jayayya damu ba. Dan haka munaso ka kasance da shi dan hankalinsa ya sake kwanciya. Sai auren Aysha da shima aka ɗaga kamar yanda dangin ango suka buƙata, duk da dai bakama san da zancen ba dama mun bari sai ka dawo a sanar maka”.
Numfashi Shareff ya sauke a hankaki, kansa a ƙasa cike da girmamawa yace, “Insha ALLAH Daddy zanyi hakan, ita kuma ALLAH ya zaɓa abinda yafi alkairi, duk yanda kukayi dai-dai ne ai”.
“Amin ya rabbi. Magana ta gaba kuma akan ƙanwarkane itama Mamana”.
Gabansa ne ya faɗi, amma sai ya cije bai nuna alama ba, sai ma ruwa daya ɗauka ya ɓalle murfinsa ya kai baki.. Daddy ya cigaba da faɗin, “Wasu dalilai sun sa mun yanke shawarar aurar da ita itama rana ɗaya da na Maheer ga wani bawan ALLAH da muke da tabbacin zai riƙe mana amanarta da izinin ALLAH. Itama an gama tsaida komai....”
Gaba ɗaya ya watso ruwan daya gumtsa har yana fesama Abbah dake a kusa da shi. “Subahanalillahi” Abba ya faɗa yana yana riƙo ruwan dake neman subucewa a hanun Shareff ɗin. Daddy da Abie kam sannu suka shiga masa dan bayan fesar da ruwan tarine mai ƙarfe ya sarƙesa. Idanunsa da sukai masifar kaɗawa da ja cikin ƙanƙanin lokaci ya ɗago yana kallon Daddy.
Sannu Daddyn ya ƙara masa hakan ya sashi maida idanun ya risinar. Daddy ya cigaba da faɗin “Karka damu munyi bincike mai zurfi a kansa kafin yanke wannan hukunci, sannan munada dalilai masu ƙarfi akan hakan. A matsayinka na babba saika sanya albarka a lamarin duk da yazo a ƙurarren lokaci ko”.
Kansa ya ƙara ɗagowa da ɗan haɗiyar yawu yana murmushin yaƙe. “ALLAH ya sanya alkairi”. Ya faɗa a takaice yana maida kansa ya dukar. Da amin suka amsa masa, daga haka suka cigaba da bayanin abinda yasa suka kira san. Bai bar wajensu ba sai kusan goma da rabi, ko'ina bai shigaba dan yasan duk sunyi barci ma yanzu ya shiga mota jiri na kwasarsa ya bar gidan....


★Ranar laraba aka saka amaryar Maheer a lalle, ga Anam dai babu abinda ya danganci hakan sai baƙi da suka fara cika gida. Sai a ranar alhamis ne da safe Abie da Mamie da Aunty Mimi da Abba da Daddy suka zaunar da ita. Bayan gama mata nasiha suka koma lallashinta, sai dai gaba ɗaya bata fahimtar wani fari ko baƙi a zantukan nasu, dan da alama brain nata ta raba tafiya da ƙwaƙwalwarta wajen yin aiki. har suka gama lallashinta taron ya tashi babu alamar numfashinta na fita daga gangar jikinta, a da kamar bata damu da auren ba, sai a ƙwanakin nan kuma jikinta ke mata matuƙar sanyi, rauninta na bayyana a zahiri. Bata samu damar fashewa da kuka ba sai da Aunty Mimi ta kamota suka komo ciki dan da suna a falon Abie ne.
Mamie dai kasa tsayawa tai, sai aunty Mimi ce ke lallashinta amma kuka ya gagara tsayawa. Gaba daya ta birkice cikin ƙanƙanin lokaci har takai idanunta sun fara daina gani da ƙyau. Hankalin su Mamie ya tashi, amma basu yarda kowa ya sani ba wani abokin Abie amintaccensa doctor ne na ido yazo ya dubata. Ya tabbatar musu damuwace ta kawo hakan, dan haka ya basu shawarar ai mata allurar barci ta huta. Wannan shine dalilin hana yin kamun amarya a yau da aka shirya sai dai anyi ɗan shagali duk da ba kowa yasan minene ya hana ɗin ba. A take ƙananun magana suka baje gida musamman ga su Mommy.
Duk da sun kasa gane kan zancen sunji farin ciki, har Gwaggo ta kasa haƙuri sai da tabi diddigin jin ba'asi, jin amarya Anam ce babu lafiya sai gata itada Mommy da Fadwa wai duba Anam ɗin lamarin zam-mamaki. Suna fita kuwa suka sanya dariya. Dan dama tun jiya suke dariya da ƙananun maganar rashin kawo lefen Anam gidan, acewarsu wane aurene haka kamar auren sadaka. Duk da zancen nasu ya koma kunen su Mamie harda su Daddy ma babu wanda yace komai.
Suna tsaka da wannan farin ciki Dr Jamal ya kira Fadwa yace tazo gida. Sagale tai tana kallon wayar dan ya yanke, kamar zata share sai kuma dai ganin da number ɗin Shareff ya kirata ta yanke hukuncin zuwa duk da kuwa a cikin tashin hankali suke da shi a kwanakin nan. Tadai danne ne kowa bai sani ba sai kawayenta su Sima dake ƙara tunzurata da tabbatar mata itace mai gaskiya.
Tasan bama suba duk wanda zataima bayani dole zai bata gaskiya. Dan kuwa ita dai babu abinda tai masa a kwanakin nan ya ɗorama kansa wani irin baƙin rai da yafi halinsa data sani. A gaba ɗaya satin nan baya fita aiki kullum yana gida kwance, da farko ta fara lallaɓashi da son jin minene matsalarsa? sai ya dinga daka mata tsawa da faɗin karta damesa, ta shanye na farko dana biyu ana uku takaici da ɓacin rai yasa tai fushi itama ta sharesa. Sai shekaranjiya da Dr Jamal yazo ya dubasa wai bashi da lafiya, haka ta haɗiye taje ta masa sannu ta kula da shi kuma, amma hakan baisa ya sake mata ba. Zuciyarta ta ƙara tunzura tun a jiya ta haɗo kayan tahowa nan gidan biki, gudunma karya ƙara ɗaukar azaba ya ɗora mata ta sanarma Mommy ta masa magana akan zata dawo nan gidan har sai an gama biki, bata san yaya sukai Da mommy ba tadai kirata tace ta taho, koda taje masa sallama bai tanka mataba sai hannu kawai ya ɗaga mata, itako tai fushi tai fitowarta ta barosa duk da taga kamar baida lafiya, ga wata rama da yayi a ƙanƙanin lokaci. Amma murnar Anam zatai aure yasa takejin dolene ta zam gaba-gaba a bikin nan ai, shiyyasa ta tsallakesa tai tafiyarta........✍


*_Tofa, su kawu Sharuffudden mike hwaruwa ne haka da ciwo kuma?🤭🤪🚶🏻_*



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/1, 1:27 PM] +234 813 060 4664: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718


*_33_*



.........Mommy ce ta shigo falon tare da aunty Iklima, batare data lura da halin da Fadwa ke ciki ba tafara magana cikin raba hankalinta biyu. “Fadwa a fiddo gift ɗin nan dan yanzu nake son ku wuce gidan wankin amarya ɗin nan ke da Bintu kafin sauran su biyoku a baya”.
      “Mommy inaga sai dai aunty Bintun tayi gaba. Dr Jamal ne yay kirana asibiti”.
    “Asibiti kuma? Mi ake acan ɗin?”.
“Inagafa jikin Soulmate ne, dan nata kiransa dama ɗazun bai ɗagamin ba sai nai tunanin baƙin ran nasa ne bai gama sauka ba”. Ganin tana tafiya tana magana Mommy ta riƙota da sauri. Kafin tace komai Fadwa ta rigata magana da ƙoƙarin yin gaba. “Mommy wlhy hankalina a tashe yake idan na dawo mayi magana”. Sakin nata Mommy tayi, Fadwa ta ƙarasa fita da sauri. Cikin sa'a ta samu napep data ajiye wasu mata.

        Azalzalar mai Napep data dingayi yay gudu ya sakasu isowa da wuri, ta miƙa masa dubu, yana mata maganar ga canjinta bama ta sauraresa ba tai gaba dan a rikice take. Tana tafiya tana kiran Dr Jamal, cikin sa'a ya ɗaga ya sanar mata inda zata samesa, sai dai bata gane ba. Dan haka ya turo mata Nurse ta shiga da ita.
       Yana kwance samɓal Dr Jamal na gyara masa ledar ƙarin ruwan da ake masa. Ta ƙarasa cikin sassarfa gaban gadon, idanunsa a lumshe suke alamar barci, yayi wani fayau da shi saboda ramar da yayi sosai, wadda ita sai ma yanzu ta sake ganinta a bayyane garesa.... Dr Jamal da gaba ɗaya yake cike da haushinta ya juyo yana kallonsa babu walwala tare da shi. “Fadwa yanzu kinyi dai-dai kenan? Mijinki na a cikin irin wannan halin amma kika tsallake kika tafi gidan biki kika barsa?. Badan ALLAH ya kai Khaleel gidan ba kin san kuwa komai zai iya faruwa?”.
      Kukan da take rikewa ta saki, ta kai duƙe gaban gadon tana kamo hanunsa da babu ƙarin ruwan. “Doctor ni ban san jikinsa yayi tsanani hakaba wlhy, duk ta inda na ɓullo dan nasan damuwarsa ya kasa bani damar hakan..”
           “Amma sai ki sanar a gida tunda ke yaƙi ya sanar miki....”
    Shigowar su Abba ya hanata bashi amsa. Khaleel dake gaba ya watsa mata harara ya ɗauke kansa. Taga harar tasa amma sai ta ɗauke kanta, tare da zare hanunta daga cikin na Shareff. Abba da Abie dai sai maimaita sunayen ALLAH suke a bakunansu, dan yanda Shareff ɗin yay fayau na rama a ƙanƙanin lokaci ya basu tsoto. Dr Jamal ya gaidasu, tare da kwantar musu da hankali akan su masa addu'a dan jikin nasa da sauƙi. Addu'ar fatan ƙara samun sauƙin sukai masa, tare da jajanta al'amarin. Abie ya kalli Fadwa dake gefe tsaye, faɗa ya fara mata akan miyasa bata sanar da kowa Shareff ɗin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login