Showing 18001 words to 21000 words out of 84091 words

Chapter 7 - Babu So Book 1 Hausa Novel Complete

06 Jan 2025

252

yay gaba abinsa kamar ta make masa ƙeya..........✍

_🤭🤗maza ki make to dan ALLAH_.


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
 
[10/16, 7:26 AM] Mariyamah: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


*_07_*


.........Tunda suka tafi tsakanin shi da ita babu wanda yayma ɗan uwansa magana. Yanata tuƙinsa da amsa wayoyi itako tana buga game a wayarta cike da nishaɗi har suka iso. Motar ta buɗe tai ficewarta tana taɓe baki, sai da ta rufe masa ƙofar batare data kallesaba tace, “Jazakallahu khairan” tai gaba abinta. Fusgar motar yay da ƙarfi yay gaba har yana tada ƙura. Hakan yasata faɗin, “Kaji dashi in kayane dai”.

        Koda ya tashi a aiki baibi takanta ba yay wucewarsa gida. Tun Anam na jira da marmari har ranta ya fara ƙuna gashi bata sayi layin Nigeria ba har yanzun. Sosai ranta yake a ɓace ga yunwa dake bala'in cin hanjinta dan bawani abun kirki taci da safeba ta fito, da rana ko inibi data taho dashi a bag kawai tasha da strawberry. Ganin yamma na ƙara mata, gashi bata san yanda zata kira wani a gidan ba tunda babu waya ta fito domin samun abun hawa ko zata iya ganewa. Ga wani irin zafi dake ratsata duk da rana ta risina kasancewar anyi la'asar, sai dai ita zafi takeji matuƙa kodan inda ta fito akwai ac ne.
        Ta tare abin hawa yafi sau huɗu amma ta rasa yanda zata musu misalin anguwar, wasuma basa gane jagulalliyar hausarta da yaren malay ya cinye, turancin ma idan tayi wasu suce basaji wasu suce basu fahimci kwatancenta ba. Kanta ta dafe ƙwalla na cika mata ido dajin wani irin tsanarsa a cikin ranta, tabbas bata ƙaunar wulaƙanci shiyyasa bata wulaƙanta kowa, kai bama ta tashi taga iyayenta na wulaƙanta wani ba kowa abin girmamawarsu ne koda bai kaisu wani matsayi na duniya ba. Hannu takai a hankali ta share ƙwallar idanunta tana maijin kewar iyayenta da ƙaunarsu, waɗannan matsalolin na ɗaya daga cikin abinda ta guda a zuwanta hidimar ƙasa Nigeria, amma su Mamie suka kasa fahimtarta.......
        Harya gota ta ya dawo baya da mamakin kodai gizo idonsa ke masa. Dai-dai saitin da take yay parking da sauke gilashin motar. Tabbas itace inhar bai ruɗeba, dan yanda yarinyar ta shiga ransa bayajin zai manta fuskarta koda a barci ya tashi.
     “Beauty!”.
  Ya faɗa cikin tsantseni da taraddadin wasiwasi.
           Duk da tajisa tunma tsayuwarsa hakan baisa ta ɗago ba. Sai ma sake haɗe fuska da tai ta ɗauke kai gefe fiye da yanda ya sameta. Murmushi ya saki dan yanda tai ɗin ya tabbatar masa ita ɗince. Buɗe motar yay cike da farin ciki ya fito. “A gafarce ni. Assalamu alaiki ƙyaƙyƙyawa”. Duk da bata saki fuska ba ta amsa masa. Ya koma ta gabanta cikin sake raunana murya. “Inaji a jikina ke rabonace Beauty. Ranar Yayanki ko saurayinki ne ban saniba ya gudumin dake gashi yau ALLAH ya haɗamu daga ni sai k”. Karon farko ta ɗan ɗago ta dubesa, ya sakar mata murmushi. “Dan ALLAH kar kice baki ganeni ba”.
     “Bamma taɓa ganinka ba”.
Ta faɗa da ƙoƙarin barin wajen. Sauri bin bayanta yay. “Please dan ALLAH karkimin haka. Ni ne wanda muka taɓa haɗuwa a GJ restaurant da daddare”. Sarai ta ganesa tun kiranta Beauty da yay dan muryarsa bata bace mata ba. Amma sai ta sake ɓata fuska aɗan fusace tace, “Bani bace Please kabar bina”.
       “Kiyi haƙuri bazan iya daina binki ba wlhy dan kullum cikin addu'a da sadaka nake akan ALLAH ya sake nunamin ke. Ya kuma amsamin sai nayi sakaci da damata”.
   Sosai ya bata dariya a wannan gaɓar, wai sadaka. Dan kawai ya ganta zaiyi sadaka. Hararsa tai zata sake wucesa ya babbake ko'ina. “Dan ALLAH ki saurareni”. Kanta ta dafe dan yanata faman haɗata da abinda bazata iya jayayya ba. Hakan yasa dole ta nutsu ta sauraresa. Bawata magana sukaiba damar kaita gida kawai ya nema. Bata da mafitar data wuce binsa, amma maimakon gida da yace zai kaita sai kawai ta buƙaci ya kaita inda zata sai layin waya. Bai musa mataba, dan a ganinsa hakanma wata damace.
        Kai tsaye office ɗin mtn dake cikin wata plaza yakaita duk da yasan sun tashi aiki yanzu. Sai dai yanada alfarmar da za'a iya biya mata buƙatarta a wajen. Ilai kuwa tarba ta mutuntawa taga ana masa a wajen, yanda kuma suke gaisuwa da ogan wajen taji a ranta ɗan uwansane ko aboki.
      “Mutumina wannan ƴar shilar fa haka?”.
    Abokin ya tambaya cike da shaƙiyanci cikin zaurancen hausa da Anam ta kasa gane komai dan shima ya fahimci bata iya hausan ba, saboda yanda yay mata tambaya da hausa ta gagara bashi amsa mai ƙyau. Dole suka koma magana da turanci. Murmushi kawai yay batare daya bashi amsaba, sai ma danna waya da yake faman yi abinsa.
     “Wai ka zama kurma ne?”.
Abokin ya sake tambaya yana harararsa.
       “Sarai ina jinka. Kai dai yi aikinka  kawai ba buƙatar tambayar ne”.
   Dariya kawai abokin yay ya cigaba da ƙoƙarin ɗaukar Anam hoto. Tun a gurin ta ɗora layin akan wayarta, ta kuma tambayesu ko zata iya amfani da shi. Kasancewar abokin nasa babban ma'aikaci sai ya amshi wayar yay ƴan danne-danne ya miƙa mata. “Indai kiran gaggawa kike sonyi da shi bashi nan da mintuna talatin sai kiyi”.
    Godiya ta masa tare da duban saurayin da har yanzu ko sunansa bata sani ba. “Zamu iya tafiya?”.
     “Why note Beauty”.
  Ɗan murmushi kawai tai da mikewa. Shima ya bama abokin nasa hannu suka cafke. “Friend ina zuwa ka jirani Please ”.
     “Ba damuwa”.
Cewar abokin nasa yana dariya.
        
    Ganin sun ɗan gota plaza ɗin tace su ɗan tsaya mintuna talatin ɗin su cika. Bai musaba sai dai ya kalla agogonsa duk gudun kar lokacin salla ya shiga. “Beauty inaga muɗan matsa gaba akwai massallaci sai na shiga nai magrib ko”.
     “Babu damuwa”.
Ta faɗa hankalinta akan wayarta. Tun fitarsa a motar babu abinda take sai irga mintuna har ALLAH yasa suka cika. Kai tsaye number ɗin Abie tahau gwadawa dan ta loda kati daga kuɗinta na bank a ciki. Taƙi samunsa saboda network. Komawa tai kan Mamie itama dai yaƙi tafiya kiran. A take idanunta suka sake cika da ƙwalla, ta kife kanta a gwiwarta tana karanto duk addu'ar da tazo mata a baki. A haka ya dawo ya sameta. Sai dai tanajinsa tai azamar goge hawayen nata ta haɗiye kukan.
     “Beauty ina muka dosa yanzu kenan?”.
           “Abinda nake tunani kenan, dan kona maka kwatance ba lallai ka gane ba. Amma in ban takurakaba ka kaini restaurant ɗin nan kawai ka ajiye zan samu mafita”.
        Kallonta kawai yake cike da nazari. “Na miki wani tambaya mana in bazaki damu ba?”.
    Shiru kamar bazata amsashi ba. Sai kuma taja numfashi da jinjina masa kanta. Gyara zamansa yay sosai yana fuskantarta. “Harshenki ya tabbatar min idan ma ke ƴar Nigeria ce ba'anan kike rayuwa ba? Hakan na nufin ke baƙuwace shiyyasa bazaki iya gane inda zakije ba?”.
       Nanma kamar bazata amsashi ba sai kuma ta ɗan kallesa ta duƙar dakai. “Karka damu ka kaini inda nace kawai Please”.
   “Baki son na sani ko?”.
“No, kawai”.
Ta faɗa a taƙaice. Bai sake magana ba ya ɗan rausayar da kansa da yima motar key yana murmushi.

         Koda suka iso kamar yanda ta buƙaci ya tafi ya barta a wajen bai yarda yayi haka ba. Cikin lallashi ya sata suka shiga wajen. Yabi ya takura mata akan ta faɗi mi take son ci amma taƙi, dan Anam nada wani hali inhar bata saba da kai ba bata taɓa yarda ta sake da kai. Shi kansa badan tana neman mafitaba bazata bisaba tun farko ko wane irin naci zai mata kuwa. Haƙura yay ya amsar musu drinks kawai da snacks amma ko kallon natan bataiba balle yasan zataci.
    Tunanin kiran Aysha ne yazo mata a rai. Ta sake zaro wayarta dake cikin bag ta hau lalubenta. Cikin sa'a kuwa kiran ya shiga, sai dai harya katse ba'a ɗaga ba. Bata gajiba ta cigaba da kira har wajen 8missed call amma babu amsa. Da ƙyar ta iya ƙoƙarin danne kukan dake son taho mata......

_______________________

      Ko kaɗan baiyi tunanin bazata iya maido kanta gida ba. Hasalima zuciyarsa raya masa take tuni ta dawo ɗin saboda yayi over time a office yau yana aiki, ga kansa na masa ciwo. Daya shigo gidan ma a ɗan gurguje ya shiga suka gaisa da Mommy ya fito. Wanka yayi a gaggauce shima saboda magrib dake kusantowa. Koda ya kammala shiri ya fito a compound ya haɗu da Abbah da Khaleel suma zasu massallaci. Tare suka fice, bayan an idar da magrib basu dawo gidaba sukai zaman jiran isha'i....

       Tun kafin su ƙaraso suka hango Mom da Aunty Amarya tsaye cirko-cirko a ƙofar sashen aunty Amaryar. Dukansu sai suka nufi can dan da alama babu lafiya. Shidai kusan shine ƙarshe dama. Daddy da suka haɗu a massallacin ne ya fara jefama su aunty amarya tambayar “Lafiya kuke tsaye anan haka?”. Aunty amarya ta bashi amsa cikin damuwa da ruɗani. “Daddyn Shareff lafiya ba lafiya ba. Anam ce bata dawo gidaba har yanzun. Mubarak yaje har wajen aikin nata kuma maigadi ya tabbatar masa babu kowa a ciki ita ɗincema kusan ƙarshen fita, ta kuma jima a titi kafin yaga wani ya ɗauketa a mota”.
      “Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un”. Daddy da Abba suka faɗa kusan a tare. Shareff ma dake daga bayansu gabansa ne ya faɗi, suka haɗa ido da Daddy daya juyo yana masa kallon tuhuma. cikin son danne abinda keson taso masa yace, “Shareff nasan dai kaji mi mamarku ta faɗa ina ka baromin yarinya?”.
      Sosai ƙirjinsa ke luguden duka. Ya girgiza kansa da risinar da idanunsa da sukai sirkin ja kaɗan saboda gajiya da ciwon kai.
      “Ba girgizamin kai zakaiba ka buɗe baki kai magana!!”. Daddy ya sake faɗa a tsawace.
            Kansa a ƙasa yace, “Ban baro office ba sai kusan 6, shiyyasa nai tunanin ta dawo gida”.
    “Shareff are you out of your senses?!! Har kake gayamin kazata tama dawo gida. Kana da hankali kuwa? Innalillahi wa-inna'ilaihirraji'un”.
         “Wai lafiya mike faruwa ne?”.
Mommy da Hassan yaje ya sanarma gidan babu lafiya ta faɗa tana ƙarasowa wajen. Babu wanda ya iya bata amsa saboda maganar da Daddy ya cigaba dayi a kausashe cikin kuma tsananin ɓacin rai....
       “Wlhy na baka nan da zuwa ƙarfe sha biyun dare ka kawomin yarinyata gida, inba hakaba sai ranka yayi mummunan ɓaci Al-Mustapha!!”.
           Cikin sauri Mommy ta dakatar da shi itama a fusace. “A'a Alhaji kamarya da wannan hukunci haka. Shine ya ɓatar da koma wacece ake neman da za'ace ya fita a wannan daren nemanta bay......”
        “Babu ruwanki a wannan maganar, idan kuma kikace zaki shiga wlhy zan sakaki nadama ne!!”.
      Gaba ɗayansu binsa sukai da kallo ganin yanda yabar wajen a matuƙar fusace. Banda Shareff da kansa ke ƙasa. Abba ne ya dubesa da damuwa shima, sai dai cikin sauƙaƙa murya dan bai kai Daddy zafi ba yace, “Son kayi kuskure. Ka manta Anam babu inda ta sani, ko anguwarnan bana zaton ta san sunanta ma, kag........”
     A harzuƙe Mommy ta katse Abba “Anam!!. dama akan wannan tsifatar yarinyar ake wannan tada jijiyar wuyar? Shareff bance ka fita harkar yarinyarnan ba a gidan nan?”.
      Bai iya ya ɗago ya kalleta ba, dan baisan wace amsa zai bataba. Tana ƙoƙarin nufosa isowar Gwaggo ya dakatar da ita. “Wai hayaniyar mi nakeji a gidanne haka kai?”. Duk juyawa sukai gareta. Ganin kowa ya kasa cewa komai Khaleel yace, “Anam ce bata dawo gida ba”.
       “Shine miya faru kuma? Ita ɗin yarinyace?”.
      “Haba Gwaggo ya zakice haka? Nawa Anam ɗin take? Sannan ina ta sani bayan kinsan kamar baƙuwa take a ƙasarnan bama garin kano ba”.
          Harara Gwaggo ta zubawa Abba mai maganar. “Oh to kana faɗaminne ko kana tunamin Abubakar? Gallaƙeƙiyar budurwa da yanzu idan aka sakata ɗaki da namiji zata samo ciki kake sanarmin nawa take? Toni abindama ban ganeba mi'akema hayaniyar anan?”....
      “Titsiye Shareff sukai yaje nemanta kamar shine yace ta tafi yawon tazubar ɗin, dan nasan bai wuci can ɗin ta tafi ba tunda an saba a inda aka fito..”
       “A lallai kuna bukatar Addu'a Abubakar. Shi Mustapha ɗinne ya kaita ya ɓatar da zakuce yatafi nemanta a wannan daren bayan wahalar da yaje ya gama shawowa a wajen aiki ya dawo. Kai Mustapha muje naga ubanda zai saka fita ko nan da gate a daren nan dan.......”
     Sauran maganar ta maƙale ganin kaf wajen babu alamar Shareff ɗin. Su dukansu babu wanda yasan yama sulale yabar wajen. Horn da ƙarar buɗe gate ya sakasu juyawa can gaba ɗayansu. Sai dai kafinma wani yay wani yunƙuri har motarsa ta fice.....

         Wajen aikin nata ya fara zuwa, sai dai kamar yanda maigadin wajen ya faɗama Mubarak shima haka ya sanar masa. Lokacin da yake tafiya a hankali ya dinga tafiya kozai ganta a hanya. Amma ko alamarta babu duk da titin wajen tako'ina akwai hasken fitulun solar. Duk da hakan bai fasa sake bi a hankali yanzun ma yana dubawaba har ƙarshen titin. Ganin har tara ta gota na dare yay fakin gefen titi ya kifa kansa kan sitiyari dan ciwo yake masa matuƙa kamar zai faɗo ƙasa. Dama tuƙin yinsa kawai yake cikin dauriya.

           A gida kowa ka kalla a cikin damuwa yake, idan ka cire Gwaggo da Mommy da suketa bala'i da kowa ya kasa fahimtar dalilin yinsa. Aysha harda kukanta. Dan ansan ko wayarta aka nema baza'a samuba tunda bata da layin Nigeria. Abba da Daddy da Khaleel ma sun fice police station.
      “Aunty wayarki sai haske yake tun ɗazun”. Hassan ya faɗa yana duban Aysha data zuba uban tagumi tana sauraren masifar Mommy kawai daketa faman kai kawo tsakanin bedroom ɗinta zuwa falo. Kamar Aysha bazatabi takan wayarba sai kuma tacema Hassan “Ciromin daga cajin”. Ciro mata yay, ganin bata san no ɗinba tai tsaki ta ajiye. Duk kiran da aka cigaba dayi har kusan sau biyar bata kulaba. Sai ma ɗaukar wayar datai rai a ɓace zata kashe sai saƙo ya shigo da no din da aketa kiran nata. Guntun tsaki tai ta buɗe dan taga wai waye ma ya addabeta ya barta taji da damuwarta ma itakam. Zumbur ta miƙe da waro idanu, har zata fasa ihu sai kuma tai saurin gumtse bakinta da satar kallon inda Mommy take. Tai saurin haɗiye farin cikinta ta nufi bedroom ɗinsu da sassarfa. Jikinta har rawa yake ta maida ƙofar ta rufe harda saka key tana dailing number ɗin...
      “Blood da gaske kece?”.
Kamar jira Anam keyi ta fashe mata Aysha da kuka. “Ya ALLAH Blood Please kibar kuka, kina ina ne yanzu? Ga gida duk hankalin kowa a tashe da rashin dawowarki su Yaya dasu Abba duk sun fito”. Ta ɗanji sanyi, amma hakan bai hanata jin zafin Shareff ba. Da ƙyar tace, “Zan tura miki address ɗin yanzu bansan inaneba”..... Aysha na katse kiran tai kiransa.

      Har yanzu kwance yake kawai akan sitiyari, yama rasa wane kalar tunani zaiyi shi kam. Ring na wayarsa ne ya katse masa tunani. Yay banza da wayar harta tsinke aka sake kira. Nanma bai ɗaukaba sai ana uku ya ɗago a fusace da nufin cin uwar mai damun nasa yaci karo da sunan Aysha. “Lafiya kika isheni da kira ke kuma?”.
      “Kayi haƙuri Yayah. Anam ce ta kiranifa yanzu da wani number sai kuka take.”
     Idanu ya rumtse da ƙarfi yana sauke wata irin bahaguwar ajiyar zuciya da har Aysha na jinsa. “Turomin number”. Ya faɗa a takaice kawai da katse kiran. Mintuna biyu kacal number ɗin da address ɗin data turo mata duk ta turo masa. Wayar ya cilla gefensa yayma motar key da fisgarta a guje yabar wajen. Tafiyar mintuna ƙalilance ta kawosa wajen saboda uban gudun daya zabga..........✍

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*


YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107




     
*_ALLAH yasa yau a rama mana marinmu😹😹😜🚶🏻_*
[10/16, 7:26 AM] Mariyamah: *_Typing📲_*




*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


*_08_*


..........Tunda ya amsa wayar ya turama wadda ta kira da sister ɗinta address ɗin inda suke yaketa lallashinta ko ruwa tasha amma taƙi sai faman sharɓan hawayema takeyi. Hakan yasa yay tagumi kawai yana kallonta. Komai tai birgesa takeyi, Duk da ƙaramin jiki da take da shi kai kasan ba yarinya bace, sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci lallai ƴar gatace a gidansu dan saurin karayanta yayi yawa. Hoto ya fara mata yana murmushi batare data sani ba.....
         Tunda ya shigo idonsa ya sauka a kansu. Wani irin baƙin ciki da ɓacin ransa sai suka ƙara ninkuwa. Nufarsu yay rai a ɓace sai dai bazaka taɓa fahimtar hakan akan fuskarsa ba duk da ya ciskulleta sam babu fara'a. Kamar ance ta ɗago idonta ya sauka a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login