Showing 21001 words to 24000 words out of 98628 words

Chapter 8 - Tmw Book Two Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

351

na yi mgana na Tuna a gaban wa na ke.
Idanuwana a sanyaye na dago ina kallonsa shima ni ya ke kallo.
Ammh sai naga ya basar da mgana da fadin"Na saka miki lambata in kina bukatar wani abu ki kirani na saka miki kudi a wayar."
Ya dakata kafin ya cigaba da fad'in"Sannan sai ki kira sauran yan'uwan ki ko?
Da kai ma amsa masa na kasa Rufe bakina.
Ya rasa ta inda zai faramin mganar ne yasa ya yi shuru ni kuma ta duba wayata ina murna kamar an sani a Aljannah.
Kamar daga sama naji ya na fadin"Hasiya kin taba fad'a ma wani ba anan na ke kwana ba ne?
Na girgiza masa kai Lokaci daya ina fadin"A'a."
Ina ji ya sauke ajiyar rai kafin yace"Yauwa. Kada to ki sanar da kowa kin ji ko? Ko Amma ko sauran yan'uwan kin ji ko? Wannan sirrin auran mu ne"
Sai da na yi masa mirmishi kafin nace"In sha Allahu ba wanda zai ji."
Numfashi ya saki mai karfi na samun salama.
Ina kallonsa nace"Na kira Adda Fati?
Kai tsaye yace"Kira ta mana ki na da lambarta ne?
Sai na gyada masa kai jiki na rawa da Hannuna na saka lambarta na kirata ta na dauka taji murya na tace su Asee asee an yi waya kenan nace mata eh.
Hira muka sha na manta da shima afalon ballatana girkin da na dora sai da ya fara kauri ni ban ma ji ba shine yaji ya yi min mgana ina chan muna hira da Adda Saboda murna har Mijinta sai da nace ta bashi mu gaisa.
Shi ya rigani isa kitchen din ya kashe gas din ya na fadin"girkin Amarya ya yi kauri"

Kunya naji da yasa na kasa mgana.
Sai da na sauke tukunyar na bude yaga uban abincin da na Dafa ya kama baki ya na fadin"Hasiya ina zaki kai wannan abincin?
Kai tsaye na kallesa ina fadin"Bazaka ci ba? Kuma zan zuba ma yan kawo amarya har yanzu ba'a kawo musu abinci ba."
Sai ya kasa musamin cikin yanayin mganarsa yace"To zubamin kad'an tafiya zan yi."
Yau sai naji ban damu da tafiyarsa ba.
A filet na saka masa da ruwa na kai masa falo.
Kuma abun mamaki ya ci kadan ya rage ya sha ruwa ya mike yace min zai tafi sai ya kara zuwa.
Ni kuma sai nace ya tsaya mu fita tare na mika musu abincin
Shi ya Daukamin kulan abinci ni kuma na Dauki karamin baho inda na saka musu ruwa da filet da cokullaya.
Har bakin kofar dakina.
Shi ya karbi key din ya Rufemin dakin ya na fad'in"Kada fa ki zauna achan da kin kai musu ki dawo dakin ki "
Da Toh na amsa masa.
Naso ya bani kulan ammh yaki har sai da ya rakani har kofar dakin Ummi sannan ya mikamin na tare hannuna guda d'aya na karb'a da mukullin dakin nawa saura kadan robar hannuna ta fad'i ya yi saurin tallafewa ya na fadin"Kin gani ko? Daman nace bazaki iya ba."
Wasu yan matan Amarya ya gani su biyu a kofar dakin suna kallon mu suna zaune.
Cewa ya yi su zo su taimakamin bazan iya ba ni ko fadi na ke yi wlh zan iya.
Cikin ido ya kalleni kafin yace"Bazaki iya ba SIYA.."
Sai na kasa yi masa gardama dukkansu suka taso d'aya ta karbi kulan d'aya ta karbi Roban sai alokacin nagane wad'anda suka shigo dakina ne.
Bai tsaya ba ya juya ya na fadin Sai da Safe.
Nima na amsa masa da Sai da Safe.



Slm ina maiso taga tayi kiba jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga nono yacika yayi kyau ina maiso taga duwawu yafito kinzama cikakiyar mace ❤️ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku *ZUMAR K'IBA*, zumace wadda take saka k'iba cikin kwana 7 da yardar Allah *ZUMAR K'IBA* zumace mai inganchi wadda aka had'ata da magun-gunan gargajiya Masu kyau da da tasiri ajikin d'an Adam,hajiya indai kina fama da rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kika sha zuma sai kin chanza..,Ina masu fama da Ciwan sanyi duk nacin sanyin ki hajiya kikai amfanin da maganin Mmn khairat saikin warke duk ko iya da d'ewarshi ajikinki..Domin k'arin bayani👉 WhatsApp no 07044450136, 08167453086




*Janafty*
*TMWB2K006*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/GoRzZ7ZgslV2alO5hYGAnj


*BOJUWA HERBAL'S BY SURAYYA DEE*!

*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Gaban ayu*.
*Hakkin daka gangariya*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
*Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
*Ana dafa GIMBIYAR KAZA da tattabarun garari*.

Bayan ya  b'ace ma  ganin mu ne har ma ya bude get ya fita daga gidan. Budurwan da ke kusa da ni ta kalle ni ta na fad'in"Ba shi ne mijin ki ba?
Cikin mamaki na kalleta sannan na gyad'a mata kai na alamun eh.
Sai naga sun kalli juna da ta kusa da ita kafin ta kara kallona ta na fad'in"Oh na gane kina da abokiyar zama ne ko?
Kura mata ido nayi cikin mamaki ina so na fahimci dalilin tambayan nata sai da ta ambaci abokiyar zama na Fahimci bakin zaren.
Dan daure fuska na yi kafin nace"A'a me ki ka gani?
Yanayin yadda nayi maganar ne yasa tace min bakomai.
Ina gaba suna bayana har cikin Dakin Ummi sai da muka kwankwansa wata yarinya ta zo ta bud'e mana.
Nasan kawai sun yi shuru ne ammh suna da tambayoyi fal acikin su.
Ni kuma na datse su ne saboda nima bani da amsar tambayan na su in kuma suka matsa zasu san abunda bai kamata su sani ba.
Sai a lokacin naga Ummi Amarya tunda har cikin bedroom din ta na shiga yan'uwanta da kawayenta suna ta min godiyan abinci da Dawaniya.
Hakane din ne baza mu wuce sa'annin ba sai dai ganin farko da na yi mata na Fahimci ba kamar ni ta ke ba.

Ita ta na da wayewa sosai da Bud'ewar ido sannan rayuwarmu da muka taso ba daya ba ne da ni da ita.
Ban wani jima a dakinta ba na musu sallama na koma dakina saboda ina zumudin na koma daki na kira Ramatu da Sabuwar wayata tunda itama na Haddace lambarta.
Ina ko komawa daki na dauko Sabuwar wayata raina fes na saka lambar Ramatu na kirata.
Nayi murnan jin muryata sannan taji dad'in jin na samu wayar da za su rika samuna.
Mun jima muna ta hira da ni da ita har gwarancin Noor nace ta sakamin ina so naji.
Gajiya inaga tayi dare ya yi yasa ta fara Hamma ta na fadin"Ke wai mijin ki baya nan ne hala?
Bansan me nace ba sai ji nayi bakina yace"Eh."
Da mamaki Ramatu tace"Eh kuma? Ke kad'ai ne yanzu a wannan gidan Hasiya?
Da sauri nagyara mgana ta da cewa"Ya na nan abokinsa ne yazo suka fita tare. Yanzu zai shigo."
Sai Ramatu ta sauke Numfashi kafin tace"Oh na zata baya nan nace ko yaje kauyen su ne?
Ni dai daganan ban kara mgana ba na samu muka yi sallama da ita.
Ban hakura ba na kara kiran Addan Fati nace ta turomin Lambar Adda
Rukayya da Adda ina so na yi mgana da Amma.
Karamin Tsaki Adda Fati taja kafin tace"Baki da Hankali ko Hasiya? Kinsan karfe nawa ne yanzu?
Sai da ta fad'a na duba agogon wayarta naga goma ta wuce.
Jiki a sanyaye nace"Sai da Safe."
Bata amsamin ba ta kwashe wayarta, sai na koma na lafe kan kujera ina cigaba da danna wayar tawa yau ban ji na wani damu ba.
Sabuwar wayar ta Daukemin Hankali na sosai.
Ina cikin Saving din lambar su Adda Fati na shiga cantact sai kawai naga Lamba da sunan ASSADIQ.!
nayi jim ina kallon Lambar sai na samu kaina da murmusawa.
Ranar na jima ban yi barci ba game na rika yi a wayar sai da idanuwana suka fara yaji na ijiye wayar na yi shirin kwanciya

Washegari ma Ummi ni ta roka na saka musu ruwan zafi sannan na ara musu kofinan da suka sha tea nima ba kayan kitchen din gareni sosai ba abunda na ke da shi na ba su.
Ranar kamar a gidan mu ne bikin Saboda duka Danginta nan suka zo da rana aka kara gyara daki.
Nima ba laifi ban wani zauna adaki ba ina dakin Ummi ina ganin abunda suke yi da rana ma Hajiya zainab tace kada na Dafa abinci daga gidan su Ummi za'a kawo abinci.
Lafiyayyar Jalop harda Nama suka Diba'rmin a kula mai yawa shi naci da rana har na ijiye na dare.
Da yamma kafin kawayenta da sauran yan'uwa duk sun watse sauran ne da suka Rage ango ya kawo mota har da Ummi suka dauketa zuwa gidan Surukanta, ammh kafin su tafi sai da Hajiya zainab tace ga Ummi ne mu zauna lafiya da juna nace mata in sha Allahu.
Ni dai ina ganin haka na shige daki na kulle na dauro alwala na yi sallar mangariba sannan na dauko wayata na kara kiran Adda Fati na kara mata Tuni lambobin da nace ta Turomin.
Sai tace bari ta bama Habiba ta Turomin ba jimawa Sai ga lambar Adda da ta Adda Rukayya.
Jikina na rawa na kwashe Lambar Adda na saka a cikin wayar ita na fara kira har sai da ta kusa katsewa sannan Adda ta dauka da sallamanta cikin Hausanta da ta had'e da Harshen Fullanci.
Cikin Zumudi na kira sunanta da Adda.
Bata gane ni ba sai da nace mata Hasiya ce sannan ta gane muryata.
Cikin shakiyanci tace"Au Hasiya ce? Kin gama Fushi da uwar taki kenan kin kira? Sai na kasa mgana kunya ta kamani cikin sanyin murya nace"Ku yi hakuri Adda."
Bata damu ba tace"Yar nema. Ga uwar taki tunda yanzu kin gane muhimmancinta."
Nasan tana mikama Amma wayar ta fice daga d'akin ina jin muryan Amma ta na kiran sunana.
"Hasiya."
Sai kawai na sakar mata kuka ina Fad'in"Amma ki yafe min don Allah."
Mirmishin nan nata ta yi min kafin tace"Baki yi min laifin komai ba Hasiya. Ban kuma rike ki a raina ba nasan komai daren dad'ewa watarana zaki kirani ki godemin."
Ina sharen hawaye nace"Ki yi hakuri Amma."
Amma tace"Nace kada ki damu bakomai yanzu dai ki fad'amin kina Lafiya? Ina Abubakar ina Fatan ba wata matsala ko?
Cikin Sanyin jiki da na Murya nace"Lafiya kalau mu ke Amma."
Ina jin Ajiyar zuciyar Amma kafin tace"Alhamdulillah daman ni na sani akwai wani lokaci da zai zo mutane su gane babu mai yi sai Allah."
Ina gyad'a kaina kamar ta na ganina nace"Amma ki ga fa babu abunda ya samu Assadiq wannan wayar ma shi ya siyamin ita jiya."
Amma na dariyan jin dadi tace"Daman ai ke baki isa ki yi ma wani mutum arziki ba, balle ki yi masa Talauci kuma ke baki isa ki sauya rayuwar wani ba Allah kad'ai ke da wannan ikon Hasiya."
Da sauri nace"Hakane Amma."
Amma Nasiha ta cigaba da yi min ta na kokarin nuna min komai ma da ya faru a baya ba ni bace daga Ubangiji ne kamar yadda ta ke kara gayamin yanzu.
Na kasa bude baki na gayamata kalubalen wannan auran sai naji bazan iya wargaza mata wannan Farincikin nata ba sai na yi shuru da bakina na saki jikina muna ta Hira.
Cikin Shagwaba nace"Amma na yi kewar ki yaushe zaki zo na gan ki?
Amma ta yi dariya kafin tace"Hasiya ki zauna lafiya a gidan auran ki. Ina nan watarana ke da Abubakar zaku zo ku gaisheni in sha Allahu."
Sai na kasa ce mata komai sai na basar da wannan mganar da fadin"Amma kina jin dad'in zaman chan?
Amma tace"Alhamdulillah hankalina a kwance nasan ya'yana suna cikin Tabattaciyar rayuwar da na yi musu fata."
Jin Amma na lafiya yasa sai naji na samu natsuwa mun jima muna Hira ina ta bata labarin gidan da na ke ciki jiya an kawo wata amarya zamu zauna mu biyu yanzu kafin sauran su tare.
Amma ta ta yi min fad'an na kama kaina nasan dai kalubalen zama a gidan Haya ji na yi kamar ban ji ba na gani nayi kamar ban gani ba sai na zauna lafiya nace mata in sha Allahu.
Sai da aka kira sallar isha'i sannan Amma tace zata yi sallah nima naje na yi sallah sai alokacin muka yi sallama.
Ban samu na kira Adda Rukayya ba sai da Safe kuma bata Dauka ba.
Sai chan da rana ta kira muka gaisa tamin murna jin nayi waya tace daman rashin wayar nan ba dadi gwara dai a rika jin mutum ya zauna Shuru ba waya a hannunsa.
Ba mu cika had'uwa da Ummi ba tunda ta na ta cin Amarci sai dai ranar litini mun had'u da Safe ta fito Diban ruwa nima haka.
Muka gaisa cikin sakewa sannan da Rana ta kawo min Cincin da su Dublan da yawa harda Alkaki.
Ban taba ganin mijinta ba sanda ya ke fita ina dakina kuma sanda ya ke shigowa ma ba na waje ina cikin Dakina.
Sai dai ina jinsu suna ta baki maza da mata mazan ina tunanin abokansa ne suka zo ganin Amarya da yammah haka ko da Daddare.
Matan kuma kawayen Ummi ne da yan'uwanta masu zuwa ganin daki da Rana.

Ba jimawa ta fara girki ranar ma ni na san mata kayan miya tunda na nika shi na tafasa shi ya ma kusa karewa, na gayamata ta saka a kawo mata daga gida nan ba'a samun kayan miya to ina ma d'an aiken? Ko almajirai ni dai ban taba gani ba ko suna shigowa anguwan basa zuwa gidanmu.
Ni na rika damun Adda Fati da waya ina mata shagwaban bata kara zuwa Dubani ba sai ga shi ta zo ita da yaranta gabadaya da Habiba suka min yini ita tazo min da kayan miya mai yawa har na Diban ma Ummi tunda itama da aka kawomata kayan miya da kayan lambu ta dibar min har kofar daki na tazo ta bugamin na bud'e ta bani na karb'a ina mata Godiya.
Sannan na rakasu su Adda Fati Dakinta suka gaisa ta tarbesu hannu bibbiyu ta ba su ruwa da lemu ta na basu hakuri cincin ya kare  naace kada ta damu na wajen nawa da ban cinye ba na basu sauran sun ci.
Ko da yaushe na shiga dakin Ummi sai naji kamar nawa ne Saboda ya Tsaru sannan koda yaushe cikin kamshin Turaren wuta.
Sannan Ummi akwai Daukan wanka da gayu ni dai ta na Burgeni sosai.
Da zamu tafi ta bama Hanif da Hanifa Dari biyu ta kuma rakomu har barandar Dakinta.
Da muka koma Dakina Adda ta yi ta yabon Hallayar Ummi ta na min Fad'an mu zauna lafiya da Amana.
Shinkafa da miya na yi mana muka ci muka sha sai bayan la'asar suka yi shirin tafiya.
Da Adda Fati tace ina Abubakar sai nayi mata karyan ya na wajen aikinsa.
Sai dai wani abu daya ya bata mamaki ita da Habiba suka kwashe kayan akwatina suka jeramin acikin wadrope ammh ko abunda ba'a so ba su gani na Miji na ba.
Da Adda ta tambayeni sai na rasa me zan ce mata sai karyan ya kai wanki ta fad'omin nace mata da Safe ya kwashe ya kai wanki.
Adda Fati har ta na ce min me yasa ni bazan kwashe na wanke masa ba.
Nace shi yace ma barshi zai rika kaiwa ana wanke masa.
Araina ko nace ina na ganshi ma? Na dai wanke sauran kayana da suka yi datti Tunda ya siyamin sabulun wanka da na wanki tun washegarin ranar da na tare.
Tunda ya zo ya kawomin wayar nan bai kara zuwa ba, kuma a Waya bai wuce sau biyu ya kirani ba.
Shima muna gaisawa yaji lafiyata sai yace min baya nan sun yi tafiya ne ammh in ya dawo zai zo.
Ya tambayeni ba ni da wata damuwa nace masa Eh! Tunda ga ranar bai kara kirana ba nima ban taba gigin kiransa ba na cigaba da Lallaba Rayuwata a yadda kaddara ta zab'wmin.
Jin dad'ina da Tarewar Umma in muka gama aikinmu zata zo dakina ko naje dakinta mu sha Hira da ya ke ta na da Surutu shiyasa duk wani Labarin da ya Danganceta ta na fad'amin da na Mijinta sannan in muka yi girki muna zuba ma junan mu.
Ban tab'a bata labarin Mijina ko yanayin Rayuwata ta baya ba.
Abu d'aya na taba gayamata da ta taba cemin hala ni buzuwa ce? Nace mata a'a Amma bafullatana ce Babanmu kuma Bazazzagi ne.
A lokacin Dariya ta yi ta na fadin"Shiyasa sunan ki ya zama Hasiya kenan? Daman sunan Fulani ne."
Ni kuma sai nace mata"Ba sunan Fulani ba ne sunan kanwar babanmu mai rasuwa na ci Hasiya."
Daganan kuma sai ranar kawai tazo dakina mu yi hira tace min"bata taba ganin mijina ba ko matafiyi ne?
Sai na samu kaina da ce mata Eh Saboda bani da mafita bayan wannan bata san komai a kaina ba.
Ummi ta iya girken girken zamani Sosai ni kuma na fi iya na gargajiya.
Tunda na saka Adda Fati zuwanta ta kawomin garin Damwake tunda na yi Ummi taci tace mijinta na son Damwake zan koya mata.
Nace mata me zai hana? Shikenan sai muka had'a kanmu ni da Ummi in ta na girki na kan shiga in gani sai dai ko in mijinta ya na nan in baya nan tare mu ke yi ni kuma daman mijina baya nan ta kan kai dare a dakina sai Mijinta mai suna Muhammadu ya dawo sannan ta ke min sallama ta koma Dakinta.
Bani da wata damuwa Rayuwa daidai misali mai sauki ni ke gudanarwa.
Muna waya da Amma kullum tunda kudin da ya sakamin a wayar sun kai Dubu uku har lokacin ba su kare ba.
Ummi kuma ta na da Sati biyu tace min zata koma aiki Tunda ta na koyarwa duk sai naji ban ji dadi ba Tunda mun fara sabawa.
Sai dai ba ni da yadda zan yi tunda Saboda ni bazata fasa zuwa aikinta ba.

******

*KADUNA.*
_Area: Malali_
8:35pm.

Zaune ya ke a falon gidansa mai cike da kayan alatu na more Rayuwa.
Wata takarda ne a hannunsa ya na Dubawa.
sanye ya ke da Riga da wando farare rigar bata da Hannu kamar na shan iska ne acikin gida.
Babban mutum ne domin zai iya kaiwa kimanin Shekaru Hamsin da Takwas zuwa da Tara a duniya.
Alhaji Jibril kenan ma'aikaci ne a Hukumar Nepa ta jakar kaduna wanda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login