Showing 30001 words to 33000 words out of 98628 words
yanayin jikina ya ke min kallon mara karfi.
Wasa wasa tun ina saka ran Assadiq zai ce min zai tafi har na saki jikina.
Daganan ya ke tafiya wajen aikinsa ya kuma dawo, an ce mutum rahma ne sai na fi walwala saboda zamansa tareni da ni shi kanshi kusan hakane baisan ya akayi kawai yaga ya na ta kwaso kayanshi zuwa gidana ba.
Tundaga ranar bai kara komawa Samaru ba sai dai za shi wajen aiki.
Sati daya cur muka kwashe tare kwanaki bakwai masu muhummamci matuka a wajena.
ko da ba Daki daya mu ke kwana ba Assadiq ya na da kirkin sannan ya na da kyakyawan mu'amala.
Ko aiki na ke yi ya na tayani sannan ya na nan ruwa dakina ya kare yaga na fara Dibowa daga waje ya faramin Fad'a wai na Dauki Almajiri mana nace masa ba Almajirai a barayin sosai.
Shi da kanshi ya Tube ya cikamin ko'ina ranar ma ina wanki yace na kawo zai tayani da na hanashi yaki hanuwa sai nace ya yi min Dauraya da Shanya.
Atsakar gida muka yi wannan Diraman da shi Ummi bata nan ta na makaranta, shi kuma ya shanyamin su tas sai nace mu had'a da kayansa mu wanke sannan ya amince.
Ina mamakin yadda kowani aiki ya iya shi sai da na tambayesa ya yi min mirmishi kafin yace"Ni fa Tashin kauye ne sannan goyan kakane ba kuma goyen Sangarta ba."
Har nake ce masa yaushe zai kaini na gaishe da Kaka.?
Kai Tsaye yace ba yanzu ba ammh zamu je watarana.
Ina lura da shi ko waya zai yi sai dai ya kunna wayarsa ya fice daga gidan sai ya gama wayarsa ya ke dawowa.
Ban taba tambayansa ba sannan ban taba saka masa ido kan wasu al'umran da bai sakani aciki ba.
A tunanina ko fita ya ke yi ya na mgana da Uban gidansa kila baya so yasan yana wajena.
Har acikin raina ban kawo tunanin komai ba.
Sadiq bai san Tahir ya Dawo ba sai ranar da ya cika sati a gidan Hasiya da yammah ya na kwance saman kujera ni kuma ina kitchen ina Kokarin yi ma na abincin Dare.
Wayarsa tun safe ta na kashe babban wayar kuma ta na chan samaru ya barota.
yaana kashe wayar ne saboda itace wayarsa da kowa ya san shi da ita akwai matsala in ya na barinta a kunne a kusa da Hasiya.
Ya kunna ne zai kira Tahir saboda Shekaranjiya sun yi mgana ya tambayeshi yaushe zai dawo?
Yace masa bai saka rana ba duk da Jikin Hajjan da Sauki har an sallamo su sun dawo gida.
Tahir da yajisa shuru ya tambayesa sai ya yi masa karyan daga wajen da ya ke bautar kasa ne bai samu Sarari ba.
Ya na kokarin kiran Tahir din sai ga wayar Tahir ya shigo.
Hanyar Kitchen ya kallah kafin da Sauri ya tashi ya shiga ciki ya Daga wayan
Ko sallamansa Tahir bai amsa ba yace"Kai dilla kana ina ne? Na dawo tun dazu ban ganka ba."
Sai Sadiq yaji gabansa ya fad'i da Sauri yace"Arm eh ina wajen aiki ne gani nan zuwa."
Tahir yace"Naga kuma bakwa kaiwa yammah?
Sadiq yace"Ina hanya gani nan zuwa."
Daga haka ya katse kiran.
Sai yaji zufa na ketomasa kamar Abba ne ya kira shi.
Bai tsaya ba ya fito daga Dakin Dole ya tafi yanzu bayaso Tahir ya Fahimci ga inda ya ke duk tsawon kwanakin nan.
Bai ma yi tunanin Tsayawa Dibar kaya ba ballatana takalmansa da ke gidana Jakarsa kawai ya Dauka sai kuma ya yi mantuwa laptop dinsa kan kujera bai sakata aciki ba.
Ina kitchen ya leko ya na cemin zai tafi yanzu.
Cikin mamaki na mike ina fadin"Tafiya kuma? Yanzu?
Ya na duba agogon hannunsa yace"Wannan megidan nawa ne ya kirani tafiyar gaggawace ta same mu. Zan kira ki a waya ki kula da kanki."
Daga haka ya wuce lokaci d'aya yana cemin nazo na kulle kofa.
Sai da ya fita ne na dawo naga Na'urarsa saman kujera kuma ya riga ya tafi, ni kaina duk jikina ya yi sauki Daman ban riga na Dora girkin ba ina gyara kayan miya ne.
Sai na barshi na koma kawai na zauna na yi Tagumi.
Shi ko Sadiq ya na zuwa ya yi ma Tahir karyan sun tsaya wani abu ne.
Shi kuma Tahir bai kawo wani Tunani a ranshi ba.
Hirar Hajja suka dinga yi da ciwonta har suka kwanta sai washegari ne ya Fahimci ya baro Na'uransa a gidan Hasiya.
Kuma sai da Tahir ya lura ba bu ita da ya tambayi Sadiq sai yace a wajen aiki ya barota.
Sannan suna saka takalman junan su Tahir ya Fahimci ba wasu takalman Sadiq.
Cikin mamaki ya tambayesa.
Wannan karon Sadiq sai da ya kusa ba da kanshi kafin karyan ya kai folish ya fad'o masa.
Ammh duk da haka sai da Tahir ya so ya gane wani abu.
*LAME NIG!*
*KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*.
*AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*.
*KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA*
*KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?*
*KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?*
*TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*.
*BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.*
*TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*.
*KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*.
*ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU*
*Janafty*
*TMWB2K008*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
*LAME NIG!*
*KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*.
*AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*.
*KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA*
*KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?*
*KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?*
*TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*.
*BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.*
*TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*.
*KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*.
*ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU*
https://chat.whatsapp.com/GoRzZ7ZgslV2alO5hYGAnj
*GUSAU.*
Asabar, 10:50am.
Yau asabar din karshen mako ne. Gidan Alhaji Sulaiman Shinkafi kamar yau d'in sun ta shi da Hidima ne sosai saboda za su yi baki daga Jahar kaduna.
Abokin kasuwancin Abba ne zai zo tare da iyalansa gabadaya.
Shima a gidan Alhaji Sulaiman su Umma sun yi ma yaran na su waya, suma duk za su zo wad'anda ke cikin garin kenan na nesa kuma ban da su.
Tun safe Umma da Mama ke kitchen a shaahen Umma suna ta dorawa suna Saukewa, tare da taimakon ya'yan su Salima da siyama sai Sultana.
Abinci kala kala su ka yi musu sai kuma lemuka kayan Snkas kuma Anty Surayya tace zata zo da shi.
Anty Sa'in kuma tace zata yo pepe Chicken ta zo da shi.
Ita kuma Sajida tace za ta yi Dambun Nama itama ta zo da shi.
Tun misalin karfe takwas da wani abu na Safe Abba yace bakin sun taso suna kan hanya.
Shiyasa suka fara aikin da wuri kada Bakin su iso kuma ba su gama ba.
Bayan sun gama girkin daman Tuwon Shinkafa ne miyar agushi suka yi musu sai Farar shinkafa da miyar Naman rago.
Sai jallof d'in Couscous da ta ji hanta da kayan lambu.
Sai lemun kankana, sai kunin gyada da Kunin aya.
Da farko Abba yace bakin a shashen Umma za'a sauke su ita kuma Umma taga ga bangaran Innani bai kamata a sauki baki a na ta Shiyar ba.
Sai tace a kai komai bangaran Innani a jera a nan bakin za su sauka.
Abba bai ce komai ba Mama ce ma taso ta yi mgana sai kuma ta fasa.
Siyama da Sultana ne ma su kai abincin zuwa Shashen Innani da daman Tun safe Sultana ta gyara Bangaran sai tashin kamshin Turare ya ke na daki.
Innani na zaune a kasan cafet a cikin Falonta sai faman kankaran Rake ta ke yi da wata karamar wuka, ta na sawa a baki tana mamula da hakoranta na roba.
Ta ci uban Dauri ta Rufe kanta Ruf har kunnuwanta ga gilashinta da ya cika rabin Fuskarta.
Atamfarta mai kyau ce super ce mai tsada, dinkin Riga da zani na su na Tsoffi.
Ta na jin sanda suka shigo ta dago ta na kallon su ba'a a falon suka jera komai ba ciki suka shiga da shi.
Innani ta gaji da shige da ficen su ta dago ta na kallonsu cikin takaici kafin tace"Nace lafiya ku kuma ku ke ta min Faman sintiri a shashena da Uban Safiyan nan?
Siyama ce tace"Kai Innani Abinci fa muke shigowa da shi."
Innani ta ce"Abinci kuma? Na waye?
Siyama na Tura baki tace"Na baki ne."
Innani tace"Bak'i kuma? In ji uban wa ya ce a kawo abinci nan?
Sultana ce da ke bakin kofa tace"Innani Umma tace mu kawo nan."
Sai Innani ta yi shuru kafin tace"Oho na zata kinibibin Suwaiba ne. Bakin sun iso ne?
Sulatana ce ta tsaya ba ta amsa ba Siyama ficewa ta yi ta na kunkuni.
Innani ta rakata da fad'in"Uwarki kika yi ma kunkuni ja'ira."
Ita dai Sultana ta fice ta bar Innani na ta masifa ta na faman cewa Sulaimanu ya auro dangin Jaraba sun zo suna neman hanata zaman lafiya ita da gidan d'anta.
Daman in dai wad'anan kalaman ne kusan duk wamda ke gidan nan ya Haddacesu daga bakin Innani.
Kowacce bangaransu ta wuce domin su yi wanka su shirya.
Salima daman ita suka bari zata gyara kitchen din Umma.
Masu aikin su daman basa zuwa Weekend saboda suna gida sai ranakun Litini zuwa jumma'a da basa gida.
Abba kuma ya fita ammh yace zai Dawo ba jimawa zai yi ba.
Ko kafin sha biyun rana ta yi kowa ya shirya Umma wani less dinta ta saka mai Tsada dinkin Doguwar riga ita kuma Mama sai ta saka Shadda ita mai Dinkin Doguwar riga.
Siyama kuma da Sultana shigar Maryam Epytian Abaya su ka yi.https://chat.whatsapp.com/CPRnRPcAD5K8vEY91Ziz8V
kuma duka iri d'aya suka saka kalan pick ma su kyau da Tsari sun kuma yane kansu da mayafin Abaya.
Ita kuma Salima daman iyayen iyayine wani material ta saka Dinkin Riga da sikat ne sun mata kyau sosai kamar wata black American
Kuma daman Salima ta na da kyau sosai suna kuma D'iban kama daman da Sadiq.
Zuwa kuma lokacin su Surayya duk sun iso suma tare da ya'yan su suma sun yi shigar alfarma kana ganinsu kasan ya'yam manya ne sannan kuma suna auran manyan mutane ma su Rufin asiri.
Gabadayansu Bangaran Innani suka yada Zango tunda nan bakin za su fara sauka, Innani sai washe baki ta ke yi ballatana kowacce da yar ledanta na Innani ka na bata zata fara washe baki ta na zuba mu su albarka sannan har taja ya'yanka a jikinta.
In kuma baka zo ka bata komai ba ta Dinga Hararanka kenan, in kaci sa'a ka tafi salin alim ba'a bika da gori ba.
Sadiya Kaza guda ta soya ma Innani suyan da ta ke so, Innani ta saka mata albarka kamar me.
Sa'ima Miya ta yi mata mai Naman sa, Sai ga Innani na fad'in ya'yan Suwaiba duka ya'yan albarka ne ya'yan mutumci.
Siyama ta kalleta ta na mamaki, Dazu da Safe ta gama cewa ya'yan Suwaiba ya'yan Jaraba ne ammh shine Saboda abun duniya har ta sauya mganarta.
Ai Innani in dai kana son Siye bakinta to toshe shi da abun duniya shikenan sai ka samu lafiya.
Sha biyu da rabi da wani abu baki suka iso tare da Abba suka iso daman sanda Alhaji Jibril ya kirasa ya fito daga inda yaje zuwa gida shine kawai yace Direba ya tsaya a hanya su taho tare da su zai fi da kwatance.
Suna shigowa Haraban gidan Abba ya kira wayar Umma yace su fito su tarbi baki ga su nan a haraban gida.
Umma ta shaida ma Mama da Sauram yaran suka Dumguma gabadaya.
Har da Innani da ta mike ta na Faman Dogara sandarta.
Salima ta kalleta lokaci d'aya ta na fad'in"Innani ke kuma ina zaki je kina tafiya Dakyar?
Innani ta kalleta kafin tace"Gidan uwarki zani. Ka ji min yarinya mara kunya? Ina ce baki nan na Sulaimanu ne ba bakin Suwaiba ba ko?
Umma ce ta katse fad'an Innani da Riko Sandarta ta na Fadin"Kyaleta Innani muje ke ya kamata Daman ki Fara musu maraba."
Innani na jin haka sai ta washe baki ta na fad'in"Yauwa salamatu yar albarka."
Sauran gaba su ka yi Mama daman ta na jin Innani ta fara ambaton sunanta ta bata rai ta na Hararan Salima domin tasan ita ta ja mata zagi wajen Innani da daman bata taba fari a wajen wannan Tsohuwar ba.
Umma ce ta tsaya ta na taimaka ma Innani suka fito tare.
Duk suna Haraban gidan Abba ne sun Sarke Hannu da Alhaji Jibril suna gaisawa kowanne fuskarsa cikin Annuri da Farimciki.
Dukkansu kuma suna Sanye da Manyan riguna kamar wad'anda za su je wani waje Daurin aure.
Su Mama kuma Hajiya Murjanatu suka nufa cikin Sakin fuska suna yi mata maraba da zuwa.
Siyama ne da Sultana suka tarbi su Fathihatu da Zahra'u Salima kuma na gefe ta na faman Danna wayarta sai dai ta na wani kare ma mutane kallo cikin irin takun ta.
Mubarak na gefe shima ganin ba shi da aboki namiji a wajen.
Sanye yake cikin shigar shadda Fara dinkin zamani kafarsa cikin bakin Takalmi na Fata mai kyau.
Kansa kuma cikin Hula kube kalan aikin shaddar jikinsa mai baki baki.
Muryan Innani ne ta karad'e wajen da Muryanta sanda suke karisowa ita da Umma.
Cikin muryanta na Tsufa tace"To gani na iso ina shi abokin Sulaimanun ina so na ganshi da idona."
Jin haka yasa aka bata Hanya Abba ya kalli Alhaji Jibril ya na yar Dariya yace"Ga mahaifiyata da na ke yawan baka Labarinta."
Innani ga Alhaji Jibril abokin kasuwancina ne shekaru biyar da suka gabata."
Innani ta washe baki ta na Fad'in"Ma sha Allah sannu Jibrulu sannu kaji? Ai sulaimanu akwai kirki ga mutumci da son jan mutane ajiki sannun ku da zuwa Allah ya yi muku albarka."
Alhaji jibril cikin Ladabi ya ke amsawa da Ameen Ameem kafin ya Zube a kasa ya na gaida Innani.
Ita kuma sai amsawa ta ke yi cikin waahe baki taji dad'in ganin yadda ya bata girma.
Alhaji jibril ya gabatar da iyalansa ga Abba shima Abba ya gabatar da na shi iyalan a wajen Alhaji Jibril.
Sai faman saka albarka ya ke yi Alhaji Jibril ya Dafa kafad'ar Mubarak da ke gefensa cikin mirmishi yace"Ga babban yaro na Mubarak."
Abba ya ba ma Mubarak hannu suka yi musaba yana tambayansa karatu yace ai ya gama yanzu aiki ya ke yi.
Innani ce taga ana ta tsayuwa ga shi ta gaji sai ta yamutsa fuska kafin tace"Wai nikam a tsaye zamu yi zumuncin? Haba ni na gaji tunda ba Dije soja sunana ba."
Gabadaya sai da aka yi Dariya Alhaji Jibril da sauri ya rike Sandar Hannun Innani ya na fad'in"Mu je Innani na yi miki jagora."
Innani ta washe baki ta na fadin"Allah ya yi albarka kaji Allah ya raya zuru'a."
Ya na ta amswa da Ameen Ameen.
Umma da Mama suna tare da Hajiya Murjanatu su ke bin bayan su Abba zuwa Bangaran Innani.
Su Surayya kuma suna tare da Fathihatu wacce ke Dauke da Danta karami namiji sai Siyama da su Sultana da ke tare da Zahra da Fatima Batul.
Kamal kuma daman ya na tare da Babansa ne.
Salima ce ke baya ta na tafe ta na taku d'aya bayan d'aya wayace a hannunta hankalinta ma baya kan in da take takawa.
Har sai da ta kusa cin Tuntube ta fad'i Mubarak da ke bayanta kamar ya na kirga takunta ya yi gaggawan tareta ta hannun hagu shi ya taimaketa daga Fad'uwa.
Ido cikin ido suka kalli juna kafin Salima ta yi saurin janyen kallonta Daga gareshi ta na fad'in"Thanks."
Kai ya gyad'a mata batare da ya yi mgana ba.
Sai dai ya nuna mata hanya da hannunsa ta fara yin gaba sannan shi yabi bayanta.
Ya na tafe ya na kallonta ya na mirmishi daga ganinta a ransa yace ta na da aji da isa.
Afalon Innani a ka yada Zango Abba da Alhaji Jibril duk suna zaune a kasan Cafet ne gaban innani haka su Umma da Sauran yaran
Salima ce ta zauna kan kujera ta na mai Dora kafa d'aya kan d'aya.
Hankalinta na kan wayar hannunta.
Gaisawa aka sake yi cikin mutumtata juna.
Da kuma tambayan Hanya da Mutanen gida.
Ruwa Umma ta ce su siyama su fara kawowa tare da Lemu saboda su fara sha su jika makoshi.
Siyama da Sultana suka rika wannan Zirga zirgan salima na zaune bata ta shi ba, daman ita yar iyayi ce bata son aiki sosai sai ya zama Dole.
Mubarak na gefe ya na kallon Salima ammh cikin takun da ba ta sani ba
Haka kurum ya ke jin yarinyar zata yi daidai da Zabinsa sannan da Ra'ayinsa.
Sultana ta kawo masa Ruwa mai sanyi har gabansa ya karb'a ya na fad'in"Thanks."
Mirmishi ta yi masa shima sai ya maida mata da martanin mirmishin nata.
Bayan sun sha ruwa sun natsa Abba ya duba agogon hannunsa yaa na fad'in Lolacin sallah ya yi su fara gabatar sallah tukunnah.
Umma ta ja Hajiya Murjanatu bangaranta suka yi sallah bayan Abba da Alhaji jibril tare da Mubarak da kamal sun fita zuwa masallaci.
Siyama da Sultana su ka ja Zahara'u da Fatima batul duk da ba sa'ar su ba ce sai dai salima in ma bata girme mata ba ammh halin Salima sai ita shiyasa suka ja Zahra'un a jiki, a nan Shashen Innani suka yi na su sallar.
Su Anty surayya kuma suna bangaran Mama tare da Fathihatu.
Sai da Su Abba suka dawo daga masallaci sannan aka zauna zaman cin abinci.
Sultana da Siyama har da Salima suka Shimfid'a babbar Darduma a tsakiyar Falon Innani aka jera komai a samanta
Sannan suka zagayeta kamar cin abincin Larabawa.
Innani ce kusa da Abba da Alhaji Jibril sai Mubarak da kamal sai Umma da Mama da Hajiya Murjanatu.
Sai su Anty surayya sannan su Siyama ne a karshe.
Salima ce chan kusa da Innani ta Hannun Hagu, suna kuma Facing din juna ita da Mubarak duk sanda kuma ta Dago kanta sai sun had'a ido.
Shiyasa sai ta kasa sakewa ta ci abinci sosai Sarver ur self ne kowa da kanshi ya sama ma kansa abunda ya ke so
Innani ce Alhaji Jbiril ya zuba mata ta na ta saka masa albarka.
Ba innani kad'ai ba batta su Abba sun ji dadin ganin irin yadda Alhaji Jibril ke kula da Innani tun zuwan su.
Abba ya kallesa ya na fadin"Nagode Alhaji Jibril."
Sai kawai ya kad'a kai kafin yace"Haba bakomai mahaifiyata ta rasu da jimawa ina kallon Innani kamar uwa ce a wajena."
Sai Abba ya jinjina kai cikin kara ganin kirki da Dattakon Alhaji Jibril.
Suna cin abinci sama sama suna d'an Taba Hira har suka gama.
Wannan karon manyan suka