Showing 1 words to 3000 words out of 98628 words
*TMWB2K001*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
https://chat.whatsapp.com/GoRzZ7ZgslV2alO5hYGAnj
Kamar wasu zakaru haka suka tsaya a bakin hanya suna kallon juna.
Shi Sadiq ya Rufe kwayan idanuwansa ammh da ya bayyanasu da rauninsa ya bayyana, sakamakon Tahir da ke kallonsa cikin takaici da wani irin bakincikin da bai taba tsintar kanshi aciki ba.
har gwara ace Mutuwa a kayi da wannan Danyen Hukuncin da Sadiq ya yanke ma Rayuwarsa.
Tahir bakinsa ne ya yi nauyin da ya kasa mgana shi kuma Sadiq ba shi da kalaman da zai kare kansa a lokacin.
Har abokan aikinsa da ya gayyato Anas da Mudansir ba yan zariya ba ne dukkansu yan cikin garin kaduna ne.
Zuwa suka yi suka ba shi hannu suka yi musabaha tare da yi masa murna.
Duk da auran nasa ya ba su mamaki lokaci d'aya haka, Sannan ba kamar sauran aurarrakin da suka saba zuwa ba ne wannan sai ya zame musu kamar Dabam.
Ammh kamar yadda Sadiq ya yi musu gim da fuska Haka Tahir ya kallesu ya watsar shi ko hannun bai mika musu ba sai ya koma jikin Bangon gidan Baba Tanko ya jingina bayansa lokaci d'aya ya hard'e hannayensa a kan kirjinsa ya na hangen Sadiq yan Tsirarun mutanen da ba su watse ba suna ta faman yi masa Allah ya sanya Alheri cikin su harda Isuhu duk da shima ya yi mamakin faruwar auran da gaggawa haka kuma shi Adda bata fad'a masa da wani daurin aure ba ta kuma tabbatarsa masa Amma da Hasiya zai Dauko ya kawomata ammh ganin abunda ya faru sai yasan dole Lissafin ya sauya.
Bai jira sauraran Habiba ba ya hau mashi ya koma Samaru.
Ya bar su Sadiq a kofar gidan Baba Tanko Tsaye mai afkuwa ta riga ta afku shiyasa Sadiq ya ji gabadaya duka kalaman bakinsa sun kare shi kuma Tahir kafafunsa ne suka yi sanyin da suka kasa Daukansa ballatana yasan mafita bayan sun fito daga wajen da aka daura auran da har Abada ba yajin zai iya goyama Sadiq baya akan wannan Shirmen nasa.
Suna nan tsaye sai ga Adda Fati da Habiba sun fito tun daga nesa ta ke kallon Sadiq wanda ya coge a tsaye duka Hannayensa suna cikin Aljihun wandonsa kansa kuma na kallon kasa bazaka iya Fahimtar a wani yanayi yake ciki ba.
Ita kanta mamakin bai gama Sakinta ba tunda yaran Baba Tanko suka shigo da labarin Daurin auran Hasiya bata tsinke da Lamarin Amma ba sai da Baba Tanko ya shigo shima ya ke fad'in Daurin auran da kanshi.
Har Adda Fati tayi subutan baka tace masa"Da wa aka daura ma Hasiya aure Baba.?
Kai tsaye ya kalleta kafin yace"Da wanda uwarku ta aiko ki da shi mana"
Daganan sai Adda Fati ta Fahimci Tsakiyar labarin da Karshe. Farkon ne yanzu kad'ai ya rage ta sani shi kuma Amma ke da Hakkin da zata fidda kowa acikin Duhu.
Sanda ta kariso wajen ta na so ta yi mgana ammh itama sai bakinta ya yi mata nauyi kawai sai ta Rausayar da kai ta na fadin"Mu je ko?
Ta yi gaba Sadiq ya taka ya bi bayan Habiba wacce sai ta juyo ta kallesa ta koma kuma ta kalli gabanta ta kasa yi masa mgana shima kuma ya kasa ko sakar mata fuska yadda ya saba.
Tahir ne bai bi bayansu ba Sadiq ya juya ya na kallonsa kafin yace"Tahir.".
Tahir ya kallesa kai tsaye batare da ya taso ba, Ballatana kuma ya yi masa mgana.
Sadiq yasan daman haka zata faru zai Fuskancin Turjiya ta hannun Tahir. sai dai gwara Turjiyansa bayan Komai ya faru da Turjiyansa kafin hakan shine babban matsala tunda ya tabbata bazai taba barinsa ya cika wannan ladan na taimako ba.
Sai da yaje da kansa ya riko hannunsa Sannan ya biyosa. Suna tafe har bakin Titi Adda Fati ta sake tsaida musu abun hawa kamar na dazu suka sake shiga sai Samaru har kofar gidan su Hasiya.
Wannan karon da suka sauka Sadiq ya biya kudin adaidaitan.
Sun iske Ana ta loda kaya a budaddiyar motar da Isuhu ya kawo saura ma kad'an a gama. Sadiq ya manta da zencen ta shin su Amma shi kuma Tahir dariya ce ta kusa kamashi ya zata kayan auran Hasiyan ake lodawa sai ya kalli Sadiq ya na fad'in"Gusau za'a wuce da kayan auran ko Shinkafi?
Sadiq ya kallesa cikin mamaki shi kuma ya na dariya ya nuna masa motar kayan.
Sadiq ya yi tsam bai yi mgana ba Tahir kuma kai ya girgiza kafin yace"Na kasa gane abunda kuma muka sake dawowa nan muna yi a tsaye."
Sadiq dai bakinsa gum bai yi mgana ba Tahir sai k'ak'alan mgana ya ke Sadiq ya tankasa ya yi masa bore.
Adda Fati ko ta na shiga gidanmu matan gidammu suka yo mata caa fad'i suke yi ashe kuma an Daura Auran Hasiya? Cikin sakewa ta ke amsa musu da cewa Eh ko dai na munafunci ne suna ta fatan Alheri.
Ta na daga labulen dakin mu dukkanmu muna inda ta barmu labarin da muka samu baisa mun iya dagawa daga in da muke ba.
Amma ce dai ke ta zirga zirganta sai Inna Talatu da tare da ita aka rika fita da kaya ita da yara zuwa waje.
Amma na ganinta ta washe baki ta na fad'in"Fati ya aka yi ne?
Adda Fati tace"Amma su na waje"
Da Sauri Amma tace"To to..! Ni ta kallah kafin tace"Ramatu ku je dakin Maman boy ke da Hasiya. Zan kira ku daga baya."
Ina jin haka kamar Daman ina kan kaya ne na mike Zumbur dauke da Hanifa domin ba ni da idanuwan da zan iya kallon Assadiq a daidai wannan lokacin.
Dakin Maman Boy muka shige ni da Ramatu da dukkammu muka kasa yi ma juna mgana.
Ita dai sai kallona ta ke yi ta na mirmishi ta kasa mgana ni kuma sai tunani da ya cika min kaina a raina nake ji Amma ta so kanta in dai tunaninta ne wannan bai kamata saboda jin dad'in ka kai ka jefa rayuwar waani cikin wahala da ukuba hakan ba daidai ba ne.
Bamu san yaushe suka shigo ba an d'an juma sannan Adda Fati ta leko tace mu zo dakim Amma ni da Ramatu.
Daman da Hijabi a jikina tunda kayanmu gabadaya an had'a su waje d'aya sai dai nawa akwatin Amma ta hana a fita da shi ta na jin dadi tace kayana a bar su tukunna ba da ni zata tafi ba gidan mijina zan zauna in sha Allahu.
Hanifa ce ta tashi sai na ari zanin Maman Boy na goyata Ramatu kamar zatayi min mgana sai kuma ta fasa ammh ina ganinta ta na kunshe Dariyanta.
Itace gaba sannan ni ita kuma akaji sallamanta ni dai a saman lebena sallamar ta tsaya kuma har muka shiga na samu waje na zauna ban yarda na dago fuskata ba.
Kusa da Ramatu na rabuke kamar wata marainiya. A sace na kalli mutanen Dakin Adda Fati sai Adda Rukayya Hamma Isuhu da bansan yaushe ya shigo ba. sai Habiba da Inna Talatu ban kalli Barayin Assadiq ba ammh naga kamar ba shi kad'ai bane ne zaune akan Dauduma daga gefen Amma.
Muna zama Amma tayi gyaran murya kafin ta fara fad'in"Hasiya tun jiya ki ke tambayata me na Tattauna da Abubakar ko?
Sai alokacin na Dago kaina ina kallonta a jiyan ne zuwa da Safe na ke neman karin bayani ammh daga dazu zuwa yanzu ba na bukatar wani karin bayani.
Sai dai ban ce mata komai ba na maida kaina kasa ina wasa da yatsun hannayena acikin Hijabina.
Amma ta cigaba da fad'in"Bayan Hasiya ina so kowa anan ya zama Shaida kan mganata. Nasan zuciyarku na cike da Tunanin ta ya ya haka ya faru? mganar gaskiya ni ce na kira Abubakar da kaina na kuma kwance masa komai na labarin Rayuwarmu da Halin da Hasiya ta tsinci kanta aciki sannan ni ce nan na yi masa tayi auran Hasiya batare da Tunaninsa ko cewarsa ba."
Nasan kowa ya kalli Amma alokacin ban da ni saboda nasan daman za'a zo wajen ai tatsuniyar gizo daman bata wuce ta kok'i in ba Rokomsa ta yi ta ina Rayuwata ta dace da Rayuwarsa?
Sai dai na jira ta gama ne duk da ta na mahaifiyata bazan fasa gayamata gaskiya ba abunda ta yi son kai ne sannan ba ta yi daidai ba.
Ba wanda ya tambayeta dalilinta na aikata haka da kanta ta cigaba da fadin"Rauni irin na uwa ita ta sakani aikata haka. Hasiya yata ce na santa fiye da kowa acikin ku. Abubuwa da dama sun faru da ita a kananun Shekarunta wanda ba da son ranta ba ne ina son Hasiya ina kuma kaunar itama ta samu natsuwa da ingantattaciyar rayuwa a gidan auran ta kamar yadda yan'uwan ki suka samu, wannan Kwad'ayin yasa fara ganin Abubakar da Natsuwarsa da Hankalinsa yasa rauni irin na uwa batare da wani Tunani ba na yi masa tayi auran ki Hasiya."
Amma ta karishe fad'a muryanta ta fara rawa alamun kuka.
Sadiq ya dago ya na kallonta mganarta a jiya ta na dawo masa.
Ya tausayama Rayuwar Hasiya matuka duk da ya ji labarin a bakin Tahir sai dai shi ba yadda ya Dauka ba ne.
Yaji duniyar ta tsaya masa Lokacin da Amma ta durkusa a gabansa ta had'a Hannayenta waje d'aya ta na kuka ta na rokomsa da ya rufa mata asiri ya auri Hasiya.
Alokacin kallonta ya yi a tsorace kafin yace"Aure kuma Amma? Meyasa zaki ce na auri yarki Ahalin baki sanni ba bakisan komai a game da ni ba?
Amma ta bude baki cikin kuka ta na Fad'in"Bansan ka ba Abubakar ammh wlh tallahi naji lokaci d'aya ka shiga raina ina ji kuma ajikina bazaka taba cutar da Hasiya ba."
Sadiq ya dad'e ya na kallon Amma ajiyan ya na tunanin ita ko meyasa zata yi haka?
Cikin Sarkewar murya yace"Ba ni da kowa sannan ba ni da komai da me zan riketa? Sannan in dai a wajena ne ba zata samu kyakyawan rayuwar da ki ke mata fata ba, Saboda ni d'an makaranta ne ba ni da komai sannan ban mallaki komai ba Amma"
A lokacin Amma ta fad'i wasu maganganu da suka sanyaya masa jiki da su ne silar da suka saka ya amince ya taimaki uwar da ke bukatar taimakonsa indai yasan Darajan Mahaifiya.
Kafarsa ta kama ta rike lokaci d'aya ta na fad'in" _Ka ciyar da ita da abunda kaci Abubakar, Sannan ka Tunfatarta da ita da abunda ka tufatar da kanka, sannan ka ijiyeta a inda ka ke Rayuwa Ba rayuwar Kud'i ko dukiya Nake son Hasiya ta yi ba. a'a ina mata Fatan rayuwar natsuwa kwanciyar Hankali mai Dorewa har Abada._"
Ya na wannan Tunanin ita kuma Amma na warware musu yadda tattaunawarsu ta jiya ta kaya tsakaninta da Abubakar.
Tahir na kallonta ji ya ke kamar ya tashi ya fita domin gani ya ke kamar Tatsuniya ta ke faman maimaita musu sannan ji ya ke kamar ya bude baki ya gayamata Sadiq ba maraya ba ne da yasa ta yi wasa da rayuwarsa Abun alfaharin wani kyakyawan Ahali ne sannan dan gata ne da bai Chanchanci auran kaskanci kamar yadda ta cutar da shi wajen aura mata zabiyar bazawaran yar ta ba.
Amma ta share hawaye da Haban zaninta ta na fad'in"Ba na so na tafi da Hasiya garin mu saboda nan ne ta saba da shi fiye da ko'ina sannan zata fi sakewa in ta na ganin yan'uwanta a kusa da ita da wannan dalilin yasa na Roki Abubakar da ya aureki Hasiya sannan ki yi hakuri ban nemi jin ta bakin ki ba duk da addini ya baki wannan damar ni na yanke miki Sadakin ki da kaina nace ya bada Dubu talatin mun yafe komai Daga bangaransa.
Na tara ku ne ku zama shaida sannan na raba minti saboda Mutanen da ke zagaye damu suma su shaida hakan. Isuhu ma naji dadi da ya zama shaida wanda da ni da shi zamu iya gayama Adda abunda ya faru wanda bata sani ba ni zan bishi mu tafi na bar Hasiya Hannun mijinta Abubakar da na ke da yakinin zai rike min ita bisa gaskiya da Amana. Sannan na barta hannun ku Inna talatu Ramatu Fati da Rukayya Hasiya ta ki ce Amanarta da kula da Rayuwarta duka suna Hannun Allah ne kuma suna hannunku. Ku kular min da ita don Allah tunda kuna gani Rayuwarta ba ta yi daidai da irin kyakyawan Rayuwar da ku ka samu ba."
Sai kawai Amma ta fashe da kuka wiwi. Adda Fati ma ta fara tayata Inna Talatu ne ta ke fad'in"Ki yi Shuru Aisha in sha Allahu kyakyawan Niyarki ta Alheri bazata tafi a banza ba. Hasiya kuma kada ki damu ki kaddara kina tare da ita in sha Allahu."
Amma ta gyad'a kai cikin muryan kuka ta kalli Sadiq da Tahir da kansu ke kasa kamar ba sa wajen tace"Abubakar ga Hasiya nan. Ka rike hannunta ka da ka saketa har abada. Ka zame mata bango wanda zai kareta ga duk wani abun k'i, ka zame mata tudun Dafawa Abubakar ka kare rayuwarta ga dukkan wani barazana. Nasan Hasiya bazaka taba samun matsala daga bangaranta ba zata zauna da kai ta yi hakuri da kai sannan zata yi maka biyayya har karfin iyawarta Allah ya baku zaman Lafiya tare da zuru'a mai albarka a Tsakanin ku."
Tahir a saman lebensa yace ba Ameen ba Sadiq kuma sai ya samu kansa da amsawa acikin ransa.
Inna talatu ta bude murya ta na amsawa da Ameen Ameen.
Amma Adda Fati ta kallah kafin tace"Kayan Hasiya na jere su na wuyan ki Fati na bar komai a hannunki."
Adda fati ta jinjina kai kafin tace"In sha Allahu Amma."
Adda Rukayya ta sake kallah kafin tace"Rukayya ke ce Babba. Ki rike girmanki ki ja yan'uwanki ajiki kada ki manta bayan su baki da yan'uwan da suka wuce su, Ki zama Alkaliya mai adalci a tsakanin kannen ki, ki yi hakuri da su don Allah bayan ba ni ke zaki cigaba da Bibiyan lamarin su. Sannan kada ku manta da Dangin babanku ku bisu ku yi zumumci da su ko da su baza su yi zumumci da ku ba hakki ne ku a kan ku ku yi zumunci da su."
Adda Rukayya kanta na kasa tace"In sha Allahu Amma"
Amma ta juya ta na kallon Ramatu Lokaci d'aya ta na fad'in"Ramatu ba sai nace miki komai ba. kinsan matsayinki a rayuwar Hasiya basai na yi miki wata mgana ba, nasan zaki yi komai domin ganin Farinciki a rayuwar Hasiya nagado miki sosai Allah ya saka miki da Alheri ya Dauwamar da zaman lafiya a tsakanin ki da mijinki."
Ramatu ta amsa da cewa"In sha Allahu Amma Ameen nima nagode."
Kowa sai da ya yi mgana a dakin nan ban da ni da kaina ke kasa ko motsin kirki ban yi ba.
Amma ta kalleni na wani Lokaci kafin ta kira sunana ina Dagowa ta ga hawaye suna bin kumatuna alamun kuka naci a zaunenan da na ke.
Cikin mirmishi Amma tace"Hasiya baki ce komai ba?
Ajiyar rai na Sauke kafin nace"Amma me zan ce? Kin riga kin yi abunda baki shawarce ni ba, gaddama ko saba Umarninki ba Halina ba ne ammh wannan karon na kasa yi miki biyayya. Na kasa jin auran nan a raina Amma na kasa."
Ba Amma kad'ai ba hatta Sadiq da Tahir a tare suka dago suna kallona.
Ni ko idanuwana na Runtse sai hawaye Sharr cikin kuka nace"Nasan rayuwata cike ta ke da tarin kaddarori ina cikin Tsaka mai wuya Amma, Kinsan na sani aure ba shi ne mafita a cikin Rayuwata ba.
Nayi auran nan na farko me na tsira da shi bayan saki da Tozarci? Ban karaya ba na sake yin wani auran shima me na Tsira da shi bayan Sakin wulakanci da Tozarcin da ya biyo baya Amma meyasa kuma zamu kara koma gurbin da muka san karshensa? Kin so ni kin yi son kai Amma kin jefa Rayuwar sa cikin Rayuwata Alhalinsa kinsan karshen hakan daidai ya ke da asaran dukiya da asaran lafiya da wani abunda wannan karon bamu san me zai Faru ba."
Na karishe fad'a cikin kuka Amma da Sauri ta mike ta na fad'in
"Hasiya.."
Cikin Daga murya nima na mike ina Daga mata hannu Lokaci d'aya ina Fad'in"A'a Amma. Wannan karon baki yi daidai ba. Kin so ni ki ki shi, Kuma Hadisi ne kyakyawa ka so ma Dan'uwanka abunda ka ke so ma kanka. Amma na riga nace na gama aure a duniyar nan indai ta sanadina Rayuka zasu rika baci suna shiga mawuyacin Hali wlh na Hakura na Hakura Amma."
Bansan lokacin da naji wani irin kuka ya fito daga kasan raina ba sai gani kawai suka yi na zube a kasa ina wani irin gunjin kuka domin kafafuna ne suka daina daukana da ya sa dole na bi zabinsu na zube a kasa.
Kuka na ya tada Hanifa da ke bayana da Sauri Adda Rukayya ta yaye hijabina ta saukota duk ta had'a zufa. Kokarin kamani su ke in tashi naki Amma sai ta fashe da kuka ta kasa mgana.
Cikin kukan na d'ago muka Had'a ido da Assadiq.
da rarrafe na karisa gabansa cikin fitan hayyaci nace"Ka yi ma girman Allah ka sakeni ASSADIQ. ka da ka kara minti d'aya da aure ne a tare da kai ka tsira da rayuwarka don Allah. Ka gani bazan damu ba, Salisu ma ranar da aka daura ma aure ya sakeni ammh duk da haka bai Tsira ba yana nan yana jinya Abubakar ma sai da komai na shi ya kare sai da komai na mahaifinshi ya kare duk saboda Dalilina ka sakeni ni ba kamar sauran matan da zasu samu kwanciyar Hankali ta sanadin aure ba ne ni Hasiya na yarda Annoba ce sannan gobarace ni duk inda na shiga sai naci Dukiya ko na taba lafiya."
Na karishe fad'a ina wani irin kuka Amma ta dakamin Tsawa lokaci d'aya ta na fad'in"Hasiya lafiyan ki kalau kuwa?
Cikin kukan na cigaba da fadin"Amma me yasa kika yi min haka batare da sanina ba? Kina so ki dauwama kina ganina cikin kunci ? To wannan auran ne zai sakani cikin kuka kamar yadda sauran suka zo suka kare haka shima wannan zai kare kamar ba'a yi ba."
Wannan karon Adda Fati ce ta zo ta kamani ta na fad'in"Hasiya wani irin mganace wannan?
Ta ke fad'a itama kamar ta