Showing 51001 words to 54000 words out of 122381 words

Chapter 18 - Daudar Gora Book 1 Hausa Novel Complete

25 Dec 2024

406

“Ito baba banace ba, dan kusan nima hakan dai take, amma bayan tashinsa daga anguwarmu nasan inda ya koma, sai dai bani da tabbacin ko har yanzu acan ɗin yake zaune tunda ba wani huɗɗa muke ba gaskiya, dama dalilin Abu Hanash ɗinne ake gaisawa sai kuma idan wani zama na anguwa ya haɗa kafin ya tashi kenan. Amma yanzu dai bara mu tafi can ɗin kawai rana ma nayi”.

Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso anguwar, kasancewar ma ta cika ba kamar da ba da kyar suka iya samo gidan. Duk da jikinsu ya ɗanyi sanyi ganin ƙofar gidan babu alamar anyi wani abu daya shafi mutuwa Abu Zainab yay sallama har sau uku. Ana huɗun wani mutum ya fito. Cikin binsu da kallon rashin sani ya basu hannu suka gaisa. Abu Zainab da shima dai jikinsa yay sanyi ya ce, “Kayi haƙuri nasan baka sammu ba. Muma dai munzo nan ɗinne neman wani bawan ALLAH daya zauna anan shekara kusan huɗu haka baya. Sunansa Dawood, amma ana masa alkunya da Abu Moosa. Matarsa ɗaya bashi kuma da yaro ko ɗaya”.
“ALLAH sarki, gaskiya ban sanshi ba, dan nima dai ban wuce shekara biyu da tarewa anan ɗin ba. Na kuma sayi gidanne a hanun wani mutum Ibrahim Askari”.
Abu Zainab zai sake magana Kaka ya girgiza masa kai alamar kar yace komai. Godiya sukai masa da sallama suka wuce.

“Baba ban san miyasa ka dakatar dani ba. Dama zan tambayesa ne ko zai faɗa mana inda zamu samu shi Ibrahim Askari ɗinne”.
Numfashi Kaka yaja ya fesar, “Dalilin da yasa na dakatar da kai kenan. Kasan shi al'amari irin wannan yana buƙatar kasan dawa zakai maganar abu na gaba. Inaji a jikina waɗanda suka haddasa tushen wannan matsalar dole suma zasu kasance suna bin bayanmu domin toshe duk wata hanyar da zamu iya bi. Dalili kuwa shine ina kallon lauje ne cikin naɗi akan al'amarin”.
“Eh gaskiya hakane kuma Baba. To amma in har hakane mizai hana mu nema lauya, sai nake ganin cikin sauƙi shi zai iya binciko mana inda suke ma, kuma koma minene sai yazo cikin sauƙi tunda ana magana ne akan abinda ya shafi shari'a ko kuwa?”.
“Itama wannan babbar shawara ce a mahangar hankali Zakariyya, sai dai shi lauyan ne matsala musanma irin mu wanda muke bukata. Mai gaskiya da amana”.
“In dai dan wannan ne babu damuwa insha ALLAHU, akwai yayan matata data rasu, kwararren lauyane kuma mai nagarta da nasan zakaso aikinsa kuma zai taimakemu kasancewarsa babba. A yanzu dai nasan bazamu samesa a gidansa ba. Bara kawai muje ofishinsa”...

★★..... ★... ★★.....

Kamar yanda Iffan ta nema alfarma a wajen Daneen Ammarah akan ɗakko mata akwatinta da aka kawo ta gidan dashi ya iso gareta. Taji matuƙar sanyi a ranta da farin ciki. Hadimar data kawo na fita ta buɗe akwatin ta shiga dubawa. Alhamdullah komai yana nan yanda yake, hatta takardar da malam Fawzan ya bata ɗinnan itama tana a inda ta ɓoye ta. Tana idar da sallar azhar littafin data sako a kayan nata kawai ta ɗauka da biro ta fara rubutu. Anutse take rubuta komai daya faru daki-daki tun daga barowarta gida har zuwa shigowarta cikin masarautar, abinda ya faru da ita dama wanda ke kan faruwa bayan warkewarta. Da zarar taji motsi koda ma Daneen Ammarah ne sai ta boye, a haka ta kwashe kaf yinin har zuwa dare tana abu ɗaya. Da daddare bayan kammala shirin barci maimakon kwanciya zaman karatun Alkur'ani tayi, koda Daneen Ammarah ta shigo ta sameta a hakan bata katseta ba. Tasa Hadimar dake biye da ita ajiye mata madarar da suka shigo da ita. Daga haka ta fice taja mata ƙofar da nufin ta dawo zuwa anjima, dan yanzu tana son zuwa ta duba Malikat Haseena ne da yai batajin daɗi.
Iffah na ganin ta fice ta sauke ajiyar zuciya, addu'a tai ta rufe Alkur'anin ta mike, kofar taje ta sanyama key bayan ta leƙa babu kowa a corridor ɗin. Ta ɗan jingina da ƙofar tana mai ambaton “Alhamdullah” da sakin ɓoyayyen murmushi. Cikin sassarfa tabar jikin ƙofar zuwa ga akwatinta, ta buɗe tare da ɗakko wayar Arfa da takardar da Malam Fawzan ya bata. Number da aka rubuta ta kwashe a wayar, ta haye tsakkiyar gadon ta kwanta tare da jan lallausan bargon ta shige ciki har kanta sannan tai dailing number. Gaba ɗaya a kage take da zumuɗin a ɗauka. Dan haka take bin sautin shigar kiran da zuciyarta. Sai dai harta yanke ba'a ɗaga ɗin ba. Kira ta sake yi, nan ma dai shiru, bata gajiya ba ta cigaba da kira har fin sau goma kafin a ɗaga a karo kusan na goma sha biyar. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tamkar wadda aka tsamo daga cikin ƙanƙara. Sai kuma tai saurin faɗin, “Assalamu alaikum”.
“Wa'ake nema?”.
Aka faɗa daga can maimakon amsa sallamar tata. Da lafiya lafiya ne sai tayi mitar ƙin amsa sallamar, amma sai tai saurin faɗin, “Sir Ajmaal”.
“Wa'ake nema?”.
Aka sake maimaita mata tambayar.
Zuciyarta ta ɗan fara zabura amma sai ta danne ta sake maimaitawa itama.
“Sir Ajmaal”.
“Wa'ake nema?”.
Still aka sake faɗa kamar dai ba'ama jita ba.
Wayar ta janye a kunenta ta tashi zaune ta ɗauka takardar, number dai dake a jikice dai-dai batai mistake ba. Sake maida wayar tai kunne aranta tana faɗin (bara naga ƙarshen ku dai) ta sake amsawa da “Sir Ajmaal”.
“Kin saɓa lamba”.
Aka bata amsa da yanke wayar lokaci guda batare da anjira cewar ta ba......


★★..... ★... ★★.....

Kasancewar Abu Zainab suruki ga barrister cikin sauƙi suka samu ganinsa ta hanyar kiran waya. Har office yasa masinjansa daya fita yay musu iso ya shiga da su. Ganin lafiyayyen office ɗin nasa dama hukumar tasu ya sake tabbatar ma da Kaka babbane gaskiya. Sun gaisa cikin nuna sanayya shi da Abu Zainab. Ya kuma gaida Kaka da girmamawa kasancewar tsoho dama zai iya haifarsa. Basu saurari lemo da aka kawo musu ba Abu Zainab ya shiga masa bayani dalla-dalla. Sai da ya gama tsaf Barrister Abdallah dake rubuta wa ya ajiye biron yana jinjina kansa. Kaka ya fuskanta cikin son ƙarin bayani....
“Baba kaima kasan shi Dawood ɗin kenan?”.
“Tabbas na sanshi yaro. Hasalima ga gidan mahaifin shi Muhammad Zayyanu gana mahaifin Dawood. Sannan ta ɓangaren mahaifiyata ma munada alaƙar jini da mahaifin nasa. Shine kuma yay sanadin zuwan Muhammad Zayyanu garin nan, shi kuma Muhammad Zayyanu ya koya masa noman zuma daya gada ga mahaifinsa”.
“Eh lallai sanayya ce babba kam. Sai dai kuma inaga ya kamata nasan miya rabasu? Dan yanzu hujjojin hanunmu sune zasu taimaka mana wajen kubutar da su saboda wannan case ne babba kuma da alama shiryayye”
“To nidai kai tsaye banace ga abinda ya zama sanadin rabuwar kawunan nasu ba. Dan shi Muhammad Zayyanu mutum ne mai zurfin ciki da rashin kwaramniya. Amma dai lokacin da naga bana ganinsu tare na tambayesa ko akwai matsala? Shi da abokin nasa. Sai ya sanar min shi dai a saninsa bai masa komai ba ya janye daga jikinsa, ya kuma bisa ya bisa babu adadi danya faɗa masa amma yaƙi, daga karshe ma ya tattare kayansa da iyalinsa sukabar anguwar, bai kuma sake ganinsa ba har watanni sunja a lokacin. Na bashi shawarar ya ƙara nemansa dai, da muka sake haɗuwa na tambayesa sai yace ai yama bincika yabar gari. Iyakar abinda na sani kenan gaskiya”.
“Shi kuma Dawood ɗin baka sake ganinsa ba kaima?”.
“Eh to gaskiya ban sake ganinsa ba. Dan ko'a rasuwar mahaifinsa sai wai-wai mukaji yazo yay gaisuwa ya tafi kawai. Daga nan kuma dai bamu sake jin ɗuriyar tasa ba dan dama mahaifiyarsa bata raye tuni”.
Barrister dake faman kaɗa kai ya sake ajiye bironsa. “Uhhm yanzu to inaga mataki na biyu shine musan wane station suke. Ko kuma inda ita matar tasa take”.
Cikin damuwa Abu Zainab yace, “Munje inda muke tunanin samun nata bamu sameta ba. Sai dai an ambata mana sunan wanda ya saida gidan ga wanda ke ciki yanzu”.
“Miye sunan”.
“Ibrahim Askari”.
“Badamuwa kuje abunku, insha ALLAHU daga nan zuwa gobe za'a nema mana Ibrahim Askari ɗin. Suma kuma zan ɗan bincika ta hanyar jami'an dana sani a mabanbanta station na garin nan”.
Sosai kaka ya dinga ma barrister godiya. Hakama Abu Zainab. Shi dai faɗa musu yake karsu damu. Aje a cigaba da addu'a komai zai zama labari insha ALLAHU......

★★..... ★★.... ★★.....

Iffah kamar zatai kuka ta ƙara dailing number amma sai ma aka sanar mata switch up. Wani irin zafi da lugude ƙirjinta ya shiga yi, ta shiga neman number Malam Fawzan cikin rawar jiki tunda dai shine ya bata number..........✍️



*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 90165991

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻


*_23_*


........Itama ɗin dai switch up. Wasu zafafan hawaye suka silalo a kumatun ta. Ƙoƙarin sake kiran waccan number ta gwadayi knoking ƙofar da akai ya katseta. Da sauri ta yanke kiran da kashe wayar ma baki ɗaya ta ɗaga gadon ta tusasu har da takardar gaba ɗaya sannan ta sauka dan tasan bazai wuce Daneen Ammarah ba...
“Ibnati baki barci ba kenan?”.
Kan Iffah a ƙasa tai ɗan murmushi. “Yanzu zanyi Mamy karatu na kammala”.
“Masha ALLAH, ya kamata ki kwanta to dare yaja, nima zuwa zanje na kwanta”.
“To Mamy ALLAH ya tashemu lafiya”.
Koda Daneen Ammarah ta wuce Iffah ba kwanciyar tai ba, sake ɗakko wayar tayi ta cigaba da neman wancan layin da a yanzu ake cemata not available saɓanin switch up na ɗazun. Hakama number Malam Fawzan har yanzun. Daga ƙarshe dai barci ɓarawo gwanin iya sata ne ya saceta akan dole ta haƙura, sai da asuba ta tsinta wayar a ƙasa yashe....

Yau dai kam ta ƙudiri niyyar fita gaida tsohuwa Malikat Haseena da kanta, tunda dai jikinta Alhamdullah hatta saɓar ma sai inda ba'a rasa bane bai gama ba. Bayan hadimar dake gyara ɗakin ta kammala ta fita key ta sama ƙofar sannan ta shiga wanka. Dan duk da tausayin hadiman da takeji a yanzu batajin zata sake yarda da waninsu. Ta fito tana tsaka da shiryawa cikin ɗaya daga kayanta na gida akai knoking. Karasa saka abayar tayi sannan taje ta buɗe, a tare suka sakarma juna murmushi, tai ƙasa da kanta tana faɗin, “Barka da safiya Mamy”.
Daneen Ammarah takai hannu ta taɓa kanta da faɗin, “Kin tashi lafiya?”.
“Alhamdullah”.
“Haka ake so. Ga kayanki nan na amfanin yau, mun zaɓi yin hakane saboda gudun abinda zai iya zuwa ya dawo Ibnati, amma insha ALLAH kayanki na amfani na gab da kammaluwa, saiki shirya ni zanje sashen Umm Jasrah. Ki tabbatar kinci abinci sosai yanzu zan dawo ba jimawa zanyi ba”.
“Adawo lafiya Mamy a gaisheta”.
“Zataji, amma ki tabbatar kin canja waɗan nan kayan”.
Kai kawai Iffah ta jinjina mata. Amma a ranta tana mamakin minene aibun abayar tata? Tana cikin sabbin kayantama da take matuƙar ji da su. Shigowar hadimai biyu da kayayyaki ya katse mata mitar tata, sai dai batace komai ba bayan amsa musu gaisuwa. Fita ɗayar tai aka barta da wadda tafi yawan kasancewa da ita, tazo gabanta ta zube kanta a rissine. “Ya Zawjata-almilki bisa umarninki za'a shirya kayan”.
Karo na biyu Iffah ta amsa neman izini da umarni ga hadimai a gidan. “Ba yanzu ba, zaki mun rakkiya ga Mamma ne, ki jirani a waje”.
“Umarninki shi nake zaman jira ya Zawjata-almilki”.
Hadimar na fita ta taka inda kayan suke tana dubawa. Tunda ta samu lafiya kullum da safe za'a kawo mata kaya kala uku, washe gari za'a kwashesu koda daya kawai ta saka a sake ajiye mata wasu. Da farko ta ɗauka ko haka tsarin masarautar yake. Sai a yau bayanin Daneen Ammarah yasa ta fahimci ita akema hakan saboda tsaro. Waɗanda ranta yafi kwantawa da su ta dauka ta saka. Ta koyi ƙyau sosai musamman da suka kasance bakake da adon stones masu sheƙi da ɗaukar idanu. Ga farar fatarta data koma ja ƙaɗan saboda saɓar datai tamkar ta larabawa ta sake fitowa. Ɓoyayyun turarenta na wajen Kaka ta ɗakko ta saka, wani irin ƙamshi mai daɗi da saka zuciya nutsuwa ya fara ratsa ɗakin...

Sosai murmushi ya bayyana a fuskar tsohuwa Malikat Haseena saboda ganin Iffah akan kafafunta, takuma ji daɗin wannan ziyarar bazata data kawo mata duk da kuwa suna a sashe ɗaya ne. Iffah data kai zaune gefenta bisa tattausar dardumar da aka ƙawata falon da shi ta risinar da kai tana gaisheta da tambayarta yaya jiki?.
“Alhamdullahi ƴar albarka. Yaya naki jikin?”. Malikat Haseena ta amsa da kulawa har yanzu murmushi ƙawace da fuskarta.
“Naji sauƙi ai Mamma” (kamar yanda taji Daneen Ammarah na kiranta.
“To Alhamdullah ALLAH ya ƙara kiyaye gaba”.
Da amin duk hadiman wajen suka amsa. Malikat Haseena sallamar duk Hadiman tayi, tare da bada umarnin a shirya mata breakfast da Iffah. Hakan ya bama hadiman mamaki sosai, dan duk wanda Malikat Haseena zata buƙaci zaman cin abinci da shi ba karamin mai sa'a bane ba. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa aka kammala shirya komai, ita dai Iffah na kallon ikon ALLAH da tsagwaron mulki wajen wannan tsohuwa. A ranta kam tunani take shin wai idan haka matan suke waishi babban dodon nasu yaya za'a gansa kenan?. Bisa umarnin Malikat Haseena Iffah ta mike suka nufi wajen da aka shirya abincin. Zamansu dai-dai da shigowar amintacciyar hadimar Malikat ɗin ɗauke da wani ƙaramin kwano...
Shigar ƙamshin turaren Iffah hancin Hadima Banou ya saka jikinta fara tsuma. Hanunta na ɗan rawa ta sunkiya zata ajiye kwanon suka haɗa ido da Iffah. Zabura tayi da sauri ta miƙe kanta a sunkuye. Iffah ma dake jin jikinta na wani irin yamutsawa ta sake kallonta da kyau, haka kawai matar batai mata ba, gata wata irin doguwar mace gandaƙaiƙai kamar namiji babu wani fasalin mata tattare da ita... Malikat Haseena da rawar jikin Hadimar ya bata mamaki itama ta tsura mata idanu. Sai dai mulki da kasaita baisa ta tanka ba. Hadima Banou dake jin kamar ta zura a guje saboda yanda take jin jikinta ta zube ƙasa, cikin rawar hannu ta fara yunƙurin haɗama Malikat Haseena abinci.. Iffah dake mata kallon nazari ta dakatar da ita. “Kinga jeki kawai”.
Ai kafin ma ta rufe baki tuni ta mike zaram kamar wadda ke akan wuta. Iffah da gaba ɗaya abin ya gama ɗaure kanta ta fara haɗama Malikat Haseena abincin da kanta. Itako Malikat Haseena komai bata kawo a ranta ba game da yanayin Amintacciyar hadimar tata, saboda takan ganta a wasu yanayi daya fima hakan, dan haka ta jima da sakata a jerin masu aljanu...

Hadima Banou na fita a falon ta sauke wani irin nannauyar ajiyar zuciya da kai hannu ta yarce gumin dayay sharkaf a goshinta kamar wadda ta tiƙi surfen gero. Gaba ɗaya manyan idanunta masu saka tsigar jikin mutane tashi sunyi jazur. Gefe ta koma ta zauna a ranta tana fatan ALLAH yasa har Iffah ta tafi Malikat Haseena bazata nemeta ba. A ganinta ma tai zamanta anan koda an nemetan ai sai an ganta. Wannan shawarar data yankema ranta ya sata cigaba da zama a wajen har lokacin jikinta bai gama komawa dai-dai ba....

Gaba ɗaya Iffah kasa sakewa taci abincin tai saboda kunya, ganin haka cikin hikima Malikat Haseena ta cigaba da ɗan jan ta da hira domin jan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login