Showing 15001 words to 18000 words out of 122381 words

Chapter 6 - Daudar Gora Book 1 Hausa Novel Complete

25 Dec 2024

394

salla. Komi take aka kira salla, ko'a ina take inhar wajen zaiyi ibada zata ajiye abinda takeyi kuwa tayi sallar. Wannan halin nata na ƙara sakama iyayenta da ƴan uwanta sonta, dan tunsu Arfa na raye ma sukansu Ummu takan zaburar dasu akan halin Iffah ɗin na kiyaye ibada da ƙoƙarin yinta akan lokaci. Koda ta shiga ɗakin bayan tayi alwala bakin gadonsu takai zaune dan tana fashin salla ne, sai da taji tsakar gidan yayi tsitt sannan ta ɗan leƙo, babu kowa kuwa Ummu ta shige su Hanash sun fita massallaci. Da sanɗa ta fito ledar maganinta na ɗazu da taketa ɓoyo riƙe a hanunta. Wuff ta afka ɗakin Babiy, cikin sa'a bata wani sha wahalar ganin tulunan da aka cika da zuma ba sabbi ƙal. Ta saki murmushi dajin kamar tai ihu dan farin cikin da takeji a zuciyarta. Amma sai ta kanne cikin rawar jiki da ɗan yin leƙe-leƙe irin na mai tsoron a kamasa yana laifi tana ƙoƙarin buɗe kwalbar. A tulun farko ta zuba kusan rabi, sai kuma ta dakata bisa shawarar zuciyarta akan ta zuba duka tunda bata da tabbacin dukansu Tajwar ɗinne zaiyi amfani da su. Ƙaramin sandan data shigo da shi tasa ta motsa da ƙyau har saida ta tabbatar ya gauraye sannan ta sakama ɗaya, tana tsaka da juyawa ta tsinkayo muryar Ummu na kiranta. Ido ta rumtse da sauri tana ambatar sunan ALLAH, da hanzari ta shiga rufe roban sauran maganin saboda jin kamar Ummu na nufi ɗakin, cikin riga ta saƙa maganin da sandar sannan taɗan leƙo. Can ta hango Ummu ta nufi kitchen ɗinsu, aiko tai wuff ta fito ta faɗa ɗakinsu. Ummu data juyo saboda jin kamar motsi ta sake ƙwala mata kira. Yanzu kam amsawa tai da fitowa tana gyara mayafin abayarta.
“Yi haƙuri Ummu ina karatune”.
“Shine kuma bazaki mun ko gyaran murya ba zaki barni ina wage baki”.
“Kiyi haƙuri to Ummuna”.
Ummu ta fito daga kitchen ɗin tana gyara mayafin jikinta itama. “Jeki ki cigaba da karatunki dama motsi naji kamar, amma fara duba kosu Hanash sun bar mana ƙofa buɗe ne”.
Da to Iffah ta amsa tana nufar hanyar soro da sauke ajiyar zuciya...

Tana shiga ɗaki wani uban tsalle tai ta dirga saman gadonsu dan farin ciki. Mulmula take tana dariya irin wadda ta jima batayi ba, wauta da ƙuruciyarta tafi hango mata nasararta na ɗaukar fansar ƴan uwanta fiye da tunanin idan wani abu ya faru Babiy ne na farkon wanda za'a tuhuma kasancewar zumar daga hanunsa ta fito. Haka Iffah ta ƙarasa wannan dare cike da zumiɗin ganin wayewar gari Babiy ya kai zuma masarauta.
Bayan ta idar da salla yau ko fama da ita Ummu batai ba akan shirin tafiya makaranta, a da kuwa saita tasota daƙyar kasancewarta mai son barcin safen tsiya da tayi salla take komawa barci. Babiy kansa saida yay mamakin wannan sammakon tashi nata yau, Hanash kam kasa haƙuri yay saida yay magana. Sai cewa tai ai sunada program ne a makaranta yau... Koda taje makaramtar ma dai bawai ta nutsu bane, rabin hankalinta ne kawai ga duk malamin daya kasance da su har aka tashi.

★A ɓangaren Babiy kam duk da tabon da masarauta daular ruman ta bar masa a zuciya bai taɓaji koda wani zai bari ya cutar da su ta hanyarsa ba ko shi ya aikata hakan ta damar dake hanunsa na kai musu zuma. Tsaf yay shirinsa kasancewar yau juma'a ce ya ɗiba tulunan zumar nan guda uku ya nufi daular ruman. Idan yaje ba kaitsaye yake ɗaukar zumar nan ya kai ga Tajwar ba, dan ganin Tajwar kam babban abune da sai wanda ya cika ya tumbatsa keda wannan damar. Akwai wanda keda alhakin amsarta shi ya isar da ita inda ya dace har ta isa ga sashen Tajwar ɗin. Bayan ƴan bincike a kansa na kullum da basa ƙarewa ya shiga daular ruman iya ƙofa ta biyu. Dattijo da kamanni da suturar jikinsa kawai ta isa tabbatar maka da shima wanine ya iso ga Babiy bayan zaman jiran kusan mintuna goma da yayi. Cikin girmamawa Babiy ya gaidashi duk da zasu iya zama kusan sa'anni da shi. Shiko ya amsa yana hura hanci irin na masu dama ta mulki a hannu. Umarni ya bama Babiy akan ya ɗanɗana zumar, Babiy da yasan babu wani abu na razani ko shiga dogon tunani kafin ɗanɗanawar kansa tsaye ya kai hannu ya ɗauka cokali dake bisa tire a hanun hadimin dake biye da dattijon nan. Tunda dama haka ba sabon abu bane garesa duk sanda ya kawo sai ya ɗanɗana ɗin. Tulun farko ya kwancema baki kasancewar a ɗaure bakin yake da ganyen ayaba, yasa cokalin nan ya ɗibo zumar da bismillah ya nufi bakinsa.........✍

*_😬😬😬Iffahhhhhh!!!!🙆🏻._*


*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+2290165991

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻


*_7_*


.........Haniniya da ƙarar takun sawayen wani farin ingarman doki ta saka Babiy sakin cokalin da yake shirin kaiwa bakinsa ya miƙe domin ceton kansa kamar yanda Dattijo nan da hadiman dake tare da su suma sukai nasu waje. Tuni tulunan zumar uku da Babiy ya kawo sukai nasu gefe suma, gaba ɗaya zumar ta kelaye a wajen. Cikin daka tsawa dattijon nan ke duban hadiman da suka biyo dokin domin kama shi...
“Wane mara hankalinne yay sakacin daya kunce?”.
Su dukansu jikunnansu rawa yake, cikin ƙarfin hali shugaban hadiman dake kula da barga ya zube ƙasa yana mai girgiza kansa. “ALLAH ya ƙara maka tsahon rai an gama masa wankane za'a maidashi na rantse maka”. Dattijon ya cije baki mai nuna alamar takaici, “Na baku mintuna goma kacal ku madashi shashashu kawai”. Miƙewa hadimin dattijon yayi cike da girmamwa dan dama sauran sunata ƙoƙarin ganin sun kama dokin ne, bama su kaɗai ba hadiman da yawa sun ƙaru saboda bahagon dokine da babu ma iya controling nashi sai Tajwar Eshaan. Horarran doki ne daga horonsa, da abinsa ya dawo ƙasar ruman, dokin yafi kowanne doki tsananin ƙarfi a masarautar. Shiyyasa idan har sukai sakaci ya ɓalle kowa sai ya jigata kafin a kamashi da ƙyar, kafinma kamashin sai an samu wanda sukaji raunika da yawa. Akwai randa irin haka ta taɓa faruwa baƙaramin jigata mutane yay ba harda masu karaya a hadimai, kuma duk iya wahala da jigata babu wanda ya iya kama dokin har duhun magriba yayi dan da yamma al'amarin ya faru. Kowa yayi laushi an rasa in za'a kama sai ga Tajwar Eshaan ya fito sallar magrib, abu mafi ban mamaki daya saka masarautar yin shiru na sakanni uku kiran sunan dokin kawai yay sai gashi gabansa, ya girgiza jikinsa tare da yin haniniya sannan ya koma kan ƙafafunsa ya tsaya cak tamkar bashiketa jigata mutane da hargitsa wajen ba. Wannan abun mamaki ya saka dukan hadiman da suka zube saman gwiyawunsu kawunansu a ƙasa a lokacin kasa haƙuri sai da suka saci kallon dokin dama Tajwar Eshan ɗin da hirami daya yafa a kansa ya rufe rabin fuskarsa.....

★★★★

A ɓangaren Iffah gaba ɗaya idanunta sun kasa barin ƙofa, babban burinta kawai dawowar Babiy taji zuma ta isa hanun Shahanshan. Sai dai shiru kakeji har akai sallar juma'a bai shigoba. Ko abinci babu yanda Ummu batai da ita tai zaman ci ba amma taƙi, Hanash ma sai da ya mata maganar tazo suci kamar yanda sukanyi duk juma'a tunma su Fariha nada rai amma tace batajin yunwa. Ƙyaleta sukai dan sun kasa gane minene ya hanata nutsuwa waje ɗaya.
Babiy bai shigo gida ba sai bayan sallar la'asar. Azabure Ummu ta miƙe tana kallonsa. “Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un. Abu Hanash haɗari kayi?”.
Kai Babiy ya girgiza mata yana kaiwa zaune da ƙyar. “Ke dai bani ruwa na fara sha”.
Kafinma ya rufe baki Iffah da itama jikinta ke rawa ta kawo masa ruwan, dai-dai nan Hanash ya fito daga ɗakinsa cikin shirin fita ƙwallo. Shima a ruɗe yay kan Babiy ɗin yana jera masa tambaya. Babiy ya ajiye kofin ruwan yana mai kallonsu gaba ɗaya. “Kunga ku kwantar da hankalinku babu abinda ya faru daga masarauta ne. Wani bahagon dokine fa ya kunce al'amarin tamkar yaƙi, hatta da zumar dana kai ba'a mora komai a cikinta ba ma”.
Ummu da Hanash suka shiga jera salati, yayinda Iffah taji wani ƙududun baƙin ciki ya tokare mata maƙoshi, hakan na nufin bataci nasara ba sai ma Babiy daya dawo da raunika. Jitake kamar taga Tajwar Eshaan gabanta ta shaƙesa da hannayenta har sai ya bar duniya saboda tsabar tsanarsa. Har Hanash ya gama yima Babiy dressing ciwukan batace komai ba, daga ƙarshe ma ɗaki ta shige ta shiga faman kaikawo na tunanin abu na gaba. Dan tayi alƙawarin bazata taɓ haƙuraba sai ta kai *_Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed_* ƙasa zata samu salama game da rasa ƴan uwanta.

Sam a wannan dare Iffah bata wani isashen barci ba saboda ƙullawa da kwancewa aka shiri na gaba. Abinda ta gama ƙullama zuciyarta yasata shirin fita a gidan da hantsi da dalilin cewar zataje wajen Ikram duba mamanta bata da lafiya bazata jima ba. Ummu tayi kamar bazata barta ba amma taita mata magiya harta amince da sharaɗin karta jima, kuma dolene ta rufe duk jikinta. Ta yarda da hakan saboda tana son fitar. A gurguje tai shirin fitar, tare da lalubo wayar Arfa a cikin kayansu. Koda ta haɗa batteryn ta kunna tayi sa'a tanada caji, dan haka ta loda number da take buƙatar kira tana mai addu'ar ALLAH yasa akwai kuɗi ma. Addu'ar tata bata amsu ba, dan haka ta tura wayar cikin jikinta bayan ta kashe sannan ta fito tai sallama da Ummu ta fita bayan ta amsa kuɗin taxi. Sai da ta fito daga cikin anguwarsu gaba ɗaya sannan ta tsaya ta sai kati, koda ta loda sai ta sake gwada kiran lambar ɗazun. Cikin sa'a kuwa aka ɗauka, jimm sukai su duka kafin ta katse shirun da sallama. Daga can aka amsa a noƙe alamar rashin sanin dawa ake tare. Fahimtar hakan ta saka Iffah bashi amsa tunkan yay tambayar.
“Sir! Kana magana da Fareedah bint Zayy......”
“Serious?”.
Ya faɗa cikin katseta da alamar zabura tun kan ta ƙarasa faɗa. Baki ta ƙyaɓe a ƙasan zuciya tana jan tsuka, a zahiri kam sai ta saki murmushin da har sautinsa ya kai cikin kunnensa. Cike da sake ƙanƙan da kai tace “Tabbaci Sir. Ina buƙatar muhaɗune yanzu yaya za'ayi?”.
“Kai! Iffah! Ke ɗin dai?...”
“Bazan samu damarba ko......?”
Cikin sauri ya katseta. “No ba nufina kenan ba, kawai na shiga al'ajab ne. Amma bara na ajiye tantamar tawa gefe dai. Inaga zanzo na sameki gida kawai...”
“A'a sir”.
“Miyasa?”.
“Ba buƙatar hakan, mu haɗu kawai”.
Jimm yayi na tunani, sai kuma ya sauke numfashi. “Okay! okay inaga bara na tura miki adireshin inda nake a yanzu haka sai mu haɗu nan in ba damuwa ko”.
“Ya dai kasance babu abinda zai shafi mutuncina a wajen sir”.
“Wannan shike ƙara samun naji ke ta daban ce Iffah”.
Baki ta sake ƙyabewa. Amsa garesa kuma tace “humm” kawai.



Kallon baki da hankali mai haɗi da tsoro tun daga ƙarƙashin zuciya yake mata tun bayan gama masa dogon jawabin da tayi. Tasan zataga fiye da hakan ga kowa bama shi kawai ba, dan haka bataji komai ba sai ma murmushi data sakar masa. Bata san mi yake tattaunawa da zuciyarsa ba, amma tanaji a ranta yana auna shekarunta da maganganun da kowa zai auna da wautarta ne kawai. Ilai kuwa sai ta tsinkayi muryarsa da irin amsar datai tunanin samu.
“Nikam Iffah shekarunki nawa?”.
“Ashirin a kwashe biyu sir”.
Ta faɗa tamkar bata fahimci alaƙar tambayar tasa ba. Kansa ya jinjina da cije lips nashi, kansa tsaye yace “Nama tunaninki mai kama da mafarki uziri. Amma zan baki shawara data dace da waɗanan shekarun naki na ƙuruciya. Ƙoƙarin ya kamata kiyi wajen cinye jarabawar share fagen shiga jami'a da ke tunkaroki kamar yanda nasan burinki. Tunaninki kuma ya zam tamkar baki taɓa yinsa ba, sannan na kasance na farko kuma na ƙarshe da kika faɗawa. Hakanne zai baki damar cigaba da ƙyaƙyƙyawar rayuwar da kika fara da ke da ahalinki har nima na cigaba da saka rasan samunki matsayin uwar ƴaƴana wata rana dan ALLAH Iffah”. Ya ƙare maganar da haɗe hannaye alamar roƙo.🙏🏻
“Ƙyaƙyƙyawar rayuwa ta daɗe da yankewa a cikin rayuwata data ahalina. kuma irinta nake hangowa da son daƙilewa ga ƴan baya ciki harda ƴaƴan da kaima a karan kanka zaka iya haifa wataran Sir. Sannan wannan tsoron da nake gani yanzu a cikin idanunka shine zai tabbatar da hakan, koda ni bana raye kai zaka rayu ka tuna. Nagode da saurarena da kayi sir”.
Da sauri yasha gabanta kasancewar ta riga ta miƙe. Tai takwaf-takwaf da fuska tana mai tsaresa da manyan idanunta da tuni hasken cikinsu ya koma launin ja. “Ki fahimceni Fareedah, koba komai na fiki shekaru, na fiki ilimin sanin rayuwa dama sirrikan dake zagaye da lungu da saƙo na ƙasar Ruman....”
“Na sani sir, tabbas na sani shiyyasa ma na fara nemanka. Sai dai nima kayi haƙuri, dan babu shawararka ɗaya data shiga cikin wannan kan nawa, saboda abinda ke cikinsa tamkar kundin littafin da aka rubuta labari daki-daki ne, kaga dole zaizo feji bayan feji. Kuma duk abinda ya shiga ciki bazai taɓa goguwa ba sai ta hanya ɗaya tak! Mutuwa!. Mutuwa ce kawai zata goge wannan yunƙurin insha ALLAH. Na barka lafiya”.
Sororo ya bita da kallo harta tare mototaxi ta shiga, ji yay ta ƙara masa girma a ido, girma bana shekaru kawai ba na wata ilhamar kwarjini da cikar mutuntaka. In har yara irinta da ayanzu suka fara rayuwa zasuyi irin wannan tunani akan al'ummarsu mi manya kakaninsa, iyayensa, yayunsa dama sa'aninsa sukeyi ne su? Shin basa ganin abinda take gani ne? Ko kuwa da gaske tsoron data ambata ta gani a cikin idanun nasane a idon kowa?. Kenan hatta da sauran sarakunan ƙasar da mafi yawan cikinsu sun rasa ƴaƴansu suma cikin tsoron suke? Anya maganar mutane ba tabbatacciya bace akan danganta Shahanshan na daular ruman da magajin fir'auna daya shuɗe batare da labarinsa ya gushe ba?. Iffah! Iffah!! Da gasken gaske ke tadabance kamar yanda nasha faɗa a aji aduk sanda kika bada amsar data danganci darasi......

★★★

Kwanaki uku kenan da Iffah ta tunkari malaminta batare da nasara ko ƙwarin gwiwa daga garesa ba. Sai dai hakan baisa taji ta sare ba ko haƙura da ƙudirinta. Koda ace nata ajalin take tunkara tayi alƙawarin sai tabi kadin jinin ƴan uwanta guda biyu. Koda ace bata da ƙarfin ikon ruguza mulkin sarkin dake kama da mulki irin na fir'auna zata tabbatar sai kuwwar gunjin kukanta ta fita a duniya, koba komai tanada yaƙinin a bayanta zata samu masu share mata hawaye insha ALLAHU.
Hanyar da tabi a farko ita kaɗaice hanyar da tasan tanada ita wajen bi ta samu nasara cikin sauƙi. Sai gashi kuma ba'a dace ba. Gashi tabi ta biyu itama, sai dai anƙi buɗemata ƙofar saboda tsoro da ƙarfin tasirin mulkin azzalumin, a yanzu haka tunaninta hanya ta uku koda itama bazata samu nasarar ba. Zata kuma cigaba da bin hanyoyin koda zasu ninka dubu sau dubu har sai ta dace. Nannauyan numfashin data zuƙa ta fesar, tare da gyara kwanciyata ta jawo wayar Arfa da har yanzu bata bari wani a gidansu yasan da tana amfani da ita ba. Ido sosai ta tsurama wayar, tabbas ba gizo bane tarin missed call ne daga malaminta. Taruwarsu da rashin jin sanda suka shigo wayar kuma nada nasaba da kasancewarta a silent. Tayi kamar zata share amma sai ta kasa hakan. Dan a yanzu shine kawai madubin da take kallo matsayin damar dake a hanunta ta isa ga abinda take so da wurwuri. Cikin sa'a tana kokarin kiransa sai ga kiran nasa ya sake shigowa. A dakile ta amsa tare da masa sallama murya a cuɗe.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login