Showing 66001 words to 69000 words out of 122381 words
Wannan tambaya tafi kowace tambaya girma da girgiza zuciyarta a duk abubuwan dake cin ranta. “Kai nifa nama ruɗe wlhy”.
Ta faɗa a zahiri tana zamewa cikin sarewa ta zube ƙasa. Ta jima a wajen cikin halin shiru da ambaton hasbinallahu wa ni'imal wakil ko zata samu dai-daiton komawa cikin hankali dan da gaske komai na halittarta mai motsi ya raunana da rauni mafi ban tsoro da shiga ruɗani. Tsahon lokaci ta kwashe a wajen tana kokawa da raunin zuciyarta da rashin ƙarfin gudanar jini. Fahimtar wancan tunanin na buƙatar lokaci ya sata turesa ta maida hankali akan tattaunawarsu da su Malikat. Tabbas wannan shine babban ƙudirinta dayin ƙundunbalar juriya na tunkarar rayuwar da bata da tabbacin tsallakewa. Duk da tasan anfi ƙarfinta, dama duk wani mai ƙarfi da take kallon ƙarfinta ta zaɓi fuskantar mutum mafi girman iko da tsaro domin ɗaukar fansa. A kwanakin da suka gabata na kasancewarta cikin wannan daula ta fara fidda ran samun cikar burinta saboda dalilai masu yawa. Ciki harda rashin samun koda ƙanƙanuwar ƙofar sanin minene ma daular ruman ɗin ta ƙunsa balle Shahan-shan da kansa. Sai gashi a yau cikin sauƙi an buƙaci kaita inda zuciyarta ta fara raya mata zuwansa ba ƙaramin tsalle bane da ba'a da tabbacin fita idan an shiga, aka kuma sanar mata wani yanki na sirrin daular ruman mai girman gaske da ko na ciki basu san da shi ba ƙila. “Anya babu wani abu a ran mutanen nan saɓanin abinda suka faɗa?” bakinta ya furta a zahiri cikin sake dulmiya a ruɗani. (Koda akwaisa yardar ki dasu ce zata baki ilimin sanin hakan) zuciyarta ta faɗa cikin ƙarfafata da ture raunin dake neman rinjayarta....
Knoking ƙofar daya wanzu a dai-dai lokacin ya sata jan numfashi a sauƙaƙe. Da ƙyar ta iya miƙewa daga zaman daɓaron da tayi ta buɗe. Daneen Ammarah ta sakar mata murmushi. Cikin yaƙe ta mayar mata da murtani da matsawa ta bata hanya. Rissinawa hadimar da suke tare tai ta gaisheta, hannu kawai ta ɗaga mata alamar amsawa tana bin ledar hanunta da kallo......
★★.... ★.... ★★.....
Kamar yanda aka sanar da Barrister kai tsaye station ɗin da akace su Babiy suke suka nufa. Kasancewarsa babba kuma sananne basusha wahalar ganin ogan station ɗin ba kai tsaye. Sunyi gaisuwa irin tasu ta manyan ma'aikata, su kai kuma gaisuwar girmama juna da su Kaka.
Barrister ya gabatar da kansa, ya kuma gabatar da abinda suke tafe da shi harda hoton su Babiy domin sauƙaƙawa. Jami'in yay shiru yana kallon hotunan kamar mai hasashe, sai kuma ya ɗago ya kalla Barrister “Gaskiya banajin akwai waɗan nan mutanen a wannan station ɗin Barrister”.
Barrister daya fahimci matsala ce ke neman shigowa yay ɗan murmushi da muskuta zamansa. “Yallaɓai adai sake dubawa, zata iya yuwuwa ko akwaisu ɗin baka da labarin hakan. Amma tabbas suna a wannan station ɗin. A matsayina na Barrister ba nazo nan dan a bani belinsu bane ba, duk da nasan basu da hannu a abinda ake zarginsu. Nazo ne dan na gana da su, sannan a miƙasu kotu saboda nasan dai ita matar data saka aka kawosu nan burinta a kwatar mata hakkin mijinta”.
“Iya gaskiyata nake faɗa maka Barrister babu waɗan nan mutanen a wannan station ɗin. Amma mizai hana ku sami ita matar na tabbata tunda tare da ita akaje tasan wane station ne”.
Barrister yay shiru yana kallonsa cike da nazari. Hakama Kaka da Abu Zainab. Kusan minti biyu shiru babu wanda ya motsa, kafin Barrister ya miƙe yana ɗan murmushi ya bashi hannu. Suma su Abu Zainab miƙewar sukai...
Da kallo ya bisu har suka gama ficewa, ya kai hannu kan wayarsa dake saman desk ɗin sa yana wani murmushi. A bugu biyu aka ɗauka wayar daya kira. Sallama kawai yay da faɗin, “Kamar yanda kai hasashe ranka ya daɗe yanzu suka bar office ɗina”.
Shiru yana sauraren mi'ake faɗa daga can, sai kuma yay murmushi da amsawa da “Angama ranka ya daɗe”. Daga haka ya ajiye wayar yana wata ƴar iskar dariya...
Abu Zainab daya kasa fahimtar komai saɓanin Kaka da Barrister dake hangen wani abu dalilin kashedi da akai musu kafin zuwansu nan dama ya katse shirun da motar ta ɗauka ta hanyar nisawa. “Anya kuwa wannan jami'in akwai gaskiya a maganarsa Barrister. Kagafa yanda yake ƙyaf-ƙyaf da idanu kamar tsohon ɗan jari hujja. Nifa wannan al'amari ya fara bani tsoro wlhy”.
Barrister da zuciyarsa ke kai kawo ya fesar da huci, “Kana tunanin yaƙi faɗa mana gaskiya ne Zakariyya?”.
“Fuskarsa ta nuna hakan ai Barrister, ko kuwa Kaka?”.
Kaka da shima dai yake aune-aunensa a rai ya girgiza kansa. “Zata iya yuwuwa gaskiyar ya faɗa, sai dai kumin wani taimako ɗaya dazai warware mana gaskiyar tasa ko saɓaninta, bayan nan zan sanar muku abinda ya faru kafin zuwanmu nan”.
Barrister da shima abinda ke'a ransa kenan ya ɗan juyo ya kalla kaka ta madubi, “Muna jinka Baba”.
“Muyi gaggawar isa gidan Dawood”.
“Shawara mai ƙyau Baba”.
Barrister ya faɗa yana juya motar hanyar da zata kaisa gidan Abu Moosa.
★★... ★★... ★★...
“Mamy kuma duka wayar da lap-top ɗinne nawa?”.
Iffah ta faɗa da mamaki. Murmushi Daneen Ammarah tayi, “Ibnati wannan ai ba komai bane ba, sannan ko baki faɗa ba kina buƙatar su tare da ke kodan ki dinga jin motsin gida. Na biyu kuma wannan aikin da zaki fara kowa yasan mai haɗari ne, dolene ki kasance da waya a duk inda kike a masarautar nan. Da zarar Kinga abinda zuciyarki bata kwanta da shi ba a cikin mu huɗun zaki iya kiran kowa ki sanar masa. Lap-top kuwa ni naga ya dace na kawo miki ita domin ɗebe kewa. Amma kiyi taka tsantsan ki kuma kula sosai, dan samun waɗan nan na nufin zaki iya mu'amula da kowa musamman a yanar gizo batare da kin samu tabbacin wanene ɗin ba”.
“Haka ne Mamy, insha ALLAH zan kiyaye. Nagode sosai ALLAH ya saka da alkairi”.
“Karki damu kin cancanta ne ai”.
★Iffah ta daka tsallen murna bayan ficewar Daneen Ammarah, harda ƴar rawarta. Duk wani tunani da kaikawon da zuciyarta ke mata akan Shahan-shan zuwan wannan waya da lap-top ya kauda mata shi. Domin a ganinta dama biyu ce tazo mata a lokaci guda kuma zata damata ta yanda dole sai Shahan-shan ya shata. Yanzu dai abu na farko da zata fara shine malam Fawzan. Ta tura masa saƙo bayan nemansa da tai shi da abokinsa wayar Arfa dake hanunta ta mutu ba caji, tana buƙatar tasan ko yaga saƙon? Ya kuma iyayenta suke?.
Samun wayar da caji yasa tun a daren ta haɗata, duk da taga akwai sim card batai amfani da shi ba ta cire na Arfa ta sanya. Tamkar jira saƙon Malam Fawzan ne ya fara shigowa, jikinta har tsuma yake wajen buɗewa. Batako kai ƙarshen karantawa ba kira ya shigo. Gabanta ne ya faɗi ganin baƙuwar lamba, amma tsabar ƙarfin hali sai ta ɗaga.
“Sir!”.
Ta faɗa cikin gwalalo idanu da nufar ƙofa da sauri ta saka key. Daga can aka amsa mata da “Na'am Fareedah. Ina kika shiga haka? Tun bayan ganin saƙonki na kasa samunki, har zuciyata ta karaya da ko wani ya gano ki ne?”.
“Babu wanda ya gano ni Sir, akasi aka samu wayar ta mutu, na kuma rasa ta yanda zanyi cajinta dan na manta da cajan a gida”.
“Ayya. Kin ganni akoda yaushe cikin gwada wayarki nake koza'a dace. Saboda ke na samar da wannan layin na sirri. Yanzu ma gwadawa kawai nake amma banyi tunanin samunki ba sam”.
Iffah ta share hawayen da suka silalo mata tana ɗan murmushi. “Nagode Sir, koda banyi nasara ba bazan taɓa mantawa da kai ba. Ina fatan ka bincika min su Ummu. Dan sam na kasa samun kwanciyar hankali na rashin jin su”.
Ɗan jimm yay kamar mai tattaro abin faɗa, sai kuma yay ɗan murmushin basarwa. “Suna lafiya dan har gida naje, sai dai ban samu shiga ba kasancewar suna tare da tsaron dakarun masarautar har yanzu. Amma nayi ƙoƙari mun haɗu da Hanash....”
“Amma miyasa wayoyinsu basayi?”.
Ta katsesa a ƙagauce. Da ƙyar ya iya tattaro abin faɗa a wannan gaɓar ma. “Shi Babiy wayarsa ta samu matsala ne. Hanash kuwa network ne dan yace min shima yasha nemanki amma baya samunki”.
“Bani da lafiya ne, ba koyaushe kuma wayar ke kunne ba. Amma yanzu zan sake nemansa insha ALLAHU dan ina matuƙar bukatar son naji muryoyinsu kozan samu nutsuwa”.
“Hakan yana da ƙyau. ALLAH kuma ya ƙara lafiya. Kinyi waya da abokina kuwa?”..
“Eh nayi, amma kamar yanda na sanar maka a text message an ɗaga amma ana mun wani shirmen banza. Daga ƙarshe ma akace wai na saɓa lamba”.
Karan farko malam Fawzan yay ƴar dariya. “Taku ne kawai irin na masu iyawa. Amma a yanzu na tabbatar zai saurareki”.
Iffah ta ɗan taɓe baki kamar tana gabansa. “Ni ALLAH harna ɗauka ko ka yaudareni ne ka bani number daba itaba ma”.
“Iffah koda abin wasa kikazo da shi bazan masa riƙon banza ba balle wannan mai matuƙar muhimmanci da ma'ana. Yanzu dai ina fatan wayar taki akwai caji?”.
“Ai bama waccan bace, sabuwa fil aka bani a kwali yau harda lap-top”.
Jimm yay na wasu ƴan sakkani. Sai kuma ya cire wayar a kunnensa ya duba. Tuna ashema shine ya kirata ya sashi sake maidawa. “Amma baƙya zargin akwai wani dalili a baki wayar? Mutanen nan fa sunada haɗari sosai Iffah. Bazan ɓoye miki ba inajin tsoron ƙarfin ikonsu”.
“Nice zan baka wannan labarin Sir kasancewata a cikinsu yanzu. Sai dai kuma wanda suka bani wayar yanki ne na mutanen kirkin cikinsu. Kasan a ko ina akwai ƙyakykyawa akwai kuma mummuna”. Tsaf ta kwashe yanda sukai ta sanar masa saboda ta matuƙar yarda da shi. Shine kuma takema kallon wanda zai taimaka mata a wannan yaƙin kamar yanda tai fata. Ya jimanta al'amarin matuƙa, ta wata fuskar kuma yayi murnar ganin hanyar samun nasararsu ce tazo.
“Lallai mun samu hanya ta jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya Iffah. Sai dai dole kiyi taka tsantsan da waɗan nan wayoyin. Ki buɗe account da duk kike ɓuƙata da layin da suka sanya miki, shi kuma wannan nakin watsap kawai zaki buɗe da shi, sai dai karki barsa akan wayar, da kuma kinyi magana da Ajmaal da shi ki goge watsap ɗin ki cire layin sai zaku ƙara ki maida. Akoda yaushe wayarki ta kasance da security na idanunki bana wayar ba. Dan inada tabbacin suma zasu saka ido a kanki. A daren nan ki buɗe watsap ɗin ki sake ma Ajmaal magana”.
“Nahode Sir, insha ALLAHU zan yi duk yanda kace”.........✍️
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*
*DAUDAR GORA Billyn abdul*
*KI KULANI hafsat xoxo*
*A RUBUCE TAKE Huguma*
*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*
*IDON NERA Mamuh ghee*
_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_
_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_
_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_
_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_
_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_
_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN
MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171
SAI A TURA SHAIDAR BIYAN
09033181070
IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA
09166221261
*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*
+227 96 09 67 63
Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA
KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.
MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻
*_29_*
.........Barrister na ƙoƙarin shiga layin gidan Abu Moosa wata baƙar mota na ficewa. Babu wanda ya damu da ganinta a cikinsu, suka ƙarasa kutsa kai har ƙofar gidansa. Ganin gidan rufe daga nesa baisa sun kawo wani abu a ransu ba duk suka fita. Abu Zainab ne ya ƙarasa har jikin ƙofar. Kansa tsaye ya kai hannu ya fara knoking, amma har tsahon mintuna biyu babu alamar motsin mutum.
Juyowa yay ya ɗan kalli su Kaka dake kallonsa. Cikin sarewa ya girgiza musu kai. “Banajin fa akwai mutum a gidan nan, dan babu wani motsi”.
“Kara dai bugawa”.
Cewar Barrister cikin bashi ƙwarin gwiwa. Kai Abu Zainab ya kaɗa ya cigaba da bugawa, maimakon a buɗe nan sai ƙofar makwaftansu ce ta buɗe. Wani matashin saurayi ya fito. Abu Zainab ya maida hankalinsa garesa suka gaisa. Kafinma ya tambaya saurayin ya bashi amsa.
“Ai banajin akwai kowa gidan nan. Saboda yanzu babu jimawa matar gidan aka ɗauke a mota harda ƙaton akwati”.
Da mamaki Abu Zainab ya ce, “Kana nufin yanzun?”.
“Eh, dan banajin sunma rufa minti goma. Ta kuma yima mahaifiyata sallama akan zata koma garinsu ne. Harma mukayi mamakin hakan ganin duka rasuwar mijinta bai wuce kwanaki goma sha biyar ba”.
Godiya Abu Zainab yay masa jiki a saɓule ya koma gasu Kaka. “Waifa kunji babu jimawa tabar anguwar nan. A yanda tacema makwaftansu ma ta koma garinsu ne”.
“Garinsu kuma?”.
“Haka dai yace. Nifa na fara tsorata da lamarin nan, dan tabbas akwai abinda ke ɓoye da bamu sanshi ba”.
Tsakanin Kaka da Barrister babu wanda ya iya cewa komai....
*_MASARAUTA (JASRAH)_*
“Wai ni naga sai faman moso kike, kinma kasa bani labarin yanda kukai da Akia akan zancenmu na jiya. Kuma naga wucewarku ke da ita ɗazun zuwa sashin Mamma (Malikat Haseena)”.
Cike da zolaya ta ɗan hararesa. “Ko kuma dai ƴan leƙen asirinku sun sanar maka ba”.
“Leƙen asiri kuma? Haba sai kace dai ku. Kudai matan masarautar nan ne dai da baƙwa iya rayuwa sai dai ƴan leƙen asiri. Amma mu maza miya haɗamu da wani leƙen asiri kamar marasa aikin yi”.
Ta ɗan dara kaɗan da taɓe baki. “Muma ɗin ba kowa ne yake hakan ba kamar yanda kuke zargi. Niko waya dameni a daular nan dahar zan damu da saka wani bibiyarsa. Ko lamarin Zaki addu'a ce tamu a garesa kawai”.
“To ALLAH yasa hakan. Yaya zaman naku ya kasance?”.
“Zama an samu nasara. Dan inama Akia bayani a take ta amince, ta kumace muje sashen Mamma itama muji ta bakinta. Alhamdullah sai aka dace itama zancen ya ƙayatar da ita. Na taƙaice maka zance a yanzu haka ma mun zauna da ita yarinyar. Insha ALLAHU zuwa gobe ma zata koma sashenta. Sai dai abu ɗaya ne fa Mamma bata amince da shi ba”.
“Minene shi?”.
“Sake kai wata Zawjata-almilk turakarsa. Acewarta za'a ƙara jinkirtawa aga abinda yarinyar zata samo. Sannan za'a sakema duka Zawjata-almilk ɗin sabon horo akan kasancewar su Zawjata-almilk a wannan karon”.
(Wata sabuwa kenan, wannan tsinanniyar tsohuwar ko) ya ambata a zuciyarsa. A fili kam fuskarsa ya kawata da sabon murmushi da faɗin, “Woow wannan tsarin yayi, shiyyasa Mamma ke daɗa birgeni. Hakan ma wani mataki ne da zai taimakemu matuƙa. ALLAH kuma yasa mu dace”.
“Amin dai Abu Harith. Dan gaskiya a wannan gaɓar ina tsoron a ce abinda ya faru ya sake maimaita kansa. Saboda zuwa yanzu hankalin manyan ƙasashen duniya ya fara dawowa kan ƙasar ruman. Dan ma ana shakkarmu ne da tuni wani zancen ake ba wannan ɗin ba. ALLAH dai ka bayyana gaskiya ka kuma wanke wanda ake neman disashewa saboda son zuciya”.
“Amin Meera. Amma ko yanzu ɗin ma akwai abinda baku sani ba. Shahan-shan na ɓoyewa ne kawai dan karya tashi hankalin kowa. A wata mai kamawa shugabannin manyan ƙasashe bakwai na africa zasu kawo ziyara ƙasar ruman. Bisa jagorancin shugaban ƙasar Nijeriya, bama raba ɗayan biyu akan wannan al'amarin ne kuma”.
“Ya Arrahaman”.
Jasrah ta faɗa a tsorace.
“Ki kwantar da hankalinki, dan ALLAH kuma kar kowa yasan wannan, dan na sanar miki ne kema saboda na yarda da ke”.
Badan hankalin nata ya kwanta ba ta jin jina masa kanta kawai. Cigaba da kwantar mata da hankali yay cikin kwantar da murya har barci ɓarawo ya kwashe ta. Sai da ya tabbatar barcinta yayi nisa sannan ya zare jikinsa cikin sanɗa ya fice zuwa ɗayan