Showing 84001 words to 87000 words out of 122381 words
jefata a ruɗani takeyi......
*_BARRISTER_*
Duk yanda Barrister yaso sanin suwaye su? Mi kuma yay musu basu saurareshi ba suka turasa cikin jibgegiyar baƙar motarsu, yayinda ɗaya daga cikinsu kuma ya shiga motar Barrister ɗin ya fiddo komai na ciki a cikin wata ƙatuwar jakka suka bar wajen.. Suna ɗan matsawa a wajen wani abu mai masifar ƙara ya ziyarci kunnuwan kowa. A take aka fara gudun ceton rai dan duk wanda yasan bomb yasan shine a yanzun ma.
“Innalillahi wa inna'illaihirraji'un”. Barrister ya faɗa idonsa nabin motarsa da tai sama ta shiga dawowa pieces ƙasa alamar dai bomb ɗin daga cikinta ya tashi. Duk da ya firgita da mutanen yay jarumtar dubansu fuska a dake. “Ku su waye? Miyasa kuka aikata min haka?”.
Babu wanda ya tanka masa a cikinsu, kamarma basu jisa ba sukayi. Hakan sai ya ƙara tada hankalin Barrister, dan ya fahimci ya shiga hannun mugayen mutanen nan kenan. Yunƙurowa yayi da nufin ƙara magana suka jefa masa handkherciff a fuska, daga haka bai sake sanin inda yake ba sai buɗe idanu yay ya gansa a wani ɗaki da bai san inane ba...
Gaba ɗaya jihar Hubab da ƙasar Ruman a rikice ake akan tashin wannan bomb, dan abune da bai taɓa faruwa da su ba. Jami'an tsaro sun iso akan lokaci, sai dai Alhamdullah ba'a samu asarar rai ko ɗaya ba daga mutanen gari, amma ana tunanin harda drivern motar al'amarin ya rutsa saboda babu wanda ya lura da sanda mutanen nan suka ƙwamushe Barrister ɗin kasancewar komai sun yisa ne cikin ƙwarewa...
Jami'an tsaro da ƴan jarida tuni sun iso wajen akan lokaci, hakama jama'ar gari masu jarumta sun zagaye wajen domin ganema idanunsu. Babu gawar direban motar a duk iya bincike da jami'an tsaro sukayi, dan basu ga wani alamar sassan jikin mutum ba ko ɗan yatsa, hakan sai ya ɗaure musu kai dan mutanen da abun ya faru a idonsu sun tabbatar sunga lokacin da mai motar ya ajiye ta a wajen ya shiga masallaci, koda aka fito kuma mutane da yawa sun tabbatar sunga lokacin daya nufi motar wasu ma sunce har ya shiga. Wannan zance ya sake ɗaukar hankalin jama'a kowa yana faɗar albarkacin bakinsa akan al'amarin...
Isowar wasu samari wajen kusan dai-dai da tashin bomb ɗin, kallon juna sukai da sakin dariya a tare suna tafawa. Sai da sukai mai isarsu drivern dake jan motar ya ɗauka waya. Nuni yay musu da suyi shiru. Take motar tai tsit kuwa. Ya ɗan rissina cike da girmamawa tamkar yana a gabansa ne yana kwasar gaisuwa, bai damu da a yanda aka amsa masa a daƙile ba ya cigaba da faɗin, “An rufe babinsa ranka ya daɗe”. Murmushi yayi alamar an amsasa da magana mai daɗi daga can. Sai kuma ya sauke wayar da juyawa yana kallon ƴan uwansa ya kashe musu ido. Dariya suka shiga kwasa a yanzun ma, bayan sanyi wadda suka gamsu sun wadata sannan suka fita suma suma shige cikin taron mutanen dake wajen dan jin mi'ake tattaunawa.....
★★★..... MASARAUTA ★.....
Sai da ya kai zaune a inda aka shirya tarin abincin da kusan minti biyu sannan ta motsa itama dalilin maganar da Hadimai sukai mata. Bata musa ba ta miƙe zuwa inda yaken cikin takunta na nutsuwa da wasu ke ɗauka yanga ko makamancin hakan. Zama tai irin nasa na ƙasaita sai dai da alama ita kanta bata fahimci tayi hakan ba ma. Tsaurin idonta ya sakashi dubanta ta gefen ido batare da alamar hakan ta bayyana a yanayinsa ba. Tuni hadiman suka ƙaraso domin shirya abincin garesu. Iffah batai yunƙurin hanasu ba, dan a ganinta dole ta nutsu ta fara fahimtar yanda ake masa komai kafin ta karɓa wannan tsarin shima. Ta ɗan bi madarar da hadimar ta ɗauka, har yanzu zuciyarta na mata wasiwasi akan madarar batare data san dalili ba...
“Bar nan”.
Ta faɗa dai-dai Hadimar na yunƙurin zuba madarar a ƙaramin cup na glass daya gama haɗuwa. Cikin mamaki hadimar ta sake risinar da kai domin girmamawa ga Iffah tana faɗin, “Ya Zawjata-almilk madara na ɗaya daga cikin abinda shugaba yafi buƙatar amfani da shi a irin wannan lokacin”.
Kai tsaye babu ko ɗar tattare da Iffah tace, “Na yau dai bazai sha ba. A ɗaukesa anan”.
Tsoro ne ya bayyana sosai a fuskar hadimar, gashi bata da damar ko satar kallon sashin da Tajwar ɗin yake balle ta fahimci karatun tasa fuskar. A ɗan ɗar-ɗar na rashin madafa ta ajiye tambulan ɗin a gefe ta ƙarasa aikinta. Duk da abinda ake yi a gaban Tajwar Eshaan ne, yanaji kuma yana gani. amma tsabar miskilanci da ƙarfin iko irin na masu ƙasa a hannu bai ko motsa ba balle bada wata alama akan abinda Iffah tayi ya bashi mamaki, ko ya ɗimautashi, koya birgesa, koya bashi haushi. Ko ɗaya babu mai iya tsinta a yanayinsa. Iffah ma dai bata yarda ta dubesa ba balle ta tsinta komai a tattare da shi ɗin. Sai ma wani kallon da taima hadiman ya tabbatar musu bata bukatarsu a wajen. Dan haka tuni suka ɓace tamkar ƙyaftawar ido.
Ya ɗan ja wasu mintuna zaune batare da ya taɓa komai ba, Iffah ta ɗan laɓe baki, acan ƙasan maƙoshi ta furta
“Ranka ya daɗe barka da wannan lokaci”.
A hankali ya ɗago ya zuba mata idanunsa, a mamakinsa bashi take kalloba ma. Kuma ya tabbatar itace tai maganar ba wani ba dai. Sake tsukewar fuskarsa mai cike da gizago da motsa hanunsa dake kan spoon ya tilasta Iffah ɗan ɗagowa garesa. Sai kuma ta tsaya cak tare da ɗago birkitattun idanunta da ƙyau. Cikin nasa dake kallonta suka shige tamkar ya tsara hakan da gayya. Muƙut ta haɗiye yawu da ƙoƙarin kame rauninta dake neman bayyana a fili ta kauda kai gefe.. Shima nasan ya janye a ƙasaitance ya fara cakulal abincin kamar mai cin magani batare da ya amsa mata gaisuwar tata ba. Hakan da yay ya sosa zuciyar Iffah, dan haka ta kumbura fuska lips ɗinta suka shiga motsawa alamar akwai magana a bakinta sai dai babu damar faɗa...
★★.... ★....
Tun bayan tabbatar da madarar ta shiga jerin abincin liyafar da aka shiryawa Shahan-shan da Zawjata-almilk ta kasa zaune ta kasa tsaye, bukatarta kawai taji sakamakon da take buƙata ga amintacciyar hadimarta akan lokaci. Sai dai kuma shiru kakeji wai malam yaci shirwa har lokacin da labarin tashin nakiya a jihar Hubab ya iso cikin masarautar. Ba wannan ne a gabanta ba, dan haka cikin jan tsaki ta kashe television ɗin a harzuƙe. Idanunta ta sake maidawa kan agogon falon tanaji kamar tai tsalle ta ganta a sashen Tajwar Eshaan ɗin ayita ta ƙare. Dan yanzu a duniyar nan gani take bata da babban maƙiyya sama da yarinyar nan datai mugun shige mata hanci amma ta gagara fyatota ta huta a dalilin gargaɗin Uwa data kasa gane manufarsa har yanzu. Sai dai yarda da Uwa ɗin ya tilasta mata bin komai ɗin a sannu. Zata iya rantsuwa tunda ta san kanta bata taɓa cin karo da abinda ya kiɗima zuciyarta ba irin saƙon Zawjata-almilk na raye bayan ta kwana a turakar Shahan-shan kuma. Ba ita kawai ba, hatta Uwa hakan ya kiɗimata da sake tabbatar da yaƙine na gaske tsakaninsu da wannan yarinyar kenan. Dan haka batai wani magana mai tsaho da Ta-kurya ba bayan bata umarnin a isar da madarar data bata ga Iffah ta ɓace cikin tsanani ɓacin rai daya ƙara birkita dukkan tunanin Ta-kurya ɗin a yanzu har ta kasa zaune ta kasa tsaye sakamakon hakan........✍️
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*
*DAUDAR GORA Billyn abdul*
*KI KULANI hafsat xoxo*
*A RUBUCE TAKE Huguma*
*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*
*IDON NERA Mamuh ghee*
_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_
_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_
_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_
_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_
_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_
_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN
MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171
SAI A TURA SHAIDAR BIYAN
09033181070
IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA
09166221261
*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*
+227 96 09 67 63
Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA
KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.
MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻
*_36_*
........Isowar labarin tashin nakiya a jihar Hubab ya matuƙar tada hankalin duk wani mai faɗa a ji a daular ruman. Dan abune da bai taɓa faruwa ba a kasar ta ruman. Amma abin mamaki ga Tajwar Eshaan ba hakan bane, dan babu wani alamar damuwa ko nuna kaɗuwa da lamarin. Kallo ɗaya yayma akwatin talabijin ma ya ɗauke kai kamar ba'a ƙasar da yake mulka matsayin shugan kowa da kowa al'amarin ya faru ba. A karan farko wani abu da tun shigowar Iffah masarauta bataji akansa ba ya tsikari zuciyarta sakamakon ganin halin da ya nuna akan wannan al'amari da duk wanda ya kwana ya tashi a ƙasar ta ruman bazai ce bai shiga ruɗani ba. Duk da ance ba'ai asarar rai ko ɗaya ba taji kamar ta tashi ta shaƙure wuyan Shahan-shan ɗin ta huta da ganin wannan azzalumin shugaba da kansa kawai ya sani sai ahalinsa.
“Mi hakan ke nufi?”.
Ta faɗa tana faman kai kawo a ruɗe itama duk da a labarin an sanar da ba'a samu asarar rai ko ɗaya ba sai dai dukiya. Abu mafi caja ƙwaƙwalwa ga kowa ma ba ita kaɗai ba shine jin wai wanda ya dasa bomb ɗin ya tsere Bayan wasu sun tabbatar da sunga fuskarsa da shigarsa motar, musamman ma wasu samari huɗu da suka tanbatar da tare suke da wannan mota tun daga ƙauyen Lufana da alama mutumin daga can ya fito. Tabbas sai tayi ajalin wannan mutumin a zuciyarta zataji salama. Dan a ganinta idan yau ya tashi kowa bai rasa ransa ba na gobe kuma fa? A wannan gaɓar ta fara zargin anya wannan sarkin bada wata manufa dama ya dawo ya karɓa mulkin mahaifinsa ba? Dan alamu sun fara nuna uban nasa ma shine ya kasheshi.
“Lokaci yayi da zan fara aikina gadan-gadan”.
Ta faɗa a zahiri cikin tabbatarma kanta da yanayin ɗaukar alwashi....
(Muma kam muna bayanki Iffah, dan muna son sanin mike zuciyar wannan bahagon sarki haka mai wahalar fahimta😉🥱🏇).
★★★
A babban zauren majalisan manyan masu faɗa aji na daular ruman kuwa na can yana neman hargitsewa dangane da faruwar wannan al'amari. Kowa faɗar albarkacin bakinsa yake a duk yanda zuciyarsa ta ayyana masa musamman masu sukar mulkin Tajwar Eshaan a fakaice. Duk wannan kace nace da akeyi Tajwar Eshaan ɗin na zaune cikinsu amma uffan bai tofa ba har suka ci suka tsire. Sai da suka lafa dan kansu da kuma maganar Miran Arshaan cikin ɓacin rai a garesu sannan Tajwar Eshaan ɗin ya buɗe idanunsa dake a lumshe ya gama ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya..
Akan Miran Arshaan dake cigaba da faɗa rai ɓace kan kausasan maganganu nasu ga ɗan ɗan uwansa kuma sarkinsu a yau basu dace ba ya sauke idanunsa. Cikin muryarsa mai zurfi da ƙasaita ya fara magana a gadarance kuma a fisge...
“Barsu Aami. Waninsu bazai canja komai ba, kamar yanda bazai tirsasa Eshaan yin komai ba. Abinda kawai nake son ku sani, Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed guguwace data gama turniƙeku, kuma babu ruwan kogin da zai iya shayar da ita ruwan da zata lafa. Ku daina bama kanku wahala ƙasar ruman da jama'ar cikinta a rubuce suke tsakkiyar tafin hannuna. Idan na murza kwafsanku kawai duniya zata gani a cikin guguwata, idan na matsa, jininku ne zai dinga ɗiga a ƙarƙashin sawun ƙafata na ringa bi ina takawa matsayin kwalta, ya rage naku ku zauna a inda na baku zaɓi ko ku zaɓo mummunan ƙaddararku da kanku tun lokacin ɓacewarku a doron ƙasa baiyi ba”.
Yana gama faɗa ya miƙe cike da takun Izza da kasaita ya bar falon. Da kallo duk suka bishi ran wasunsu na ƙuna, zukatansu kam tamkar zasu kifo ƙasa dan firgici. Cikin dauriya da nuna jarumta wani ƙyamusashen dattijo da tsufansa ya fara bayyana a cikinsu yay ƙwafa rai ɓace da kausasa murya.
“Lallai wannan yaron ya cika ya tumbatsa kuwa. Wai kenan haka zamu cigaba da zama yaro ƙarami na tafka kuskure da mulkin zalunci yana kuma takamu a yanda ya gadama. Akaf tarihin mulkin daular ruman ba'a taɓa tsageran yaro kamar wannan ba, amma ubansa ya ɗaura shi matsayin Shahan-shan bayan babu mai makamancin shekarunsa daya taɓa zama a wannan matsayin. lokaci yayi da zamuyi bore wajen tsigesa kafin ya gama halaka ƙasar baki ɗaya tunda naga shi ran ɗan adam ba'a bakin komai yake garesa ba. wama ya sani ko shine yasa a dasa nakiyar kamar yanda ya kashe ubansa da ƴaƴan mutane da aka aura masa. Koda yake minene ma na tantama tunda ga amsa ya bamu da bakinsa cewar ƙasar da ƴan ƙasar duk a tafin hannunsa muke”.
A zahiri dai kowa yay tsitt yana sauraren dattijon, amma a zukatan wasunsu farin cikine fal da zantukan wannan tsoho ga Tajwar Eshaan ɗin da mafi yawansu shakkarsa ta gama zagaye tunaninsu duk da kuwa kusan duk sun haifesa dan babu wani sa'ansa, dan har yanzu tun ƴan majalissar mulkin mahaifinsa ne bai canja ba. Dattijon na rufe baki Miran Jasim ya miƙe rai a ɓace shima. Dattijon ya watsama wani mummunan kallo da faɗin, “A lallai ka cika dattijon banza dan bazan kalleka matsayin Aami ɗinmu ba yau kam. Mun godema ALLAH daya fara nuna mana ku a zahiri, ai bamu san ɗan ɗan uwanmu ya kai muku har haka a zuciya ba sai yanzu. To ku sani duk ma mai irin wannan tunanin ya makaro, Eshaan kuma a gareku sai gani sai hange sai hararar nesa, dan badai mutum ba ku rubuta ku aje”. Ya kare maganar yana ɗan ƙyaftama Miran Arshaan daya saki baki tsabar al'ajabin ɗan uwan nasa da kasa fahimtar inda ya dosa. Cikin sauri ya kaɗan kansa da amshe zancen a fusace shima yana miƙewa. “Aam ai ban san haka kakeba wlhy sai a yau, ashe zaka zama na farko a jerin wanda zasu soki jinin Haysam Akhi kuma ɗan uwanka mahaifinmu dan ƙasa ta rufe idanunsu? To bazamu ce da ku komaiba a yanzu, amma kusani duk wanda yake da wannan ƙudirin a ransa jininmu fansa ne ga kare Eshaan tako wace fuska. Mun barku lafiya”.
Waɗan nan zantuka na Miran Jasim da Miran Arshaan sun matuƙar saka ruɗani a zukatan duk wanda ke a wannan zauren taron. A take wasu suka shiga barranta kansu ga wannan magana ta dattijon Aamin sun ganin waɗanda ma ya dace suyi hanƙoro da kwarema Tajwar Eshaan ɗin baya saboda kwaɗayin kujerar da yake kai tunda suma sunada hakki a kanta na tare da shi su kuma a wa. Anan fa rikici ya kaure aka tashi baram-baram....
★★
“Nikam na kasa fahimtar dalilin ka nayin hakan”.
Miran Arshaan ya faɗa bayan fitowarsu daga zauren tattaunawar. Wani shegen murmushi Miran Jasim ya saki cike da basarwa. Sai da sukai nisa da sashen Tajwar Eshaan gaba ɗaya sannan yay wata ƴar dariya batare daya kalla Miran Arshaan ɗin ba. Shimfiɗa kenan daga cikin plan b, harinmu na gaba shine ƙulla alaƙa da yarinyar nan, dan na san yanzu abinda zatai yinƙurin farawa shine bincike akan wanene shi”.
“Wai ya akai duk kake sanin hakan?”. Miran Arshaan ya tambaya cikin mamaki. Dariya Miran Jasim yayi sosai da faɗin, “Arshaan Akhi har yanzu kai ɗin yaro ne. Waya gaya maka mai nema yana zaman jiran tsammani. Tashi yake da ƙwanji da zuciya wajen samowa ai. Karka damu da inda na sani, kai dai kawai ka tabbatar littatafan nan da mukai magana kwanaki an kaisu books room an ajiye a daren yau, dan bana raba ɗayan biyu zuwa gobe zata iya bukatarsu”.
Cikin halin ko'in kula Miran Arshaan ya ɗage kafaɗu da tabe baki, sai dai acan ƙasan ransa dariya yake dan shima akwai nasa shirin akan hakan tun randa sukai maganar......
★★
Duk da fuskarsa mai tsananin ɓoye sirrin zuciyace a yau ɓacin ransa sai da ya bayyana. Huci kawai yake faman furzarwa a kai-akai. Dan daga ɗakin meeting ɗin nasu da ba'a samu damar tattauna abinda ya dace ba kai tsaye sama yay can ƙarshen rufin ginin sashen nasa da aka gyara domin hutawa kawai. Ko gaisuwar hadiman dake tsare da