Showing 87001 words to 90000 words out of 122381 words

Chapter 30 - Daudar Gora Book 1 Hausa Novel Complete

25 Dec 2024

405

ƙofar shiga wajen baiyi ba. Ya jima yana faman kai kawo hannayensa zube cikin aljihun farin wandonsa. Bakajin komai tattare da shi sai shaƙa da furzar da numfashi. Sai da ya ɗan samu nutsuwar da yake bukata ya zaro waya dake cikin aljihunsa. Kira yay, bugu ɗaya kuwa aka ɗaga, batare daya amsa gaisuwar da ake masa ba a kausashe ya furta. “A sakaya min shi, inda babu wani mahaluki da zai taɓa hasashe a kansa”. Yana gama faɗa ya yanke kiran cikin sake tsuke fuska da zuƙa ya fesar.....

(Anya kuwa....?? 🤭bakina kanen kafa ta dai🏇).

★★

A ɓangaren Iffah tana tsaka da kai kawonta da ƙullawa da warwarewa itama wani tunani ya sata tsayawa cak. Miƙewa tai cikin gamsuwa, sai kuma ta koma ta zauna bisa wani tunanin da yazo a bayan wanda ya sata mikewar. A kallo ɗaya zaka fahimci tana cikin yanayin da duk wani ɗan ƙasar zaka iya ganin ya shiga sakamakon wannan baƙon al'amari daya shigo musu. Da farko bai lura da ita ba saboda idonsa rufe yake da ɓacin rai har lokacin, sai da ya kai zaune yay ƙoƙarin lumshe ido sai kuma ya buɗesu a kanta dai-dai itama ta kallesan mamakin yanayinsa na yanzun kuma fes a fuskarta. Ita ta fara janye nata shima sai ya furzar da huci mai zafi yana maida nasa ya lumshe kamar yanda yayi a farko.
Falon ya ɗauka shiru babu alamar wani zai tanka sai karar na'urorin ac dana tv da har yanzu ake cigaba da nuna al'amarin da yanda hankulan jama'a ke tashe. Kiran sallar la'asar ne ya katse zaman shirun nasu. Iffah ta fara yunƙurawa ta tashi batare da ta ko sake kallonsa ba dan da gaske har cikin rai haushinsa takeji yau. Da kallon ƙasan ido ya bita harta ɓacema ganinsa. Ya ɗan sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya da maida idanunsa ya rufe. Sai da Iffah tai kusan mintuna huɗu da barin wajen sannan ya mike shima har yanzu da alamar ɓacin rai tattare da shi....

★★★....

Bayan Iffah ta idar da salla kamar yanda ta tsara tai shirinta tsaf cikin wata doguwar riga mai tsananin ɗaukar idon duk wanda zai iya kallonta. Kamshin data gaje batare da umarnin mai shi ba ta baza tamkar tayi ɓarinsa a jikinta. A cikin dukkanin shirinta babu bijirema umarnin waɗan da tazo wannan matakin a dalilinsu, dan haka kai tsaye tai kiran number Daneen Ammarah. Ana ɗagawa tai sallama cikin sauƙaƙa murya mai nuna ladabi. Daga can Daneen Ammarah ta amsa cike da zumuɗi da nuna jin daɗinta da wannan kira.
“Shahrbano ce da kanta haka?”.
Murmushi Iffah tai mai bayyana haƙora jin sunan da Daneen Ammarah ta kirata da shi. Ta girgiza kai tamkar tana a gabanta. “Mamy zakisa a tsire ni a tsakkiyar daular ruman fa”.
Dariya sosai maganar ta bama Daneen Ammarah. Dan haka ta dara sosai kafin ta tsagaita. “Waya isa ya tsire Ibnati kuma Shahrbano duk faɗin ƙasar ruman. Babu mai wannan power ɗin Ibnati, ko maƙiya sun san kin gagara sai kallo daga nesa, dan kowa ya tabbatar a yanzu ke ɗin ce _Lady of the city_”.
Komai Iffah bata iya tace ba, sai dai Daneen Ammarah na iya jiyo sautin murmushinta harta gama kwarzantata.
“Mamy dama na kiraki ne na shaida miki ina ɗan son na fito zama waje ɗayan ya isheni, daga nan sai na ɗan leƙama ɗakin karatu kozan samo abin ɗebe kewa”.
“Hakan kam yana da ƙyau Ibnati. Dan haka ki shirya kawai, hadimanki na sashenki za'a sanar da su su tsumayi fitowarki”.
“Nagode Mamy, ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsohon rai mai amfani da albarka”.
Cikin jin daɗi Daneen Ammarah ta amsa da Amin tana mai saka mata albarka itama.

A yau kam Iffah ta ƙara tabbatar da tsantsar ƙarfin ikon mulkin wannan daula. Dan tunda ta baro hawa na ƙarshe hadiman sashin na Shahan-shan ke faman zubewa gabanta batare da dubi da ƙanƙantar shekarunta ba, matsayinta kawai suke kalla. Duk sai taji zuciyarta babu daɗi ganin kusan duk shekarunsu zai iya kaiwa dai-dai dana Hanash, wasu ma sun girme masa. (Nace Iffah danma Tajwar Eshaan yayi sauyi ne da matasa kikaga hakan, da har sa'an kaka da Babiy sai kin gani kuwa). Kamar yanda Daneen Ammarah ta faɗa tako samu hadiman na zaman jiranta. Ta gane hakanne ta hanyar zuwa da sukai suka zube a gabanta da sanar mata matsayinsu. Batare da damuwa ba duk ta bisu da kallo, su biyar ne cif kuma duk yara ƴammata matasa, za'a iya samun sa'aninta dama wanda suka girme mata kamar su Fariha.
“Ina buƙatar zuwa books room ne akwai wani tsari akan hakan?”.
Da sauri ƴar babbar dake ta gabanta sosai ta girgiza kai. “Ga Zawjata-almilk babu wani dokar yin hakan ALLAH ya ƙara miki lafiya”.
“Okay zamu iya tafiya”.
Iffah ta amsa mata kai tsaye. Hadima ɗaya ce tai gaba sosai Iffah na biye da ita cikin takunta na nutsuwa da wasu kan iya gani su fassara da abinda zuciyarsu ta basu. Bayanta Hadimai huɗu na biye da ita cikin taka tsantsan da nuna girma da ƙarfin ikonta a bayyane...........✍️


*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻


*_37_*



.........Duk ta inda suka gitta kwarjininta dake ɓoye shekarunta kansa a bata girma irin wanda ya dace ga Zawjata-almilk da suka isa a masarautar. Hadimai kam sai zubewa suke bisa gwiwunsu sakamakon sanarwar da ɗan kazagin da Iffah bata farga da shi ba sai da suka fara tafiya taji shelanta tahowarta da yake yi. A yau kam ta ƙara jinjinama girman wannan katafariyar masarauta mai abubuwan kallo matuƙa. Sai dai ga mai kallo bazai taɓa fahimtar hakanba a yanda take faman basarwa kai kace ita ɗin tun fil'azal jinin sarauta ce. Ba wani nisa bane zuwa books room ɗin, hakan ya sakasu isowa cikin ƙanƙanin lokaci dan ma tafiya ce ta ƙasaita....

Cikin ƙankanin lokaci labarin fitowar Zawjata-almilk ya karaɗe masarautar. Hadimai ƴan leƙen asiri dake watse ta ko'ina sun gama kai labari ga iyayen gidansu. Da yawa mamaki ya kamasu tare da gane lallai yarinyar tazo da tsageranci. Inba tsageranci ba wace Zawjata-almilk ce ta taɓa fitowa bayan kaita turakar Shahan-shan da kwana ɗaya kacal. Wasu kuma kai tsaye fassara wannan fita suke da gatsali, acewarsu Iffah nason tabbatar musu tafi ƙarfin iyawarsu, ƙarfin ikon su kuma ba komai bane dan ta gagaresu.

★Malikat Bushirat kanta isowar wannan labari a kunenta sai da tai wani tsamm na nuna mamaki, sai dai bata ce uffan ba kasancewarta mace mai tsananin jin kai da izza. Tana son Iffah, kuma ƙarfin halin yarinyar na kawatar da ita. Sai dai hakan ba yana nufin zata dama damawarta ne a yanda taso ba ko ƙetare tsarin zama a masarautar musamman ga Zawjata-almilk irinta da ƙa'ida komai sai da umarnin Malikat zatayi sa. (Kamar dai ita dake mahaifiya ga Tajwar Eshaan. A ƙa'ida dole komi Iffah zatayi sai ta nema izinin mahaifiyarsa kafin ta aiwatar). Jin al'amarin ya cigaba da caccakar zuciyarta ta sallami duk hadimanta. Kamar ƙiftawar ido suka ɓace kuwa. Rai a ɓace ta ɗaga waya tai kiran Jasrah da ita bama tasan wainar da ake toyawa a masarautar ba kasancewar a ɗan tsakanin nan tana fama da laulayin ciki ne sama-sama.
Duk da a halin rashin jin daɗi da take ciki bazata iya ƙin amsa kiran ƴar uwar tata da takema kallon uwa a yanzu ba. Haka ta kimtsa cikin dauriya ta nufi sashen Malikat Bushirat ɗin. A tsaye ta sameta cikin yanayin ɓacin rai da ya kasa ɓoyuwa a kan fuskarta. Sai duk taji itama nata ran a jagule...
“Akia kina lafiya kuwa? Miya ɓata miki rai haka har fuskarki ta kasa ɓoye wa?”.
Malikat Bushirat ta zuƙa kakkaurar iska ta fesar tana mai kallon ƴar uwar tata. Cikin ɗacin murya tace, “Yarinyar nan ce”.
“Yarinya kuma? Wace yarinya kenan?”.
Kamar bazata tanka ba, tai taku ɗaya zuwa uku batare data dubi Jasrah ba tace, “Zawjata-almilk. Da alama tana buƙatar sai an saita mata zama da tuna mata nan daular ruman ce ba getto eria ɗin data rayu ba. Komai muna yinsa da ƙa'ida bisa umarnin na gaba”.
“Kiyi haƙuri Akia. Amma na kasa fahimtar miya kawo wannan maganar, wace kuma Zawjata-almilk ce a cikin yaran? Dan nasan dai kinfi kowa so da ƙaunar wadda ke tare da shi a halin yanzu”.
“Ina sonta bashi zai bata lasisin shimfiɗa abinda ta gadama na a saman nawa ƙarfin ikon ba. Yanzu labari ya iso gareni ta fito daga sashen Saiful-malik zuwa books room tare da hadimai”.
“Tofa, ita kuma da wannan tazo? Mu muna murnar samunta matsayin wadda zata share kukanmu amma zata fara da haka?. To amma fa Akia wani hanzari ba gudu ba. Shin baki ganin salon yarinyar a wani mahangar nasara ce a garemu. Na farko dai babu wanda yasan ta fito ne batare da umarninki ba. Na biyu koba komai ta sake jaddada isar da saƙonmu akan maƙiya. Na uku salonta tamkar barazana ce ga duk wani shu'umi dake rayuwa a wannan masarautar. Inaga bai kamata ki damu ba, dan a wani ɓangaren ma kamar mune masu laifi, karki manta Mammah ta mikata sashen Abni batare da bin ƙa'idojin da ake kai Zawjata-almilk turakarsa ba. Sannan inada tabbacin ba'a sanar da ita komai game da tsarin komai ba fa, sai aikin da muka faɗa mata zatayi a garemu”.
A hankali Malikat Bushirat ta saki wata nannauyar ajiyar zuciya. Cikin kwantar da murya ta ce, “Hakane kumafa Jasrah, kin tunatar da ni abinda ya ɓacemin har idona ya rufe. Sai yanzu na fahimci lallai wannan fitar tata ma da alama tanada manufa akan umarnin aikinmu. Duk Mamma ce da wannan kwamacalar da muka kasa fahimtar manufarta a kai, nayi niyyar zuwa sashen nata ma naji dalili baƙin nan na ɗazun suka cinyemin lokaci. Amma munyi magana da Ammarah zuwa anjima zanje ko cikin ɓadda kama ne”.
“Hakan yayi, dan koni ina son sanin yaya akai hakan ta kasance. Duk da dai Alhamdullah yarinyar ta kuɓuta. Amma mun kwana a fargaba ai dan ko barci jiya banajin waninmu yayi wlhy. Hatta da Abu Harith kwana yay tunani”.
Murmushi Malikat Bushirat tayi, dan har cikin ranta tana ƙaunar ƙanin mijin nata kuma mijin ƙanwarta, tare da yaba ƙoƙarin sa akan kulawa da kaunar da yake nunawa ga gudan jinin nata tilo da har wasu ke jin zafinsa a gidan bisa hakan.....

★★....

Katafaren ɗakin daya kasance mai cika ido ga Iffah tsarinsa ya matuƙar ƙawatar da ita. Ta samu jagorancin shiga lungu da saƙo na cikinsa bisa taimakon masu kula da ɗakin. Inda a zagayen nasu suke nuna mata abubuwan tarihi na tun farkon ƙarnin kafa Daular ruman ɗin da suka shuɗe cike da girmamawa a gareta. Tafiya kam mabuɗin ilimice haƙƙun dan Iffah ta ilmantu da abinda yafi wanda ta sani ƙalilan a baya dangane da tarihin daular ta ruman da akan tsakura musu a darasin makarantu.
Shugaban masu kula da sashen ya matuƙar nuna jin daɗinsa da bata shawarwari kan tsarin zama mai nazarin tarihi data ambata dan abune daba kasafai ake ganinsa ga matan cikin masarautar ba. Akwai wadda ma bata taɓa taka ƙafarta cikin ɗakin litattafan ba. Amma ita gata ƙaramar yarinya da rayuwarta ke kamar akan ɗar-ɗar abinda ta fara nuna sha'awa na farko akansa kenan. Shine ya fara zaɓa mata books daya ga ya dace ta fara dubawa, hakan yasa ta basar da waɗanda ta shigo nema kai tsaye, dan a ganinta bin shawarar tasa zaifi bata fiye da abinda take buƙata ɗin. Shugaban da shekaru sunyi matuƙar ja a garesa yaji daɗin amsar shawarar tasa da tayi, dan yasan duk da zai iya haifarta matsayinta ya bata ikon yin duk yanda taso a sama da shi...

A cikin farin cikin daya goge duk wani damuwarta a wannan yini ta fito hadimanta na take mata baya ɗauke da ɗirka-ɗirkan littafan da ta ɗebo. A yanzu ɗin ma dai tako ina hadimai faman zubewa suke domin girmamawa a gareta harta isa sashenta data basu umarnin su kaita saɓanin sashen Shahan-shan daya kamata ace ta koma tunda a ƙa'ida sati guda zatayi kamar yanda Malikat Haseena ta sanar da Tajwar Eshaan. Iffah kam da ba zama akai aka faɗa mata komai na ƙa'idojin ba haka kawai taji bata bukatar komawa zaman takura da zuciyarta ta ayyana mata rashin amfaninsa. Shi dai wanda aka kaita dominsa ko kallo bata ishesa ba, hasalima baya kallonta da suffar da suka miƙata garesan kai tsaye. Yo dole ta faɗi haka, tunda wane mijin ƙwarai ne zai jefama matarsa kalmar tambaya ta ita (wacece?) Bayan da saninsa aka kai sadakinsa domin aurota. Bazata iya ɗaukar waɗan nan abubuwan ba, dan bama abinda ya kawota nan ɗin ba kenan tun fil'azal. A ganinta kuma ba sai dole an kaita garesa an ƙaskantar da ita ba, zatabi hanyoyin daya dace na haɗuwa da shi har lokacin da zata cika ɓoyayyen burinta....
Da wannan tunanin suka ƙarasa sabon sashen nata. Tabbas ta jinjinama ƙoƙarin su, dan ko makaho ya laluba yasan wannan sashen yayma wanda aka kaita fintinkau a komai duk da shima wancan ɗin dai ba baya bane a tsaruwar. Ta ɗan sauke numfashi da kaiwa zaune bisa ɗaya daga cikin lumbutsa-lumbutsan kujerun da aka shirya falon da su bakinta ɗauke da bismillah. Suma dai hadiman nata bayan sun ajiye litattafan a saman Centre table a gabanta suka zube. Taja tsahon mintuna goma tana mai nazarinsu kafin ta ɗan sauke numfashi da miƙewa.
“Ina buƙatar zama da duk wanda zai kasance da Ni a wannan sashen zuwa anjima”.
Cike da girmamawa duk suka amsa mata kawunansu a ƙasa. Ta ƙara jan numfashi ta fesar batare data farga da salon izzar da yay kutse ga al'amarin ta na yanzu ba ta kai dubanta ga agogon falon. “Muna da sauran lokaci yanzu da zai ishemu zagaya sashen kafin na shige salla”.
Anan ma sun amsa mata ɗinne da girmamawa. Batare da ta sake cewa komai ba tai gaba duk suka miƙe suna take mata baya. A yanzu ma dai wadda ta jagorancesu zuwa books room ce ke mata bayanin sashen da tsarinsa yanda ya kamata. Cike da gamsuwa batare data furta komai ba koda so ɗaya take gyaɗa mata kai. Sashen ya ƙunsa abubuwa masu yawa da zaman lissafinsa zai zama ɓata lokaci da cinye mana page, bayan sun kammala zaga ko'ina Iffah ta shiga bedroom ɗin da zuciyarta tafi aminta da shi matsayin master bedroom ɗin ta.
Mamaki ya kamata lokacin da taci karo da guntuwar takarda a saman duvet ɗin saman gadon. _Ibnati wannan ɗakin ki tabbar ya kasance ɗakin sirrinki, shiyyasa nasa a shirya miji duk wani abu na buƙatar ki._ takardar ta ɗan juya tana mai jan numfashi da fesarwa. Sai kuma ta saki murmushi dan ta fahimci saƙon na Daneen Ammarah ne. Wayarta ta ɗauka a ɗan gaggauce ta aika mata saƙo. Sannan ta nufi bayi gabatar da al'wala.......


*_★★SHAHAN-SHAN★★_*

Tun bayan faruwar komai daya shige ɗaya daga cikin ɗakunan barcinsa bai sake fitowa ba sai yanzu a cikin shirin zuwa Masallaci. Sau ɗaya ya ɗagama hadiman dake zube ƙasa a dalilin fitowarsa hannu ya fice. Da kallon ƙasan ido duk suka bisa, kowa da abinda zuciyarsa ke ayyana masa game da shi...

Bayan idar da sallar isha'i bai samu damar shigowa ba yay zaman ganawa da Aamin sa su biyu da suka buƙaci hakan. (Miran Jasim da Miran Arshaan). Miran Arshaan shi yafi jansa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login