Showing 30001 words to 30449 words out of 30449 words

Chapter 11 - Rayuwar Rayhana Book 2 Hausa Novel Complete

Unknown   

28 Dec 2024

94

musamman da Mimtaz ta soma hidimar kawo wannan kawo wancan tana lallaminsu su ci. Tambayar kanta take mececedin Khalipha wannan? Khalipha bedroom ya shiga ya sako cikakkiyar suttura a jikinshi ya dawo.
A baki yake baiwa Mami abinci. Mimtaz na hidimar zuzzubawa. Sai ta ji tausayinsu dukkansu su biyun ya kamata. Hawaye sosai take yi da ta tuna Mukhlis haka yake wannan hidimar da ita wajen cin abinci yadda Mimtaaz ke yi yanzu.
Kawai sai ta rungume Khalipha tana bashi hakuri tana yiwa Mukhlis addu’a. Sai ya jawo Mimtaaz ya kara mata ita cikin hannuwanta. Sun dau lokaci a hakan kafin Mami ta ce,
“Ga Radhiyyah, amma wallahi na daina shishshigi a al’amarin Ubangiji. Na baka zabi ka zauna da ita ko ka sahale mata in baka so tun iddah ba ta hau kanta ba. Babu ruwana, kana naka Allah na nashi, kuma nashin shine gaskiya”.
Ta kai gefen mayafinta tana share ido. Tambayar kanta take tana mamaki wa ya nunawa Khalipha danginsa har suka yi masa aure? Ita kanta duk dadewarta a duniya in za’a kashe ta bata san hanyar Hurghadah ba. Ya ce,
“Na sake ta Mami, Mimtaaz ‘yar uwata kuma kanwata ta isheni, Allah ya bata miji na gari, ba zan iya yin adalci ba.”.

A daren Mami da Radhiyyah suka juyo Kano ko gidanta ba ta shiga ba, sai da ta kai Radhiyyah gaban iyayenta. Ta kawo takardar saki da Khalipha ya rubuta ta bayar. Babu tsoro babu shakka ta gayawa Dr. Halima aure ya kare, Khalipha baya so.
Sai abin ya zama fadi-in-fada a tsakaninsu, aka soma maidawa juna magana ana tonawa juna asiri.
Mami ta ce, “Ai na gane kokari kike ki tarwatsa min gida, ki aure min miji, ko kin dauka ban san kuna neman Dacta har ofishinsa ba tunda naki mijin hoto ne baya amfanuwa, in takurawa Da na ya tsane ni, in kuntata masa ke ki farantawa taki?
Ko kin dauka ban san asirin da kike jifana da shi ba? Ba Rayhanah ba, ko uwarta ce yaje ya auro min zan zauna lafiya da ita, so kike ki fiddani daga addinina kina tura min shaidanu cikin kaina, to ta Allah ba taki ba. Ga ‘yarki nan Umma ta gai da Assha, gobe kuje ku kwashe tarkacenku Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhairi, amin”.
Ta mike ta nufi kofa Dr. Halima na gyada kai tana fadin
“Za ki gani, in dai Dr. Mansur ne da kike takama da shi haka za ki barshi wutsiya a zage. Tsohuwar arniya tubabba”.
Mami ta ce, a sanda ta murda kofar falon zata fita batareda ta juyo ba
“Na fi wadanda aka haifa cikin Musuluncin, tunda bana zina balle kwartanci”. Da haka ta fice.

Mu Hadu a RAYUWAR RAYHANAH 3&4.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login