Showing 3001 words to 6000 words out of 31694 words
Chapter 2 - Babban Gida Takun Farko Hausa Novel Complete
tayi Masar ne take samun kuɗi, sauran Masar kuma muna ci da daddare saboda Kawu baya bata kuɗin abinci, sai dai shi ya shigo da ledar abubuwan sa da tsire da irin lemon jarkar man ammah baya taɓa ko sanmana..” can ta ɗan yi shiru
“kuma da kuɗin Masar Mamah take min kayan sallah, sannan tana wankin gidan Cancellor ma saboda ta samu kuɗi”
Jikin yaya Ishaq sanyi yayi jin irin wata rayuwa. Yana nanata wa a ranshi wai baya basu abinci.
Kai anya wasu mazan ko zasu shiga aljanna?
Ka auro mata ka rabata da gidan su ammah ba zaka iya ciyar ta ba?
Haba maza ai kuwa zan taimakawa waɗannan ahaki ko meh zai faru.
Zahrah kuwa da taji shirun yayi yawa sai ta ɗan taɓo fuskar shi
“ka fasa zuwa ganin Mamah koh?”
Jijjiga kai yayi sannan yace
“aah cutie, zanje naga mamah”
Isar su kasuwa keda wuya suka fito, Zahrah ce gaba sai yaya Ishaq da ke bin bayan ta. Directly rumfar da Mamah ke ƙosai ta nufa.
“Mamah ga sabon yayah nah”
Mamah da ta ke kwashe Masar da ta soyu ta ɗago ɗan bata fahimci meh Zahrah ke faɗi ba.
“ya Hajiya Balaaba ɗin”
Ɗan yamutsa fuska tayi da ta tuna wulaƙancin da maamah ɗin tayi mata sannan tace
“lafiyar ta ƙakau, tace a gaishe da ke”
murmushi Mamah tayi sannan ta zuba masa uku a plate ɗin roba sannan tace
“ga Masar nan kici,, nadan baki ci komai ba”
Amsa tayi ta ajiye sannan tace
“mamah ga sabon yaya nahiyar yazo gaishe ki”
sai a lokacin Mamah ta lura da yaya Ishaq dake tsaye harɗe da hannayen shi a ƙirji. Shi kam hankalin shi baya kan shi, in ba da kallon su Mamah babu abun da yake yi.
Gyaran murya Mamah tayi, sai lokacin ya ɗan miƙe da kyau sannan ya nufi rumfar Masar.
Duƙawa yayi ya gaida Mamah cike da girmamawa.
“ina wuni Mamah, ya aikin”
“lafiya ƙalau ” kawai Mamah tace fuskar ta na ainihin bayyana mamaki da kuma kuɗin da ta shiga, idan bata yi ƙarya ba ai wannnan yaron gidan Cancellor ne.
Ganin yanayin Mamah yasa yaya Ishaq ya murmusa..
“mamah nimah ki ɗauke Ni kamar ɗan ki, ki ɗauke Ni kamar yadda na ke jin ƙanwa ta Zahrah a jiki na, bani da niyyar cutarwa a gare ku sai dai ina don tallafa wa rayuwar ku.”
Murmushi mamah tayi
“babu komai yaron nan ammah kai ɗin waye, kuma a ina kaga zahrah.”
“mamah Ni ɗa ne a wajen Cancellor sannan kuma na haɗu da Zahrah ne hanyar tafiyar ta zuwa gidan su Amira ƙawar ta”
Tun daga farko har kaita gidan su amirah da yayi ya labarta wa Mamah. Salallami ta fara
“shikenan Ita dai Zahrah ba zata taɓa sauya halin ta ba kenan, toh Allah dai ya shirya”
Murmushi yaya Ishaq yayi sannan ya matso cikin rumfar, gefen matackn da take ajiye soyayyiyar masa yayi sannan ya kwashe ledodin,, duk wanda yazo siya da kan shi yake zuba musu har lokacin maghrib yayi. Masallacin da ke cikin kasuwar yaje yayi Sallah ya dawo. A lokacin Mamah har ta gama haɗa kayan suyar ta zasu dawo gida.
Ƙarasawa yayi ya ce
“mamah a kwaso kayan sai mu tafi.”
Ƙasa musu mamah tayi kawai ta umarci Lauwali almajirin dake taimaka mata da su wuce. Har wajen motar suka nufa sannan ya jera kayayyakin suka wuce ɗiiiiiiiiiii sai gidan Kawu.
Mamah kam lumshe ido tayi yayin da zuciyar ta ta karye, tunanin when last tashiga mota take yi tun ranar da aka kawo ta gidan masoyin ta Abdulkarim Kuru. Lokacin da ta cire tsammanin wahala a rayuwar ta sai gashi yanzu ɗan uwan masoyin ta na gasa mata aya a hannu.
Suna isowa Lauwali ya ciro kayan ya shigar da su gida, abun mamaki lokacin dabar su Kawu babu kowa sai Aminu Aljan. Basu mishi magana ba suka kutsa cikin gidan. Bayan sun ajiye komai Mamah ta shimfiɗa wa yaya Ishaq sallaya ya zauna sannan ita ma taje tayi sallah.
Mutuniyar kuwa kwantawa taje tayi.
Har Mamah ta idar da Sallah bata ga giftawar Zahrah ba yasa ta ƙwala mata kira
“zahrah, Zahrah fito ki je ki siyo wa Ishaq ruwa gidan su Badi'ah.”
Zahrah da bacci ya ɗan fara kwashe ta ta turo baki gaba sannan ta fito. Mamah sake baki tayi tana kallon ta ganin ko Sallah bata yi ba. Harara ta ɗan yi mata sannan tace
“wuce kije kiyi sallah”
Juyawa Zahrah tayi tana ɓata fuska kamar wainar fulawa sannan taje tayi alwala don yin Sallah. Lauwali kuwa ya gama wanke kayayyakin kamar yadda ya saba yayi ma Mamah sai da safe. Yaya Ishaq ne ya ƙira shi bayan yazo ya zaro 5k a aljihun shi ya bashi.
Godia sosai Lauwali yayi sannan ya wuce.
Zahrah na idar da Sallah ta fito, gefen yaya Ishaq ta zauna sai wani tura baki gaba take yi kamar wani pipe😄.
Harara Mamah ta maka mata kafin ta ce
“tashi kije gidan su Badi'a ki siyo masa ruwa da lemo.. ba musu ta miƙe duk da cewa bata don zuwa gidan.
Badi'a Sa'ar ta ce ammah basa shiri ko kaɗan saboda yadda suke treating nata. Gaba ɗaya unguwar babu wanda ke kyautata musu inda ka cire gidan Cancellor sai kuma Ammin Badi'a, ita dai bata tsangwamar su ammah bata shiga sabgar su.
Bayan ta siyo ta kawo gaban shi ta ajiye, Mamah ta zubo mishi Masar a plate sannan ya fara ci ba tare da jin ƙyamar su ba. Ita ma Mamah tace tare da Zahrah.
Bayan sun gama ci yaya Ishaq ya sanar da Mamah ƙudurin shi na maida Zahrah private school da ke kusa da su. Mamah tayi farin ciki sosai har da kukan ta zai aikin godiya take rabza wa Ishaq, shi kuwa duk kunya ta cika shi.
Da haka yayi musu sallama ya wuce zuwa gida zuciyar shi wasai.
★★★★★
Sai wajen ƙarfe sha biyu na dare (12:00pm) Kawu ya dawo, su kuwa lokacin sun riga da sun rufe gidan. Bugawa yake ta yi babu ƙaƙƙautawa sai kututtuma ashar yake yi.
Sama sama mamah ta jiyo ƙarar buga ƙofa,, a zabure ta miƙe zuwa hanyar waje.
“dan abu ta kazar ubanki ki kizo ki buɗe min ƙofar nan inda ba haka ba in na shigo sai na lahira ya fiki jin daɗi.
Jinjina kan ta tayi kafin taa nufi ƙofar. Tana buɗe ƙofar ko ya banko ta har sai da ta buge kan Mamah. Layi ya shigo yana yi alamun yayi mankas abun shi.
Mamah kuwa cikin zuciyar ta tana Allah wadaran wannan miji nata.
Ƙunshi ledar hannun shi ya ya ƙara ƙanƙamewa kamar za'a ƙwace mishi daga hannun shi. A haka ya nufi ɗakin shi cikin tangaɗi har ya isa bakin ƙofa.. juyowa yayi ya kalli Mamah before ya shige ya na banko ƙofar.
Hawayen da ke zuba kan fuskar ta ta gode haɗi da wucewa nata ɗakin. Ba ita ta ta kwanta ba sai da ta yi alwala ta fara jera nafila tana roƙon Ubangiji ya kawo mata ɗauki.
_______________**********_______________
Ina kuke bayin Allah masu buƙata! Ina waɗanda ke cikin damuwa, ina waɗanda suke buƙatar neman wani zaɓi wurin Ubangiji.
Toh ga damah nan wacce take guarantee.
Manzon ALLAH صلي الله عليه وسلم yana cewa:- “idan dare ya wuce tsakiya ALLAH ( Subhanahu wata'ala ) yana sauƙowa zuwa saman duniya sai ya ringa cewa:- ( shin akwai mai neman gafara a gafarta masa ? ) yana ta fadar hakan har zuwa ketowar alfijir.
( saheeh musleem )
Saboda haka duk wata damuwa da kike da ita, don't hesitate to ask Allah, baya gajiya da amsa buƙatun bayin sa. Ki tashi kiyi sallah, koda raka'āt biyu ne sun wadatar ki roƙi Ubangiji kina mai yaƙini da shi, sai kiga ya amsa miki.
Kina cikin damuwa? Matsalar gidan aure ko kuma jarrabawar rayuwa, toh kada ki kuskura ki cire yaƙini a addu'a.
YA hayyu~ya~Qayyum!! Kayi gafara agaremu da iyayanmu da 'yan uwanmu da masoyan mu da sauran al'ummar musulmai.
KO YA ZATA KAYA?
WANE NE KAWU?ME ALAKAR SHI DA ZAHRA?, MEH YASA YAKE CUTAR DA ITA?
YA KUKE TUNANIN ZATA KAYA IDAN KAWU YA FAHIMCI CEWA WANI NA ƘOƘARIN TAIMAKAWA MAMAH?
AMSOSHIN KU NA NAN TAFe, BA A FARA LABARIN BA HAR SAI MUN JE BABBAN GIDA.
KU CI GABA DA KASANCE WA DA ALƘALAMIN DIAMOND LADY DOMIN NISHAƊANTUWA DA KUMA ILIMANTUWA.
COMMENTS ƊIN KU KAWAI NAKE SO DON SHINE ƙWARIN GUIWA TA
ALƘALAMIN DIAMOND LADY 💎🤟
Oum Zainab ce!
______________★★★_______________
Typing 📲
🏡𝙱𝙰𝙱𝙱𝙰𝙱 𝙶𝙸𝙳𝙰🏡
(𝔗𝔥𝔢 𝔟𝔦𝔤 𝔥𝔬𝔲𝔰𝔢🏠)
★TAKUN FARKO★
[Labari/Rubutawa]
🄳🄸🄰🄼🄾🄽🄳 🄻🄰🄳🅈💎
𝑂𝑢𝑚 𝑍𝑎𝑖𝑛𝑎𝑏🖊️
﷽
PROLOGUE
𝕻𝕬𝕲𝕰0️⃣3️⃣
Shafin ku ne ƙawaye na
ZAINAB SHEHU UMAR ( ZEELY)
SA'ADATU LAMARA ZULKHAIRAT (Matar mijinta)
RABI'ATU ABDULLAHI HASSAN (matar Ɗan jagade)
FATIMA AHMAD ABDULLAHI (Fatima anatomy)
Ina ƙaunar ku saboda Allah
Barkan ku da Sallah
SHARE AND COMMENT PLEASE!
_______________★★★________________
Sassafiya Mamah ta tashi da aikace-aikacen gida. Sai around 8:00am Zahrah ta fito tana miƙa
“oooooooooooh”
Mamah ce ta kalle ta sannan ta kawar da kai. Wurin Mamah ta taho
“ina kwana Mamah"
“lafiya ƙalau Zahrah kije kiyi wanka sai ki siyo manah ƙosai da koko gidan Mati."
Da “toh Zahrah ta amsa tana wucewa banɗaki. Bucket ta cika da ruwa sannan ta shiga toilet ɗin. Wanka tayi ta fito. Rigar ta ƴan kanti wacce ta ɗan ji jiki ta saka kafin ta shafa mai. Tana gamawa ta janyo hijabin ta da saman shi ya ɗan koɗe saboda dukan rana.
Fitowa tayi ta cewa Mamah
“kawo kuɗin”
miƙa mata 500Naira tayi sannan tace
“ki siyo bread 🍞 Babba guda ɗaya da canjin.
“toh"
Daga haka ta fita zuwa gidan Mati da ke kan kwanar layin su.
Tana fita ƙofar gidan su nan a cike kamar wadda za'a yi taro sun cika rumfar wasu kuma har da kan dandamalin da ke jikin gidan sai ihu suke suna buga uban shewa da gani kaga tataccun ƴan iska. Kallo ɗaya tayi musu ta kau da kanta gefe haɗi da tsaki.
Aljan ne ya hango ta sai wani fara washe baki
“ƴar oga! Ina zaki haka da sassafe"
Bata yi tunani da ita yake ba shi yasa ko kallo bai samu daga gare ta ba. Su kuwa sauran ƴan dabar suka saka ihu nan suka fara tsokalar Aljan.
Da ɗan gudu ta isa gidan sannan ta bada kuɗin ta haɗi da miƙa jug ɗin roba da ta zo da shi.
Ana sallamar ta ta amsa bread wajen Bala Mai shayi daga nan ta wuce gida.
Kamar dai ɗazu wurin a cike yake ammah haka ta wuce abun ta saboda gargaɗin Mamah kan kada ta kuskura ta ce zata kula wani a dabar.
A ɗakin mamah suka karya, Bayan sun karya Mamah ta ɗauƙo wasu kuɗaɗe daga aljihun doguwar rigar da ke jikin ta. Kuɗin zasu kai 15k. Da mamaki Zahrah ke kallon kuɗin, duk da bata da wayo sosai ammah ta san wannan kuɗin da yawa suke
“mamah kuɗin menene wannan?”
“yayan ki Ishaq na da kirki sosai, ya bamu ne mu ƙara a jarin masa”
Ko rufe baki Mamah bata yi ba taga ana shigowa da kayan abinci, shinkafa, taliya, macaroni, indomie da mai har da manja.
Mamaki ne a fuskar su har lokacin da aka ce
“a ina za'a ajiye su?”
Nuna musu ƙofar ɗakin ta tayi don kuwa nan ne wajen da zasu rabauta daga hannun Kawu.
Suna gama shiga da su suka fita. Mamah bata bar mamaki ba ammah tayi shiru abun ta.
Sai wajen 11:00am Kawu ya banko ƙofar ɗakin shi fuskar nan duk yawun bacci alamun ko sallar asuba bai yi ba. Wata shegiyar miƙa da yayi abun takaici Mamah dai jinjina kai tayi tana roƙon Allah ya shirya Yunusa..
Wani kallon banza ya watsowa Mamah sannan yace
“ke ɗan ubanki shine jiya kina ji ina buga gida kika ƙi buɗe min? Gidan na ubanki ne? Nace na ubanki ne gidan?”
Mamah dai bata kula shi ba ta ci gaba da yi wa Zahrah bayanin yadda zasu sauya kasuwancin nasu.
Sheƙa Kawu yayi hakan yasa ya kawo wa Mamah wani uban duka.
Caraf Zahrah ta tare ai kuwa sai a tsakiyar kanta wanda yayi sanadiyar faɗuwar ta ƙasa sumammiya. A firgice mamah ta yo kanta tana jijjiga ta ammah shiru.
Hakan bai ishi Kawu ba sai da ya ƙara kawowa Mamah wani dukan. Bata damu ba saboda hankalin ta da ya matuƙar tashi kada taje ta rasa ɗiyar ta.
Ba tare da ya damu ba ya fice zuwa dabar tasu. Wani ihu suka sa suka fara yi mishi kirari
“Takawar ka lafiya Yunusa BabanMutuwa, kayi yadda kaso da uban kowa, ita kanta mutuwar tsoron ka take, kaga sarki mai cikakken iko”
Dariya yayi jin yadda ake fasa mishi kayi nan da nan majalisa ta fara, ana shan sigari ana gulma tare da kututgumo ashar. Authubillah!
★★★★★★★★
Ta ɗauki kimanin mintuna 20 kafin Zahrah ta ja dogon numfashi wanda lokaci ɗaya ta saki wani irin ihu. Mutanen da ke waje kan su sun tsorata bare kuma Mamah dake kusa da Zahrah, wasu faratu ne zaƙo zaƙo suka fara fitowa daga hannun ta sannan ƙwayar idon ta ta juya baka ganin komai sai farin idon da ya sauya zuwa blue colour ga wani girma da jikin ta ya ƙara tamkar wata aljana da ta fito filin daga.
Mamah ko rasa yadda zata yi da ita tayi, banda ɓari babu abun da jikin ta ke yi.
Miƙewa tsaye Zahrah tayi tana nufar hanyar waje, Mamah bata yi ƙoƙarin riƙe ta ba saboda ita kanta a tsorace take.
Hakan yayi daidai da shigowar Kawu cikin gidan.
Zaro idanuwa yayi cikin kiɗima ya fara ja da baya da niyyar guduwa..
Kirif!! Ƙofa ta rufe kanta yayin da halittar dake gaban shi ta sheƙe da wata dariya maras daɗin ji.
“Hahhhhhhhhh_hhhhhhhhh_hhhhhhhhhhh” dariyar da bata tsaya ba sai bayan minti 10. Kawu kuwa duk rashin tsoro irin nashi yau yaji, ai ance faɗa da aljani ba daɗi.... gabaɗaya zufa ce ke ketowa a jikin shi, bata yi mishi komai ba kawai hannun ta ta ɗaga sama lokaci ɗaya Kawu ma ya ɗago bisa iska.
Gefe ta wulla kawu kafin ta ƙara daga shi can sama a wannan karon, wani irin jujjuya shi take wanda hannun ta ne ke famar yin wannan aiki ɗin, bugawar da tayi mishi sai da ƙasa ta jijjiga, tuni ƴan majalisa suka watse duk da basu san daga ina bane hakan.
Ko motsi Kawu baya yi hakan yasa ta busa mishi iskar bakin ta daga wurin da take.
A wahalce yaja wani dogon numfashi. Bai zata ba bai nufa ba sai ka cinnaku sun kewaye shi, cizo ta ko ina yi masa suke. Babu abinda yake banda susa da kururuwa.
Duk abinda ke faruwa Mamah ta kasa cewa komai. Sai can ta samu bakin magana
“zahrah don Allah kiyi haƙuri ki bar shi haka ai yaji jiki”
“hhhhhh_hhhhh" bayan wani lokaci tayi shiru sannan ta juyo tana fuskantar Mamah
Cikin haɗe fuska take magana
“Madina! Wannan ba Zahrah bace nice!” ta faɗa cikin Muryar ta maras daɗin saurara..
Jikin Mamah ne ya fara tsuma hakan yasa Zahrah hura wa Kawu iska, nan da nan cinnakun suka ɓace ɓat! Jikin shi kuwa duk ya kumbura, ga uban ciwon da yake masa. Banzan kallo halittar ta watsa mishi sannan tace
“Idrisu BabanMutuwa!"
A tsorace Kawu ya ɗaga sannan ya maida kan sa ƙasa
“ka saurare Ni da kyau! Ka gama naka mulkin yanzu lokaci na ne!
Ka daɗe kana cutar da mahaifiya ta da bata taɓa zaluntar ka ba!”
A lokacin mamah ta zube a ƙasa sumammiya. Duk wannan na daga cikin shirin halittar.
“Idrisu Ni na san ka! Ka cutar da rayuwar mu, baka san cewa na san kai ne ka kashe mahaifi naba koh?, Kai ne ka hana Mamah komawa ga dangin ta ta hanyar sihiri koh? Toh wallahi ka kuskura ka ƙara wani kuskure kan hakan zan tona asiri har ƙwayoyin da kake siyarwa”
Kawu dai an rasa bakin magana,kai kawai yake jijjigawa.
“magana zaka yi ba jijjiga kai kamar gwaje ba”
“eh na daina wallahi na daina”
Daga haka ta ɗaga hannun ta lokaci ɗaya shima ya tashi bata direshi ko ina ba sai cikin ɗakin sa.
Tana fitowa ta ɗaga Mamah ma ta kai ta kan katifar ta.
Daga nan ta hura mata iska ita kuma ta faɗi ƙasa kamar matacciya..
Numfashi Mamah ta sauƙe lokaci ɗaya kuma ta tuna meh yake faruwa. Tana juyo wa taga Zahrah kwance kamar gawa..
A hankali ta nufo ganin kamar bata motsi yasa Mamah saurin ɗebo ruwa a cup, addu'ah ta tofa ciki sannan ta shafa mata a fuska.
Numfashin da Zahrah ta ja yasa Mamah jin sanyi cikin ranta. A hankali ta fara buɗe idanuwan ta tana mai tuna abun da ya faru.
“Sannu Zahrah, ina ne yake miki ciwo?” ta faɗa a kiɗimce
“mamah kai na”
“sannu yi haƙuri bari na je na siyo miki magani, ki jira Ni kada ki fita kinji..”
Hijabin ta ta janyo ta fito, karo suka ci da ya Ishaq ƙofar gida ba tare da yan shi bane ta gota zata wuce. Cike da mamaki yace
“mamah meh ke faruwa?” sai a lokacin Mamah ta ɗago
“zan siyo paracetamol me a nan chemist zahrah ce ba lafiya.”
“subhanallah, toh ki koma ciki bari na shigo Mu kai ta asibiti.”
Da kan shi ya ɗauko Zahrah ya saka ta a mota. Babu ƙaƙƙautawa suka isa asibiti. A&E (Accident and Emergency) aka nufa da Zahrah.
Taimakon da ta samu daga wurin likitoci yasa ta ɗan ware.
Sai wajen 5:00pm aka sallame su ammah kafin nan Doctor ya nemi magana da namijin saboda matar kam duk a ruɗe take.
Bayan sun shiga office ɗin doctor, a hankali doctor ɗin ya kalli yaya Ishaq
“bawan Allah garin ya kuka bar ƙanwar taka damuwa ta mata yawa, yarinya ƙarama a ce BP nata na elevating haka tun yazo, gaskiya da matsala ko ma meh take so ya kamata Ku bata”
A sanyaye yaya Ishaq yace “in sha Allah doctor za'a kiyaye”
Daga haka ya fito.
Da kanshi ya ƙara ɗaukan Zahrah suka nufi mota har suka isa babu wanda yayi magana. Bayan sun isa Mamah da kanta ta wanki Zahrah da ruwa