Showing 1 words to 3000 words out of 37209 words

Chapter 1 - Karashan Murucin Kan Dutse Book One Complete Hausa Novel

15 Oct 2025

273

??ࡱ?>?? $??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F%WordDocument????1"0Table????????x
Data
???????????????????? P??WKSKS?1"????????rr????????3???R
R
R
R
R
R
R
R
T
$??i *r??R
R
????R
? ??? R
?R
? ?R
R
?? [4/20, 08:39] Ummin Meenat: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , ,


Zan iya cewa mu a wurin mu bamu san wainar da ake soyawa ba sai dai labari mukaji a kano anyi buki sosai don jama, a sun tafi da yawa wurin daurin aure; a sokoto.
Don can aka fara kai amarya suka kwana hudu da sati daya akace za suyi sai gasu da kwana hudu sun shigo Abuja kuma dama already an gyara part din ta don masu decoration ya dauko sukai gyaran ko ina na gidan.
Ina zaune da yara muna hutu don nayi up ranan da suka shigo tun monday shi na fara fita night duty na dare.
Muna zaune yaran sun dsmay ni da korafi akan daddy su ko waya baya bugo masu jinior keda wanan nan korafin ita ko antyna sai dai tayi zaune tai shiru ko abinci sai da kyat take ci dama abinda nakewa gudu ke nan da sabon da yaran sukayi dashi.
Hindatu ce ta shigo falon nawa take cewa dani hussunah ta damay ni wallahi sai kiran kai take yi shine nakawota ki duba min ita.
Nai murmushi tare da dan kamo hannun yarinyar nace da ita daddy ne ko hussuna sai na nuna mata Anty dake zaune tayi wani irin zama na ban tausayi a saman kujera.
Hindatun ke cewa dani aini sam ban dan abinda sukewa ke nan ba na dai dauka haka din ne kanta ke ciwo din take cewa dadi kan nace ta dan karasa inda Anty take zaune tana fadin yarinya ubanki yayi aure ya debe takaici nai.
Daga inda nake zaune nace ya dai kara takaicin shi tunda ya karo wa kansa wani ssbon tention kuma again.
Don ita ma aida nata kalar korafin zata shigo mai kamar yadda muke nan kowa da irin halin rayuwan shi itama a hakan zata shigo ya dagwara a inda ya tsaya.
Kamar hafin jaki sai ga zulfa ta shigo tana goye da yar ta a bayan ta tace da hindatu ashe kina nan ne sai hindatun ke fadin ina nan ke dai na kawo wannan ne tana nuna yar ta take cewa na dauka bata da lafiya ne ashe ita wai kewar uban ta takeyi haka kin gan su can tana nuna inda anty take zaune.
Dariya tayi tare da dan sake habaici tace a, a ke hussuna ashe ba anty kawai ke tare da ubanta ba duk kune gashi ko kullun cikin ganin bai damu da ke ba ashe kema anayi bamu sani ba tunda har kewan shi zai hana ki shakat .
Ta lakuto hancin yarinyar tana fadin ai sai kuyi tunda baba ya bar ku nan yana can yana cire takaicin shi a gun yar amaryan shi yar shila.
Murmushi nayi na dan gyara rike daddy da yazo guna ya fada a jikina sai hindatu ta ce wai ke may yasa baki sanin abin fadawa mutum wani lokaci may ya kawo wanan maganan kuma yanzu ga yarinya kuma, ?
Haba dai ba shi ke gaban ku ba don Allah ya kamata ace zuwa yanzu an daina wanan halin a gidan nan idan ba haka ba itama wacce zata shigo din sai ta shigo muna da raini a gare mu.
Bai kamata ace duk mace zata shigo ta dinga samun ana wanan irin batakan ba a tsakanin mu sai raini yai saurin shiga a tsakanin da ita.
Amma idan ta shigo ta samu kai yana hade yara ma haka sai ki ga ta rasa madafa a gidan wata idan mai hankali ne dole tabi wa yanda ta sama a zauna lafiya.
Idan kuma mai rawan kaine sai tace nata dokan zata kafa dole abita sai idan tayi taga babu kafa a gare ta zata shiga hankalinta.
Idan har wanan matar kuma ta shigo ta samu muna wanan halin na kishi haka a junan mu wallahi a take raini zai fara daga wurin ta bazata taba daukan mu da daraja ba don itama zatace zata gwada nata sa,an a gare mu da maigidan sai kiga tazo ta mallakr gidan a cikin dan lokaci .
Mata da yawa wanan barakan suke samu a gidajen su sai kiga matar baya tazo ta na son raina hankalin matar da ta samu a gidan .
Don ta samu ba hadin kai ko kuma kishiya da miji babu fahintar juna a tsakanin su shi har zata samu daman kokarin kafa nata gwaunatin a gidan.
To kunga idan har karamar yarinya zata shigo cikin mu ta samay mu a haka kamar kowan mu na jirace da dan uwa muna yawan fitina yaran mu ba hadin kai a tsakani may kuke ganin zai iya faruwa ?
Don Allah don Allah ku daina wanan halin na gwatsale juna a tsakani ana fadawa juna maganan da zai sosawa dan uwa rai.
Miji dai mun gani ba mijin mace daya bane ko biyu ko uku mijine na mata hudu Allah ya hada mu dashi idan mun zauna lafiya sai abin yai muna dadi a tsakani.
Don mun tsaya muna cin junan mu a kasan shi fa daddy babu ruwan shi duk mun sani a nan kowa da daukan da yake mata a gidan nan kuma a haka yake zaman dadin rai damu yana bamu duk wani hakkin mu da Allah ya dora mai a kan shi.
Mune dai har yau mun kasa zama mu fahinci junan mu da daya ta gusa mun shiga gulmanta ke nan a tsakanin mu.
Idan kuma dayan tazo a zauna da ita a zagi wacce bata kusa kunga hakan bai muna ba gaskiya ko yaran mu dake sauraren mu kullun zasu fara zargin mu muna fukaine ko su ma su koyi zama irin na annaminanci a rayuwan su.
Don haka don Allah mu sahircewa junan mu mu kama mutuncin kan mu mu zauna lafiya a tsakanin mu zama na amana son juna da karuwa sai kuga komay ya tafi sannu a hankali a tsakanin mu.
Amma fa ni shawara ne nake baku ba wai nace lalai sai hakan ya gudana ba don kowa da ra, ayinshi a tare dashi.
Hmmm maganan ki ai gaskiyace Rahama don baki fadi karya ba ga zancen ki tundai ni da za a kaiwa amaryan part dina mu zauna tare aiko kunga akwai matsala ke nan.
Babu wani matsala ga hakan idan kin iya kama kanki da bakin ki gare ta kika ja girman ki sai kiga kinyi power a wurin ta.
Hmm ai na yarda da ake cewa ba wayewa bane wayo dan kauye da kuke ganin su sun fimu tashin birni wayon tsiya.
Na dago ina dariya nace abin kuma sheri ne haka anty daga shawara kuma.
Tace wallahi Rahama duk sunan mun girmay ki ne kawai amma wallahi duk Rahama kin fimu wayo Allah ko.
Ki duba shawaran bada kudin nan da yai muna in badon ke ba ni ina zanyi wanan tunanen ma yanzu kuma gashi kinzo mina da wani babban shawara wanda duk maganar ki gaskiya ce a cikin sa.
Sai bango ya tsage kadangare ke shiga kafarsa ai idan muna kama kan mu, muna abin mu in matuarity wa zai kawo muna raini a gidan nan.
Mun dauki lokaci muna hiran mu duk dai akan matsalan rayuwan zaman gidan daddy ne da yadda za a dora dashi.
Kwasan ba zato sai ganin daddy mukayi a falon kowan mu ya baje sai kwasan dariya muke yi a falon.
Kallon mamaki, muka bishi dashi har ya kataso cikin falon shima sai bin mu yake da kallo yana mamakin kasancewar mu a wuri daya haka.
Sannu da zuwa muke mashi hankalin shi na kan yan yaran dake zaune a gefen mu suna shan lollipop ko kallon shi Antyna bata yi ba zakace ko wata babbace ita irin yadda ta share uban nata.
Ya karasa gunta yana fadin yau kuma wani sabon sallo kuka dauko ne a gidan haka yakai hannu ya dan taba yar wirin hindatu yana kiran sunanta sai ya juya gun ta zulfa ya lakaci fuskan ta ya dauki anty yana kiran sunan ta tare da ce beta yana fadin my Saade ke nan .
Sai yarinyar takama bultsewa tana son ya sauke ta tana fadin umm, umm ummm yace da ita kai my Saade badai kema kin iya fushi ba ko ?
Ba wanda yai mashi magana bayan gaisuwa sai da yaga yarinyar bata yarda ne ya direta tare da cewa ai ke zaki biyo ni sai Zulfa tace tunda an saba bin bayan ka ba.
Dama ai kunfi kusa ta hannun damarka ce din da sauri hundatu tace da ita haba dai kuma.
Yana sauke yarinyar yake cewa ina sauran yaran ne suke bashi amsa da suna school basu dawo ba tukun.
Ya juya zai fara tafiya sai naji hindatu na cewa dashi amaryan fa tana can ne ya dan juyo yana cewa tana part din ta mana.
To sundundun ke nan haka ashigo kamar munafuka kuma ba ko sallama asan da zuwan ta gidan shiru nayi nasa dama mai hali baya barin halinsa ai.
Abu ne mai wuya su bar hslin nan don ya zama masu jiki ko don kowa da kalar nata kishin a rayuwan ta.
Bai dade da fita ba suma suka watse kowa ya koma part din shi da zama don dama zaman na ranan ne kawai aka dan yi shi .
Ni dai ban sake bin ta kan shi ba dama akwai gajiya a jikina tare da yarana muka kwashi barcin mu na rana sallah kawai na tashi nayi na koma na kwanta abina sai shidda da yaran suka dawo gida na tashi.
Mun dan zauna dasu har bayan magariba ina idar da sallah na fara shirin fita don zuwa duty Aisha na tsaye tare dani tana fada min cewa jiya ma da kyat ta samu daddy yai barci nake cewa sai yayi hakkuri uwarshi ba mai zaman gida bace anytime.
Daddy ya shigo dakin a daidai lokacin da nake magana ina saka rigan aikina daya tsaya min daidai saman kayan dake jikina.
Sannu yaran suka fara mai ban juyo inda yake ba saida na gama na juyo yana duke rike da hannun daddy karami suna magana.
May ke faruwa ne kuma Rahama naga kowa ya shiga gun amarya ke baki shiga ganin ta ba mana tun dazun.
Wani kallo na jefa mai daga inda nake tsaye tare da cewa wa ni daddy wani komawa baya kuma zai kama ni da tazo ta sama a gida bata nemay ni ba sai nice zan je gunta haba dai abin nawa bai kai can ba ai.
Murmushi yayi yana dan girgiza kan shi tare da fadin bakuwar ku ce fa shine kuma wani matsala can daban.
Nace bakuwar ka dai daddy may ye hadina da ita ni kuma da zata zama bakuwa don Allah dai abar ma zancen.
Yace hmmm Rahama Rahama wani lokaci sai kiyi wani abin takar ba ke ba wallahi may ye na komawa baya don kinje kun gaisa kawai da ita.
Nace to yar gidan sarakai ko to talaucin nawa ni baikai can ba tukun na kai hannu na dauki hand bag dina yake fadin wai ina zakine kuma ?
Nace wurin aiki night duty na shiga week din nan na fara ok abin yakai har ki fara baki fada min ba ban sani ba kuma.
Nake cewa kamar ya ban fada ma ba tunda kasan dai aikina ne hakan banda choice akan wani abu kuma.
Na dago alaman zan fara tafiya yake cewa dani Rahama sai na dakata shiru yayi tare da kura min idanuwan shi a kaina.
Nima din kallon nasa nakeyi sai dai ba zan iya jurewa ba na dukar da kaina yace kada ki bullo min da wani sabon halin da ban sanki da shi ba a baya akan kawai na kara aure.
Naga dai ba wannan ne karo na farko dana kawo maki kishiya ba a gidan nan ko yarinyar dabaki ko santa ba, baki san waye ita ba kike son ki kirkiro wani fitina a kan ta kuma.
Nace fita akan kayi aure zanyi fitina ko may niba mata na sama a gida ba ni har ina da bakin magana ni da akai maka dole a kaina ba da son ran ka ba.
Yace ok haka kikace ko nace dashi ai haka din ne ni har wani kadari ne dani gare ka dama matar cushe ba wani power ne da ita ba sai hakkuri don haka duk matan ka ni ba wacce nake kishi ina dai zaman abinda aka dauko ni yi ne kawai .
Kuma ina fatan Allah ya bani ikon cinye nawa kalar jerabawan na rikon marayun da ya hau kaina da karantana.
Yace haka kika ce dai ko ?
Dama ai hakan ne daddy yace no warder naga baki taba kishina ai a rayuwan ki sai dai masu kaunana suyi.
Nai murmushin dole duk da raina a bace yake nace, Daddy nayi kishin hauka na zama wa a gurin ka aiko dana ji kunya kishin mijin da yake na mamajo kullun aure.
Wani sabon suna na samu ke nan kuma a gidan dama tun dawona dana samay ku haka a wuri daya nasha jinin jikina kan akwai abinda ake kulla min a wurin kuma.
Gashi kuma yanzu na gani da idanuwa na tun ba a kwana ba kin nuna a zahiri don ban sanki da saurin sarewa ba irin haka ?
Ban iya magana ba sai duban time din da nayi alaman zai sa na makara ya fara tafiya yana fadin dama mata ba a shedan ku ai na gaskanta hakan yanzu.
Indai akan kishiya ce har kai min mumunar fassara ba damu inda saniyar gaba tasha ruwa kona baya a nan zata sha itama.
Bai juyo ba ya sa kai ya fice daga dakin na sauke ajiyan zuciya nabi bayan shi tare da yara da sukai min rakiya kamar wacce zatai tafiya ba duty zan tafi ba a lokacin.
Ban yafi ba sai da nai masu abinda na saba gaba dayan su har manyan nabawa kowa abinda ya sauwaka a hannuna daga can na hango daddy yana fitowa daga part din amarya da sauri na kawar da kaina daga ganin shi na tayar da mota na bar gidan.
Ashe bayan tafiyana yake tambayan yaran na tafi ne suka ce yanzu na fice daga gidan ai.
Bai tsaya ba ya barsu ya shige wurin shi kai tsaye tare da turo kofan shi ya rufe suma shigewa sukayi wurin mu tare da rufo kofan part din.

********* ********* *********
Washegari a gajiye na shigo gidan ban daki na fada nai wanka tare da cire kayan aikin da na dawo dasu na aje a inda muke tara kaysn wanki na na kullun.
Abinci Amira ta kawo min ta zauna tana zuba min ni kuma ina shiryawa hira muke da ita a kan Jinior muna kwasan dariya sai ga Aisha ta shigo dakin.
Tace mummy dazun ai naga amaryan daddy a waje tayiwa kawayen ta rakiya mummy baki ganta bane fa wata, , , ,
Haba Aisha don Allah rabani da zancen ban haushi ko ma yaya take ai haka yaga abinshi ya dauko ko wa kan sa namiji ina ruwan shi da wani siffa idan ya tashi son mace.
Wai ni mummy may yasa daddy yin aure ne kuma sai fa da Za,id yai min magana kan auren nan da daddy ya kara ranan, cewa da wanda zata aura din.
Nace may kikace dashi ke tace cewa nayi dashi ina ruwan sa bana son yana mun irin wanan maganan again don ba abinda ya shafi rayuwan mu bane.
Nace kinyi daidai Amira don da da haja sai yakai ga fada maki maganan da rayuwan ki zai kai ga baci .
Tace ai ban daukan wanan raini ne mace ta dinga bari mijin ta ko saurinta na zancen yan gidan su a gaban ta tana kyaleshi watarana abinda zai fada sai yafi wanda ya fara fada mata da farko.
Nace kai ashe yar tawa tayi girma da wayone haka lalai daddy nada gaskiyan shi dayace aure zai maki .
Tace kai mummy auren may can kuma don shi yana son aure shine ni zai ce ai min nifa masters nake son na yi fa idan ma na gama.
Ke rufawa kanki asiri da wani karatu can kya karasa a dakin mijin ki idan kunyi aure in kuma kin haihu to shike nan kuma sai a zauna raino.
Da sauri ta fado min a jiki tana rufe min baki tana cewa kai haba haba mummy tana dan jijiga min jikina.
Uban ne ya shigo muryan shi mukaji yana cewa ke ke ya haka kuma uwar taki ce kuma kikewa haka kuma ku ba kwa girma ne wai ?
Da sauri ta daga min a jiki tana dan turo baki tace daddy mummy ce fa nice nai magana da cewa mutum bai awasa da dan shi ne ni haka nake da diyana.
Ke fice min da wanan shirmayn banzan naku don Allah zanga maman ki ne da sauri suka fice daga dakin.
Ya karaso inda nake zaune bakin gado yana kokatin tungumoni a jikin shi da sauri na dago ina kallon shi cikin mamaki nace amma dai kasan hakan bai dace ba don bani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login