Showing 45001 words to 48000 words out of 66328 words

Chapter 16 - Kurman Baki Hausa Novel Complete

da tsoro

"Aeaeaeae........sune wadacan mata na sakar geda ko?"

"Sune madam,sune" basira ta fada tana nishin qarya

"Angama" macen dan sandan ta fada tana fitowa.

Da daya da daya ta qare musu kallo tana muzurai idanunta a kansu

"Ku wuce mu tafi lafiya Allah ko na saka muku karfi" tace dasu

"Ina zaki kaimu madam?,me kuka mukayi?" Zainab tayi qarfin halin tambaya

"Tambaya na ma kikeyi?,to wa yabaki izinin shigowa gida ku dadaki matar gida kuma ku zauna a ciki ba izininta?"

"Mu bamu daketa ba,kuma hakkinmu mukazo karba" zainab ta amsawa matar

"Hey shut up stupid,naga alama kin fisu kwarin ido......hey. ... Samuel shigo ciki" matar ta fada cikin dan daga murya,nan take saiga matashin dan sandan ya sako kai,ya kuma taimaka mata suka tasa qeyarsu zainab sai police station.

****Tunda yace mata zaizo ta kasa zaune ta kasa.tsugunne,kusan ta manta rabon da faisal yace mata zaizo gidansu,ko yanzun ma tafi gasgata cewa aikin malam ne ya ciyoshi,don kuwa tayi dahuwar borkono tsidugu da rubutu,ta saka wuqa a garwashin wuta me dauke da sunansa,hakanan tasa anyi hatimi wanda aka buda aka rubuta sunansa a tsakiya dukka dai gaba daya domin azalzalo zuciyarsa,sai gashi cikin nasara da bakinsa ya furta zaizo din,bayan yazo din kuma yace akwai maganar da zasuyi wadda jikinta da zuciyarta sunfi gasgata mata cewa magana ce ta aure.

Cikin wancan satin data shaidawa isma'il bata aurenshi yayi haquri yace ba komai Allah ya hada kowa da rabonsa sai jikinta dukka yayi sanyi daga baya,har ta dinga ji cewa kamar tayi gwari,kamar bata kyauta ba,kamar tayi wata asara,amma yanzu faisal ya wanke mata zuciyarta fesss da zancan zuwansa.

Kwalliya ta zauna ta dandasa 'yar ubansu,itama umma bata zauna ba,tana ta aike siyo drinks da sauransu. Ta tatse jakarta yau tas,don hatta kudin da yaa bashir ya bata dazun duka sun narke.

Turaren da malam ya bata hadi da kwalli duka ta dauka tayi amfani dasu,da taga akwai sauran lokaci sai ta dauko carbinta ta zauna tana fuskantar gabas ta soma qarasawa don jiya bata samu kammalawa ba.

Ba dadewa suraja ya shigo yace ana sallama da ita. Kafin umma ta amsa ita ta rigata,ta ajjiye carbinta ta dauki mayafinta da duka duka bai wuce ayi dankwali dashi ba ta yafa ta fito kai tsaye ta wuce umman tana cewa

"Bari na shigo da shi"

Wani sanyi ne ya sauka a ranta sanda ta ganshi a tsaye jikin motarsa yana danne danne, exactly irin mijin da takeso. Kallonta yayi yadan saki murmushi ta maida masa

"Bismillah,ka qaraso" ta fada tana juyawa ciki ya bita a baya yana qare mata kallo,don sosai straight gown din jikinta ta fitar da shape din mazaunanta,uwa uba kuma a yanzun da tasha supplement na qiba ta sake cika,kai ba zakace itace wasila 'yar ficika da ake tsokana ba,don har nankarwa yanzu gareta(stretch marks).

Idanu ta juya masa a shagwabe sannan ta miqe tana fadin

"Ina zuwa" sai tayi cikin gida yayin da shi kuma ya bita da kallo. Bayason su rabu amma kuma bai shirya aurenta ba kwata kwata,yanason macen da tafi wanann quality,duk wasu alamu da zasu nuna budewar idanun mace akwaisu a tattare da ita,duk da a iya saninsa bata taba zina ba,amma wasu abubuwan nata suna nuni ne da qarancin tarbiyya.

Bata zauna ba sai data jere komai,komai tanayi ne cikin gwalangwaso iyayi da sanabe shi kuwa yana biye mata. Hira suka shiga yi kadan kadan,komai a shagwabe take masa hadi da kashe ido da karyar da murya kamar ba zatayi magana ba,abinda yasa ya dinga jin feelings a kanta kenan.

Sama sama yaci abincin,duk da baici da yawa ba amma hakan ya mata dadi,tasan indai ya shiga cikinsa magana ta qare,sai daya nutsa yana goge hannunsa da tissue sannan ya dubeta

"Waseela,inaso muyi magana ta fahimtar juna ni dake"

"Tun dazu nake jira naji maganar ai" ta fada tana sakin murmushi gami da gyara zamanta

"Kome zan fada miki ki dauka muqaddarine daga Allah,kuma shine qaddararmu da ni dake,amma kuma abinda zan fada din bawai yana nufin yankewar mu'amala tsakanina dake ba....." Maganarsa ta qarshe ta sanyaya faduwar gaba,amma ta dake taci gaba da sauraronsa.

"Wasila aurenmu ni dake bazaiyiwu ba,saboda yanxu haka kakata ta dage ta tada rigima harda kwanciya ciwo wai sai na auri naana 'yar qanin mahaifi na" wani mummunan faduwa gabanta yayi,qafafunta sukayi sanyi ta kasa cewa komai saici gaba da tayi da kallonsa

"Kiyi haquri don girman Allah,naso qwarai ni dake mu kasance miji da mata don nayi miki irin gatan da ban taba yiwa kowacce mace...... Amma yanzu ma bata baci ba,ni dake inaso muci gaba da mu'amala,ko meye kikeso zan kashe miki zan kuma baki".

Hawayen da batasan yadda suka samu bane suka balle mata,ta girgiza kai cikin alhini tana dubansa

"Amma me yasa duk lokacin nan baka gayamin ba?,ka barni inata bulayi da zaman jiranka?"

"Banason ranki ya baci ne,kuma da farko na dauka zanshawo kanta ashe abun yafi qarfina,kiyi haquri don Allah karkiga laifina" kasa ci gaba da zama tayi,hankalinta tashe kawai ta miqe tayi cikin gida,tana iya jiyoshi yana kiranta amma bata ko waiwayeshi ba,kiran da hatta umma ta jishi,don tana shiga dakin tana binta a baya itama tana tambayarta ba'asi,saidai kukan da takeyi ya sanya ta gaza bata amsa.


**Da sallama ya shiga sashen bayan barowarsa sashen ruqayya kaman yadda ya saba. Adan zabure Khalil da haneefa suka amsa sallamar tasa. Idanunsa ya sauke a kansu sanda suketa qoqarin daga tv plasma din data fado tayi zaman dabaro a qasan tiles.

Ko da bai tambaya ba yasan abinda suka saba ne suka aikata,wato rikito da Tv din wajen fadace fadacensu da basa qarewa,su biyu kacal amma zaka tsammaci sunyi su goma a sashen

"Waye yayi wannan aikin?" Ya jefa musu tambayar yana tsaresu da ido

"Wallahi shine daddy.......qarya takeyi daddy itace ni ba ruwana,turani tayi kai" dukka sai suka kama masa rantse rantse. Ransa yayi qololuwar baci,ya rasa wanne hukunci zaiyi musu?,yo su idan suna da laifi ma ai kaso mafi yawa laifin na uwarsu ne. Matsawa yayi gaba yasa hannu ua daga tv din,ransa ya sake baci da ganin yadda tayi kwatsa kwatsa

"Ina mamar taku take?" Ya tambayesu qasan ransa yana mamakin ya za'a yi abu me girma irin haka ya fado ya fashe amma baka ji ba ballantana ka fito?

"Ta fita tun da rana" Khalil ya fada kansa tsaye. Tsaiwa yayi cak yana dubansa

"Ta fita kuma?,ina taje?" Ya tambayi yaran

"Bamu sani ba,mudau tace mana mu zauna a nan yanzu zataje ta dawo". Wani mugu mugun bacin rai ne ya sauko masa,a duniya cikin manya manyan abinda ya tsana a wajen matarsa satar fita, saboda shike haifar da wasu matsalolin da mai yiwuwa ba zasu taba gyaruwa ba.

TV din ya maida duk da shi kansa yasan ta tashi a aiki,bata barnar da sukayi bane bama yanxu a gabansa,inda zainab ta sanya qafa ta fita bada izininsa ba tunda rana gashi ana shirye shiryen kiran sallar magariba.

Cikin bacin ran yayi alwala ya wuce sallar magariba yana sanya ran kafin ya dawo ta dawo,saidai ko sanda ya dawo din ba ita ba dalilinta,dole ya tasa qeyar yaran suka wuce sassan ruqayya,don kuwa har sun fara jin yunwa,sunce rabonsu da abinci tun da rana,abind aya sake dugunzumashi kenan. Mutum ne shi da yaqi jinin yunwa ko kadan,wannan ya sanya baya bari a hora kowa da ita,koda baisan mutum ba bare cikin gidansa kuma 'ya'yansa.

Tana zaune tana lazumi,alhassan da alhussain harma da iftee na zaune suna cin indomie da sukace sunan sha'awa ta kunna musu qaramin electric da ta ajjiye dama don saboda su,don wani lokacin qananun dafe dafe sukan iyayi,yaran badai qoqari ba,dafa taliya haka,shinkafa fara,ruwan zafi ruwan tea,tun uban yana fada da qorafi har ya barsu.
*_KURMAN BAƘI_* ⚫⚫⚫

*HUGUMA*

PAGE 23

https://chat.whatsapp.com/CKY0xZDtpby6MTkGrPkXLr

*_Assalamualaikum warahmatullah_*

*_Kin dade kina neman gurin da zaki siya kaya amintattu masu quality cikin farashi me sauqi?_*

*_ina marabtarku zuwa cikin wannan gida tare da kasancewa da juna,WANNAN GIDANNA HUGUMA CLOSET NA BUDESHI NE SABODA NA BAKU DAMAR SIYAN KAYA MASU KYAU QUALITY DA KUMA SAUQIN KUDI CIKIN AMINCI DAGA GURINA,MASU SIYAN D'AI D'AI DA MASU SARI,NATION WIDE DELIVERY cikin aminci da izinin Allah,Kayan haihuwa na jarirai har zuwa girmansu,akwai bonanza time to time da nakeyi,ina muna fatan alkhairi ni da ku gaba daya_*


Sallamarsu ta amsa tana binsu da kallo cikin mamakin abinda ya shigo dasu dukka haka a tare

"Ina zainab taje?" Ya tambayeta yana tsareta da kallo cikin salo na tuhuma. Idanu ta zuba masa na wucin gadi kafin tace

"Bata tayi?" Ta amsa masa da salo na gatse,don ba wannan amsar taso bashi ba. Ya karanci ko mene a idanunta,maimakon yayi qasa sai yaji ransa ya sake baci,gaba daya kaman sun rainashi kenan ita da Zainab din

"Kina cikin gidan nan amma abar yara su wuni da yunwa don wulaqanci?,ita ta saka qafa ta fice bata gayamin inda zata je ba,ke kuma kinsan suna cikin gidan a barsu a guri su kadai,yanzun inda ace sun taba wani gurin sun hadawa kansu gobara fa?"

"Uhmmm.....Allah sarki" kawai tace dashi taci gaba da jan carbinta. Hakan data masa ya sake qular dashi,idan ta saba share masa da qin yarda suyi zancan da ya danganci zainab ai issue din yanzu ya banbanta da na ko yaushe ko?.

"Kai alhassan,ku dauki abincin ku qaro muku ku wuce dakinku kuci tare dasu haneefa"

"To daddy,alhussain dauko plate din,ke haneefa bari a zuba muku naku ke da iftee" sai yaja yaran suka wuce.

Kallonsa ya maido kanta bayan yaran sun wuce

"Dake nake fa" kai tsaye ta sake kallonsa,duba daya ya fahimci da yunwa ya dawo daga kasuwa,ita ya kwaso take kuma tunzurashi(muddin kinsan kina barin mijinki da yunwa......muddin kinsan kina barin mijinki yana jiranki saikin kammala abinci to billahillazi daga yau ki taimaki kanki ki daina,yunwa tana jawo fushi,shi kuma fushi mabudin dukkan sharri ne,hanyar da zaki mallaki zuciyar mijinki shine ki kula da cikinsa ki tsare masa shi)

"Wai nikam ajiyarta ka bani?,ko munyi yarjejeniyar zata dinga neman izinina kafin ta fita?"

"To amma ai kece babba cikin gidan ko?,meye amfaninki da har irin hakan zata faru yara su wuni da yunwa a sashen ba tare da kin sani ba?" Dan qaramin murmushi ne da bata shirya ba ya subuce mata,tadan girgiza kai kadan

"Allah sarki,yau kuma ni ake baiwa girman ake bani muqamin na saka ido cikin gidan nan?,bayan togaciya sharadi da iyakokin da aka taba gindayamin a baya?, gaskiya ne.......to kayi haquri ranka shi dade,indai ba fitina kake nemowa ba kuma,yara dai bansan su kadai bane a sashensu,da babu i zaa yi na barsu da yunwa,kafi kowa sanin bada abinci ko dafashi bai cikin matsaloli na.......Abinci ne gashican an basu,ita kuma bansan ta fita ba bansan kuma ina taje ba,shikenan?" Ta tambayeshi tana tsareshi da idanu itama.

Wani numfashi ya saukar,kamar bazai motsa ba sai kuma ya juya ya nufi qofa,tana kallonsa qasan ranta tana hadiye dariya da mamakin halin da namiji,kamar ba'a wannan falon ya zauna ya qidanya mata dokoki da sharadai akan matarsa shalelensa wadda dangi kaf suka aza tazo ta cika gidan da 'ya'ya ba,ta nunawa ita ruqayya cewa ita din cikakkiyar juya ce,kaman bashi ba yanzun ya taho da confidence dinsa zai kawo mata qabli da ba'adi. Tasan yunwa ce take sasaqarsa,ita kuwa tun a wancan zamanin da ya watsa mata qasa a idanu ta daina bashi abincinta muddin ba ranar girkinta bane,gashi kuma shi din ba gwanin cin abinci a waje bane.

Har ya isa dab da qofa wayarsa ta dauki burari,ya dakata yana fiddo wayar,ya sake qufula sanda yaga sunan zainab din.

Koda ya daga wayar saqon da ake gaya masa sai yaji ya girmimi kansa,dole bayan ya ajjiye wayar ya waiwayo yana duban ruqayya,don ita kadaice yakejin zata tayashi tallafar nauyin da zuciyarsa da qirjinsa sukayi. Matarsa ta aure?,matarsa ta sunna a kulle a station.

Sanda yake gayawa ruqayyan ita kanta abun sai ya bata mamaki ya girmimi kanta

"Me tayi har ya kaita police station?,yaushe 'yan sanda sukazo da ni da nake cikin gidan nan banji ba har suka tafi da ita?" Tayi tambayar wadda daga shi har ita basu da amsa

"Wata rigima ya debo na tabbatar da haka" ya fada cikin gamsuwa

"Babu lallai,kaidai ka bincika"

"Wallahi ko kaffara bazanyi ba idan na rantse,nasan halinta ciki da bai,taimaka kizo ki rakani muje" da sauri ta kada hannunta

"Wa?,ni?,daga qarshe zance ya juye ace ni na saka aka kulleta?,Allah ya tsare hanya a dawo lafiya" ta fada tana nade abun sallarta. Haka ya tsaya yana binta da kallo harta gama nadewa ta wuce daki gurin yaran.

Yana tuqi a hanya zuciyarsa tana dada zafi,cikin mintuna qalilan ya isa police station din. Muryarta ya fara cin karo da ita suna sa'insa da wani dan sanda,fadi yake cewa

"Banda aure dake wuyanki da saikin raina kanki,yanzunma kuma kici gaba da cikama mutane guri kiga idan ban saka su Monica sun sassaba miki kamanni ba" tasan yadda yake da zafi iya awannin da sukayi a wajen,don haka ta rage sautinta,saidai kuma bata fasa maganganun ba.

Kunya baqinciki da takaici suka ishi saleem sanda ake karanto masa statement na dalilin zuwansu gurin

"Maganin mata da shiga har gida su doki mace har dakin mijinta" ji yayi kaman zai mutu saboda takaici,wanne irin tonon silili ne wannan?. Banda darajar su haneefa da khalil babu abinda zai hanashi tafiyarta ya barta a wajen ta nemi me belinta,to amma yaran kawai ya tuna ya karbi belinta harda tararta da sukaci,saidai kuma suna fita farfajiyar gidan yace ta nemi gidan zuwa,kada ta sake ta dawo masa gida,yaja motarsa ya wuce abinsa.

Sanda ya koma yaran duk har sunyi bacci a dakinsu,shi Khalil dama cikinsa yana dauka ya haye tattausan gadon alhassan, komai iri daya aka siya aka zuba musu,to amma rashin kulawa da rashin tsafta yasa yaran suke ganin dakinsu alhassan din kamar yafi nasu kamar nasu dakin wata aljannar duniya ne.

Wanka tayi data tabbatar sunyi bacci,ta saka rigar material mara nauyi. Abinka da me yaron ciki sai taji tana son shaqar iskar waje,don haka ta saka qaramin hijabi a kanta,ta dauki qaramin littafin hisnul muslim da taketa qoqarin haddace wasu addu'o'i masu muhimmanci a ciki ta fita waje.(akwai addu'o'i masu tarin muhimmanci a ciki,kada ki zauna ace baki haddace kowacce addu'a ba 'yar uwa,akwai babban hatsari,kaman ka gina gida ne babu qofofi ko winduna).

Bata jima da zama ba taji hon dinsa,yaron gidansu da bai tafiya sai 12 na dare shi ya bude masa ya sako motar ciki. Tana zaune har ya saita parking ya tako zuwa cikin gidan kai tsaye kuma ya nufo sashenta.

Daga kai tayi tana amsa sallamar sa tare da nazarin ganinsa shi daya

"Ya na ganka kai kadai?,ko ta wuce ciki?" Ta tambayeshi tana gyara zamanta cikin kujera. Kai ya dauke gefe guda

"Me zanyi mata?,na karbo ta amma saidai ta wuce gidansu,don ni bazan iya zama da ita ba da wannan abun kunyar da ta jawomin"

"Ban fahimceka ba,kaman yaaya?" Ta tambayeshi fuskarta a dan yamutse

"Eh nace ta tafi gidansu" kai ta ya shiga girgizawa

"A'ah, bazaiyiwu ba,ta tafi gidansu ta barwa waye yaranta?,haka kawai mace na gidanta ka sallameta?"

"Au haka kawai ne ma?"

"Eh mana,don tayi laifi?,waye baya kuskure?"

"Ganganci ne wannan zallar taurin kai da rashin jin magana"

"Hakanan zakayi haquri da ita,amma ba inda zataje,don ban shirya riqon dan kowa ba,koda nan gaba aure ka qara to ka saka a ranka mutu ka raba kai da ita,nima nawa ban gama wahalarsu ba"

"Sai naga ta yadda zakimin dole" ya fada yana shirin wucewa sashenta

"Bafa kwanana bane,kada ka shigarmin gida ka tayarmin da yara" ta fada tana miqewa tsaye.

A zafafe ya waiwayo yana dubanta,yana jin kamar tanason tunzurashi ne,wai wacce irin macace ita?wasu matan suna murna suna jiran irin wannan damar?,amma ita ta samu tana tankwabewa?.

Baikai ga cewa komai ba aka buda can qofar get aka shigo. Akwai wadatar hasken fitilu a farfajiyar,don haka kana iya gano zainab.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login