Showing 18001 words to 21000 words out of 66328 words
Chapter 7 - Kurman Baki Hausa Novel Complete
burgeta ta kuma zame masa silar mallakarta,tana ganin wadannan dalilai kadai sun isa babban dalilin da hajiyan ta cancanci dukkan wani uzuri girmamawa da dagin qafa daga gareta.
Sallamar ruqayyan yaja hankalin hajiyan. Sai ta far gyara zamanta cikin fara'a da kuma d'ari d'ari,kunya da nauyin yarinyar a yanzu takeyi
"Maraba,qaraso ciki mana,na tambayeki abokiyar zaman naki tace kina gida kina girki" murmushi cikin jin nauyi ruqayya ta saki. Hukumullah ta fada a ranta,duniya juyi juyi,wai yau itace hajiya ke tambaya?,ita din da a baya hajiyan kan fadi cewa kada a sake zuwa mata da ita?,ita din da a baya take cewa ta gaji da ganinta,yadda ta ganta jiya haka zata ganta gobe da jibi ma?. Kauda wannan tunanin tayi,ta zauna saman pillow din da hajiyan ta tura mata ta soma gaidata cikin tsantsar ladabi da kunya. Amsawa tayi cikin kulawa itama,ruqayyan ta waiwaya ta gaida sauran 'yan uwanta dake falon. Waiwayowa hajiya tayi ga wata dake a tsaye
"Lu'ubatu a kawo mata abinci ko?" A ladabce ruqayyan tace
"Bari naga me jegon tukunna hajiya"
"Gasu can acan dakin sun cikawa jama'a kunne da hayaniya" dan qaramin murmushi tayi tana miqewa. Tunda ta shigo take jin tashin hayaniya sosai a dakin,saita ratsa ta isa ga dakin.
Za'a iya cewa a cike yake dakin,saidai girmansa ya sanya kowa ke zaune a sake ba tare da an takura ba. Hira suke qwarai ba qaqqautawa,zainab na daga cikin 'yan committee na hirar don da alama ita ke bayarwa ana amshewa. Sallamarta tasa hayaniyar ta ragu,sai idanu kuma sukayo kanta,wasu na amsa sallamar yayin da wasu suka buge da qare mata kallo ciki harda Zainab dake tunanin yaushe ruqayyan ta dinka atamfar nan?.
Raliya dake zaune daf da zainab ce ta tabota murya qasa qasa
"Kin ganta kuwa sai yanzu,lallai ita me aji" waiwayo zainab tayi sannan ta tabe bakinta
"Tana can miji ya maidata jaka,sai data gama girki da gyaran gidan,kinsan ni duk ranar girki ne lallabani yakeyi,kada na gaji dare yayi ya kasa morar dadi,duk ran girkinta a wahala take qarewa,uban kayan ciki ya hadata da dahuwarsa,a dafa mana,mu koma mu kwashi banza ba tare da mun tsinana komai ba" ta qarashe zancan tana kwarara dariya raliya na tayata suka tafa ji kake fass. Dariyar tasu taja hankulan wasu a wajen,banda ruqayya data tattara hanakalinta ga dan jaririn fatima. Fatima mutuniyarta ce qwarai,zata iya cewa cikin dangin mijinta ba wadda suke dasawa da ita kamarta. Tana riqe da yaron tana duba ciwon idanun da fatiman tace kamar yaron yana yi.
Batulu ce dake gefansu ta dubi zainab dake dariya saman fuska,amma qasan zuciyarta kamar an watsa garwashi,don sosai black prince din jikin ruqayya ta tsone mata idanu,sai wani sheqi takeyi da daukar idanu
"Wato ke sauqaqqan girki ake baki ko?,sharp sharp"
"Ashe dai kin gane" ta fada tana watsa mata wani kallo. Dariya batulu ta saki
"Yo ni ai banga wani gata a nan ba,hasalima gani nakeyi kamar ya raina sanwarki ne da iyawarki,shi yasa yake dabara ya kawo ranar girkinta don yasan bazai bata kudinsa ba" da sauri ta waiwayo tana duban batulu,dama akwai 'yar tsama kadan tsakaninsu. Batulun irin matan nan ne da basu barin ko ta kwana,hakanan basu da tsoro
"Eh,ai gaskiyar maganar kenan,sanwarta tafi taki dadi,ai na tabacin farfesun naki,hakanan nasha cin girkin anty ruqayya ko wajen hajiya kuwa"
"Hajiya kuma?" Ta tambayi batulu
"Eh,lokaci lokaci ai ruqayya nada qoqarin wannan aiken kam,sai aka dace hajiyan nason sanwarta" sosai maganar ta daketa,don bata taba tunanin kaiwa hajiya koda silin taliya ba a matsayinta na 'yar 'yaruwarta,hajiyan mada tudu biyu a wajenta,babarta kuma uwarmijinta,bata kuma san ruqayya tana yi ba,asalima ita din tana cikin matan da suke ganin kaiwa uwar miji ire iren wadan nan abubuwan ba komai bane sai tarin bautar da kai. Tunda dai komai saleem yana siya yakai mata ai ba buqatar sai an kai mata dafaffe koda sau daya a wata ma kuwa. Idan Allah ya kawota baqunta taci,idan batazo ba haramiyarta a kuma sauka lafiya.
Ci gaba da hirarta batulu tayi suna gaisawa da ruqayya kuma cikin fara'a da sakin fuska. Sallamar basira ita ta katse sauran tunanin da Zainab keyi ta tattarashi ta watsar,farinciki kuma ya maye gurbin bacin ranta,ganin basira kawai ta tabbatar yau din akwai harka. Muryarta kuwa tafi ta kowa dagawa
"Kaga basira me kayan harka,Allah ya barmu dake ki jima kina yi" mamaki yadan kama ruqayya,don ta tabbatar har yanzu su hajiya na zaune a falon,kuma tayi imani suna iya jiyo komai
"Ai inata sauri hajiya zainab karki tafi"
"Wa?,ni?,Allah ya kasheni musulma naga kayan harka na tafi ban kwasa ba,ke a banza nake zaune a gidan alhaji saleem?,banda wadan nan abubuwan da tuni boka da malam sun jima da tsigeni a gidan" ta fada tana tafa cinya gami da kallon gefen da ruqayya ke zaune a sace tana gogewa babyn idonsa da magani.
Zaman dirshan basirar tayi ta kuma zazzage jakarta,take mata akayi caaa,na waje ma da basusan me ake ciki ba sai gasu da daya da daya suna gangarowa. Yawancinsu amare ne auren watanni masu haihuwa daya zuwa uku hudu. Yaran mata sosai da sukejin ludayinsu yana kan dawo suka cika cacim.
"Duk wadda bata da kudi ma kada ta damu,har adashi inayi,sai na saka kowa a wassuf guruf" basira ta fada cikin jin dadi da farinciki. Tunda take fadi tashi da buge bugen sana'o'i bata taba cin karo da sana'ar dake da wani irin mugun farinjini da kawo zallar madarar kudi a nan take ba irin wannan sana'ar
"Ni wallahi wanann nakeso,da alama aikinsa yafi na dukka magungunan nan" zainab da hankalinta ya dauku ta fada tana daga kwalbar dake cike da wani abu me danqo,an lullube kwalbar da wani rubutun hatimi da wani tsinke a maqale
"Yana da kyau akwai kuma aiki,amma gaskiya duk nan ba kaya me tsadarsa,tafiyayye ne tun daga sakkwato" sai tayi qasa qasa da muryarta
"Kinsan Allah daga gidan malamin aka karbominshi ana kawomin shi na jefashi a jakar nan na fito nayi nan,wannan ma na wata hajiya ne,idan kinaso zan yiwa malamin magana yayi miki naki hadin na musamman" a take Zainab taji qaunar maganin ta shigeta. Kai ta girgiza
"Wallahi ko na uban waye saidai tayi haquri,bani da kudi amma ina da kayan kudi,zan bayar a barmin shi,nawa kudinsa yake?"
"Fisabilillahi a bisa sauqi shi da wannan ruwan....." Ta fadi tana miqa hannu ta dauki wani ruwa da yasha gamje gamje harda su dan tsami da gishiri da sauran tarkace ya koma brown,tana zaune kuma idea din hakan tazo mata
"Idan kika hada aikinsu yafi zuwa dai dai,ki bada dubu arba'in da biyar,amma wallahi tallahi na rantse miki da Allah har dubu sittin na karba a kansa" kai zainab ta girgiza tana juya maganin a hannunta
"Ai kuma na yarda hajiya,ni dama ba kasafai nakeson maganin dari biyar dubu daya ba,ko a baki wani sassaqen bagaruwa ko sassaqen malmo ace wai ka dafa tsumi kasha,tsumin me?,kafin kiga aiki miji ya gaji da jin shuru maqatau?" Ta fada tana daga murya hadi da gatsine duk don ya isa kunnen ruqayya. Ta jita amma ta bawa banza ajiyarta,hasalima dariya ta bata,saboda a wajenta wannan hade haden da zainab ke yiwa kanta tabbas abar tausayi ce ita idan batayi da wasa ba. Kawai fargabarta daya kada ta kwaso abinda zata qunsawa saleem itama kuma ya sanmata.
Cikin lokaci kadan hannun basira ya cika da kudi dumus,aka kwashe kaya tsaf sai ragowa. Idanu ta shiga wulgawa a dakin tanason ganin wanda bai siya ba taja raayinsa,don so take ta fita da kudinta gaba daya. Ruqayya ta hango sai ta dubi zainab daketa shirya kayayyakinta qasan jaka cike da farinciki. Tasan kishiyarta ce amma ita ba ruwanta neman kudinta takeyi,don haka ta dan daga murya
"Hajiya azo a yiwa me gida gyara mana,kayanmu ingantattu ne sai an gwada akan san na qwarai" kamar ta dorawa Zainab guduma aka haka taji,ita basira zata yiwa haka?.
Fatima dake zaune tana cin tuwo gefan ruqayya ce ta zunguri ruqayyan,ba tare data kalleta ba murya qasa qasa tace
"Don Allah kema anty ki saya mana kiyi gyara" murmushi ta saka bata dubi fatima ba tace
"Hajjaju Allah ya bada sa'a" kai tadan sosa
"To amin,amma ko kudi ne baki dashi ai ina lamuni,idan kika gwada yayi aiki kya biya daga baya"
https://chat.whatsapp.com/EKyzZCUEGyRAEGGAnTHmGF
*_KURMAN BAƘI_*⚫⚫⚫
*HUGUMA*
PAGE 09
Murmushin takaici ruqayya ta saki,gaba daya babu nutsuwa ga matar bare ka samu gamsuwar abinda take saidawa
"Kiyi haquri banacin bashi,ma hadu wani jiqon idon da rabo"
"Allah ya qara,mtsweew......banda rainin hankali na gama siyan kaya a wajenki saboda saiki tallatawa kishiyata,idan baki wasa ba billhuwallazi bazan qara siyan kaya a wajenki ba" zainab dake jibgawa basira harara ta fada. Ganin zatayi asara ba wan ba qanin saita tura dankwali gaban goshi
"A'ah me yayi zafi?,idan ma kin ajiye yo ba kanki kika yiwa ba,itama da bata siya ba kanta ta yiwa"
"Gwara data yiwa kan nata,indai itace zatayi miki cinikin maganin mata zaki daina cin abinci da kudin magani a duniya,banda taci kayan ganye taci nama da coca-cola batasan komai ba" Dariya muqarraban Zainab din suka saki. Sarai ruqayya taji,amma hankalinta yana kan fatima suna maganarsu.
"Ba yunwa kika ce kinaji ba amma zaki balle magunguna ki fara sha?" Raliya ta fada tana kama haba idanunta akan fuskar zainab
"Bana bori da sanyin jiki nifa,gobe nike da turaka gwara na watsa tun yanzu subi jikina,yunwa wannan ba matsalata bace,don bata hanani shan magani abuna" tana gama fadi ta fara tuttula na sha da dama sauran da suke na gari.
Sallama aka sakeyi daga bakin qofar,na'ima ce wadda daya ce daga cikin family din nasu,kakanni suka hada dasu saleem,saidai ita babarta 'yar Maiduguri ce. Hannunta dauke da wata babbar jaka tayo sallamar,sallamartata kuma ta hade da qamshi wanda ya cika dakin lokaci guda.
"Nima ga hajata ayimin ciniki bayin Allah" ta fada tana dariya tare da kutso kai cikin dakin.
"Hajiya zee,a zazzagen bakin jaka" ta fada tana murmushi idonta kan zainab wadda tayi tatul da maganinta tana jin tabbas gobe zata sake jarraba sa'arta. Ko da saleem baiyi appreciating nata ba tayi imanin da taimakonsu take zaune a gidan,kuma yana jin dadinta ne,wannan ya hanashi asirin farraqun da ruqayya keta qoqarin yi musu ya kasa kamashi
"Ai kinzo a makare hajiya niimatu,na cinye kudin jakata harda bashi ma a kaina" zainab ta fada tana basarwa,don batajin zata wani tsaya siyan turare bayan saleem ne yake siya musu,wanda yake siya dinma ita idan suka dameta kyautarsu takeyi,ko kuma idan tana da buqatar magani ayi ban gishiri na baka manda,ta bada su a bata magani hankalinta kwance
"Aikodai ban makara ba,shi turare da kike gani shine mace ai,bari na bude miki su ko baki shirya ba kikaji qamshinsu saikin siya"
"Allah fa ni bani siya,karma ki buden qamshinsu ya cikan ciki magani na gama sha yanxu" ta fada tana yamutsa fuska
"Wayyo Allah ya baki lafiya,ko an gamu ne?" Na'ima ta fada tana dariya
"In sha Allah kwanan nan za'a gamun dai" ta fadi tana dan washe fuska,don yanzu duniya kaf burinta shine ta samu cikin 'yan biyu maza kamar yadda ruqayya ta haifa,idan hakan ta kasance kuwa gida ya gama tabbata nata ne kaman yadda ta gama sakankacewa da hakan a baya.
Ta danyi ciniki,wasu a dakin sundan sissiya,saidai ko kwatar wadanda suka siya maganin basu siyi turaren haka ba,wasu dai sun shanshana sun kuma yaba sun aje suna addu'ar Allah ya bada sa'a.
"A'ah, aunty ruqayya?" Na'ima dake shirin barin dakin ta fadi don sai a sannan ta ganta
"Hajiya na'ima inata miqo gaisuwa ai bakijini ba" ruqayyan ta fadi tana murmushi. Sauya akalarta tayi zuwa sashen da take zaune
"Wallahi hankalin yayi gaba" ta fadi tana zama gabanta.
"Bari kiga asararriya,duk gefen kama turaka babu ita,ta saki bishiya gaba daya ta kama ganye" zainab da dariya ke cinta ta fada tana tabo raliya.
"An fara DJ" wata muryar mace data leqo ta fadi,take kuwa kamar ana jansu da majayi suka fara miqewa suna fita da kadan kadan,sai gashi dakin ba kowa daga ruqayya sai fatima dake canza kaya sai na'ima da batulu dake ninke kayan da fatiman ke cirewa.
"Ga turare a siyawa yaaya saleem" na'ima ta fada tana murmushi. Murmushin itama ruqayya tayi
"Ai dole na siya turaren nan,tun kina shigowa naji yamin qamshi" sosai na'ima taji dadi, ruqayyan nada wani irin karamci da bata taba iya kushe abinka.
"Allah aunty?"
"Allah,wancan da kika bani kyauta yamin dadi sosai,yanzu ma nake son dama na tambaya ko kinzo?"
"Nazo anty ban shigo bane da wuri" na'ima ta fada tana fiddo mata da turarukan.
Da gaske turarukan masu kyau ne sosai da tsananin qamshi,guda hudu manya ruqayya ta ware sai humra baqa da fara da kwalaccam sukayi total ta miqawa na'ima kudin. Tana ta qoqarin neman canji ruqayyan tace
"A'ah ki riqe ki siyawa mutuniyata najma biscuit"
"Har haka anty?,na gode sosai,Allah ya qara rufa asiri"
"Ameen ba komai" (don Allah mu rage qanqamo,kowa baya banbararki ke ba'a morarki,motsi kadan kice dangin miji basasonki,sun tsaneki saboda Allah ya miki rufin asiri,ko miji yana wadataki,ba dole su tsaneki ba babu ihsani tsakaninki da kowa?,kowa idan abinsa ya taso saiki kama hannu ki rungume,kice sai ya baki zaki basu bayan kina da wadatar da ba lallai saishi ya baki ba?,karku manta,kyautatawa tana saka d'a ya zama bawa ba tare da ya sani ba,kyauta da ihsani tana saka soyayyarka a zuciyar mutane,Allah yasa mu dace)".
"Ni anty wallahi banji dadin rashin siyan maganin nan ba,bakiga yadda su anty Zainab ke dariya ba da sukaga zaki siya turare"
"Au haba?" Ruqayya ta fada tana dariya sanda take zuba turarukanta a babbar ledar da na'ima ta bata
"Allah,dama sunata gulmar haka kike zaune sakaka,banda asirin ma da kikewa yaa saleem da tuni ya sakeki"
"Hmmmm"batulu ta fadi kawai ba tare da tace komai ba,don itama abin yana bata takaici. Zainab ce 'yaruwarta,amma har ga Allah yadda takejin ruqayya a zuciyarta take kuma burgeta Zainab bata taba burgeta ba,tun zamanin 'yammatanci ma,saboda ko a sannn din Zainab din ta fiya rawar kai da zaqewa,ga shiga abinda shekarunta basu kai ace ta shiga din ba tun a lokacin.
"Ashe ni ban cika mace ba amma ban sani ba,indai sai na siya irin wadannan tarkacen lallai ko bazan taba amsa sunan mace ba,Allah yasa kuma bakwa kwasar ire irensu " ta fadi tana duban idanunsu.
Girgiza kai batulu tayi da sauri
"Nikam bani da juriyar irin wannana abun ma,fruit kawai sun isheni"
"Kefa?" Ta fada tana duban fatima. Dariya tayi a kunyace
"To aunty mu duka duka yaushe muka shigo sabgar ma,haihuwar fari fa nayi yanzu"
"To duk ku zauna" ta fada tana gyara zaman babyn dake kan cinyarta.
Basu musa ba kuwa suka zauna din kowa yana bata hankalinsa
"Fruit kadai basu wadatar dake ba batulu,haihuwarku uku,haka kema Fatima bazaiyiwu ki zauna haka ba,dukkanku don baku da kishiya ne shi yasa a yanzun ba zaku fahimci komai ba,saboda hankulanku a kwance suke,baku da maraba da mutumin dake dakin mamansa a kwance yana bacci" idanu suka zuba mata suna dubanta,sai ta saki murmushi tana gyada kai
"Eh,a baya nayi tunani irin naku,bayan auro zainab naci gaba da rayuwata daga abincina sai fruit,sai a hankali na fara karantar canji daga wajen saleem. Ban rasa tsafta iya girki haquri ladabi da biyayya ba,hakanan bai taba muzantani da ki cusgunamin da gangan ba,amma a aikace ina lure da rawar qafar da yakeyi akan zainab,sai daga baya na gane cewa tabbas dukkan mace tana buqatar gyara,amma gyara wanne iri?,ingantaccen gyara da bai wuce qa'ida ko hankali ba,gyaran da ko meye zataci tasan me taci,kome zata sha tasan me tasha,Allah ya sakawa anty deeja da alkhairi,bazan taba mantawa da ita ba cikin babin rayuwata,itace mutum ta farko data fara dorani akan hanya. Ta tunasar dani hatta iyaye da kakanni suna amfani da magungunan gargajiya gurin gyaran diya mace,kamar bagaruwa,ganyan magarya da sauransu. Inno kakata ta gayamin,yadda muke samun qaruwa(yagewa) yayin haihuwa haka suma suna samu,amma saidai su basusan wani dinki ba,ana gyara mace ta koma fes da bagaruwa da sabulun salo ta hanyar tsarki da shiga ruwan bagaruwan. Na baku misali mana"
"Muna jinki" suka fada a tare saboda yadda bayaninta ya fara musu dadi da tasiri
"Zai yiwu ki siya mota ya zamana kullum kin hawa kina sabgoginki,ko engine generator kuna kunnashi kullum amma ba'a masa service?" Kai suka girgiza a tare alamun a'ah
"Idan hakan ya kasance wataran ba za'a wayi gari ya tashi a aiki ko yana aikin dai amma lallabawa kawai akeyi ba baya bada abinda akeso?"
"Tabbas" batulu ta fadi
"To kamar haka yake a wajen mace,kiyi gyara saffa saffa da ingantattun itatuwa da abubuwa natural,karki tsaya a gyaran qasanki,ko ina na jikin mace yana buqatar kulawa da gyara,saidai kuma komai da zakiyi gyaran dashi ki tabbatar ingantacce ne. Shi kansa engine din idan aka yawaita yi masa service din da juyen mai haka ba gaira ba dalili ba tare da alamu sun nuna yana buqatar hakan ba me zai faru?" Kai batulu ta jijjiga
"Gaskiya akwai matsala, za'a yita sakwarkwatashi ne ana raunata qarfinsa"
"Wani notin ma idan aka kwance ba lallai a iya mayar dashi wajensa a daure,shikenan sai ya fara rawa,sanadin hakan sai wani gurin ya kuma saki" fatima ta qara dorawa
"Yauwa,alhamdulillah,komai idan yayi yawa yana da illa ga jiki da lafiya,hatta natural ways din idan ka dauke 'ya'yan itatuwa da su basa