Showing 15001 words to 18000 words out of 66328 words

Chapter 6 - Kurman Baki Hausa Novel Complete

da kuma abinda takeso.

Miqewa saleem din yayi yace

"Minti daya"

"A fito lafiya" ta amsa masa tana maida dubanta ga tv din dake aiki, wadda rabinta tayi baqi saboda yadda su haneefa suka ragargajeta duk girmanta kuwa,shi kuma yayi rantsuwar bazai canza mata wata ba,saboda bayan wadda ya siya musu ita da ruqayya ya sauya mata wata,wannan din shine karo na biyu kenan da yake sauya musun bayan ta farko.

"Ba inda zashi,yana nan" zainab din ta fada tana juyawa tabi bayanshi dakin.

Aikin da ya gagara bai gama jiya ba yake hada kan takardun nasa sai yaji motsinta,koda ya waiwayo ta fara zare t.shirt da zanin jikinta,ta fara takowa inda yake tana girgiza kafadunta

"Mene hakan?" Ya fada a mamakance,take fuskarta ta sauya kamar yadda bata iya cinye bacin ranta ba

"Ragowar haqqina nake buqata,kuma kaima aina lura bawai ka gama nutsuwa bane" Dariya ce ma taso kamashi,yadan kauda kai daga nan yana jiyo yadda smell na jikinta ya canza da alamu tana da buqatar tayi wanka amma ta kasa gane hakan. Abu na biyu kuma ya fahimci tana so ne tayi abinda zata batawa ruqayya lokaci,saidai kash bata iya durfafar miji da salon zai dauke masa hankalin ba tare dashi kansa yasan ya akayi hakan ta faru ba

"Lokaci ya fice yanzun kema kin sani"

"Eh amma hakkina ne ai a wuyanka ko?" Tsaiwa yayi yana kallonta kafin daga bisani ya girgiza kai yaci gaba da hada takardunsa. Maganganu ta shiga yi na bacin rai har ya gama,ya miqe tsaye yana zuba mata idanunsa abinda ya sanyata rage kaifi bakinta

"Kiyi qoqari ki tabbatar ba wani abun kika zubamin jiya ba,don muddin na gano hakan kinsan sai na hukuntaki tabbas!" Ya qarashe maganar yana kewayeta ya fice,saboda yasha mata gargadi akan hakan,yayi dukkan abinda zaiyi ya koya mata hade haden vegetables din da ruqayya keyi masa da suke da matuqar amfani ga lafiyarsa da auratayyarsu,amma tsabar son jiki ta kasa tsaiwa ta dinga yi masa a kullum kamar yadda yake da buqatar ya dinga ci din.

Har wani sakakken numfashi ya saki sanda suka isa sashen nata,wata ni'ima da nutsuwa suna saukar masa. Ruwa me dumin sosai ta hada masa kamar yadda tace,koda ya sanya hannu cirewa yayi da sauri yana dariya

"Wai ashe da gasken kike gasanin zakiyi?,na dauka kin fada ne kawai saboda kishi?" Yadda ya rutsata da ido yana tambayarta sai abun ya bata dariya,ta murmusa tana qoqarin danne kishinsa da takeji yana cin qasan zuciyarta

"Amma dai kafi kowa sanin ruqayya,idan tace eh tana nufin eh din,idan tace a'ah shima tana nufin hakan" murmushi ya saki yakai hannu yana shafar dukiyar fulaninta da yanayin dinkin da akayi mata ya fidda shape dinsu sosai. Har yanzun yanajin wannan yanayin a jikinsa,saidai hankalinsa na kwanciya idan ya tuna ya fado hannun da zai samu dukkan kowacce irin nutsuwa.

"Naji sashen shuru ina duka yaran"ya tambayeta sanda take taimaka masa yana fidda kayan jikinsa don ya samu yayi wankan,har yau har gobe muddin tana free irin haka itace ke taimaka masa da wannan,hakama shirin muddin ta gama nata ayyukan

"Na korasu gidan kakaninsu don nayi jinyar daddynsu da kyau" wafta ya kawo mata,ya jawo qugunta ya riqeta suna musayar numfashi. Idonsa cikin nata,hakanan duk wani fitar numfashinta sai ya hado da sassanyan qamshinta. Sai ya tuna wata rana irin hakan da ya gwada yiwa zainab hakan,daga qarshe da hannunsa ya saketa saboda bala'in rashin tsaftar baki,wanda hatta da numfashinta da irin wannan yanayin yake hadowa ya fito.

"Wannan jinyar ta tsaye miki a rai ko?,to kada ki damu,kema yau ki daure ki jinyatani hakan mana" ya fada yana kashe mata ido daya. Hannu biyu ta sanya ta turashi baya tana dariya

"To bismillah ko an gaya maka raguwa ce?,ai dai kafi kowa sanin wace ni" dariya ya saki yana kai mata cafka,sai ta zame ta fice,don sam ba zata yarda ya rabeta daga barowarsa sassan zainab ba,tafi son ya tsaftace jikinsa duk da fes yake,amma hakanan take da wannan kishin a zuciyarta.

Kafin ya fito ta hada masa hadin salad na musamman,bricole,spinach,cocumber,parsley cabbage lettuce cornflower,ta yayyankasu ta wankesu da ruwan gishiri,ta diga masa mai kadan. Tuni ta haramta zuba maggi me yawa a abincinsa bare akai ga farin magi,don haka gishiri ta zuba mishi kadan da yaji wanda tasirinsa bazai fito ba bare ya dameka. Blender dinta ta jona ta markada kabewa dabino da kanunfari yayi laushi qwarai kaman yoghurt ta wadatashi da zuma.

Duk inda ta gifta saita aje masa qamshinta,hakanan tasirin maganin jiya da bai bar jikinsa ba ya dinga tsomoshi. Sai data gama shirya masa komai sannan ta dawo ta zauna tana dubansa cikin wani lallausan kallo data aje kawai saboda shi,zata iya cewa duk duniya ba wanda ya taba ganin makamancin kallo irin wannan a idanunta saishi daya tal

"Ga abinci ya kammala,ka fara tabawa kafin na dora girkin dare" kumatunta yaja yana murmushi

"Emergency kika hadamin ne?,naga harda pumpkin smoothie" farrr tayi da idanunta tana murmushi

"A'ah,ya za'a yi mu hadu muyita tara maka gajiya?,so nake kaci ka qoshi ka kwanta ka huta,qwarin jikinka ya dawo" mintsininta yayi kadan yana murmushi, muryarsa qasa qasa yace

"Ban yarda ba,tunda kikace kin tafi gidan aunty deeja nasan there's something special yau,naga wani abu me zaqi zaqi ma a fridge dinki" idanu ta fiddo tana kallonsa

"Sai kuma kasha?" Kai ya girgiza yana langabe mata shima

"Dandanawa kayi nayi fa,Allah bansha ba" shagwabe masa tayi sosai kaman zata saki kuka

"Amma dai daddynmu kasan ba kyau bincike dai ko?" Dariya ta qwace masa

"Ni ruwa naje sha ba bincike nayi ba" ya fadi yana daga hannunsa sama duka biyun yana dariya

"To nidai na yafe yau din,an baka hutu" ta qarashe maganar idanunta nakan labulen window dinta dake ta veranda din waje. Idan idanunta sun nuna mata gaskiya shatin tsaiwar mutum take hangowa,karon farko kuma taji zuciyarta tafi kakata da cewa zainab ce. Sau uku qanwarta da maqociyarta suna gaya mata Zainab din tana mata labe,amma bata taba daukan abun da muhimmanci ba tunda bata taba kamata ba.

"Ni kuma ban yafe ba" ya fada yana matsa hannunta dake da wani sulbi da taushi.

Tana sane ta saki wata shagwababbiyar qara idanunta nakan labulen

"Allah dear......ka bari don Allah,tun ba'a yi nisa ba kada kasa na kasa komai"

"Na bari,amma mu fara salla tukunna kafin muci abincin"

"Yes sir" ta fada tana miqewa. Sai data fara wucewa kitchen ta fiddo sumammen ruwa ta juye a wata roba sannan ta wuce toilet ta shirya masa ruwan yadda zaizo da dumi bayan tayi tata alwalar ta kuma shimfida abun sallah sannan ta zarce kitchen din.

"Na daina raga miki" ruqayya ta fada qasa qasa tana dariya mugunta hannunta dauke da robar ta dawo falon din.

Sake gyara tsaiwarta tayi da kyau zuciyarta na sake tafasa da bacin rai. Ba zata bar wajen nan ba har sai taji uban me dame sukeyi tas a cikin falon. Gumin fuskarta ta goge tana jin kamar ta rushe da kuka. Babu ta yadda za'a yi ma ta yarda cewa ruqayya ba asiri ta yiwa saleem ba,don bataga wani abu guda daya da zaisa saleem din ya dinga wannan rawar jikin a kanta ba,bayan itace tafi cancanta da hakan.

Ai bata dire tunaninta ba taji saukar ruwan qanqarar da ya kusa tafiya da numfashinta gaba daya. Ta taqarqare ta kunzuma ihu ta mance ma shaf da muhallin da take a tsaye. Da sauri ruqayya ta bankade labulen da qofar gaba daya ta fito tana salati

"Jar uba!,ni kika jiqa da ruwan qanqara,wallahi tallahi yau ko sama da qasa zasu hade bazan yarda ba" ta fada tana gyara daurin qirjin da tayi a saman zanin atamfar jikinta. Wata dariya ta tasowa ruqayyan yadda tayi tsamo tsamo da ruwan har tana rawar dari,amma dai sake gyara masoyinta takeyi wato daurin qirji

"Aike za'a tambaya,me kikeyi a nan gurin?" Tambayar data daukewa Zainab din wuta difff musamman da tambayar ta fado dai dai sanda saleem yake fitowa daga falon saboda ihun zainab din daya riskeshi har bandaki.

Ido tahau rabawa, ganin yadda shi da ita gaba daya suka zuba mata ido suna sauraren amsarta sai tahau tafa hannu

"Ni zaki yiwa wannan tambayar?,ko kin manta yadda gidan nan yake naki nima haka yake a wajena?,ko wucewar ma mutum bazaiyi ba saboda window din daki ne?"

"Wucewar ce harda kujera?" Saleem ya sake jefa mata tambayar yana nuna mata kujerar data aje a wajen. Dif wuta ta dauke mata,yayin da shi kuma yaci gaba da kallonta yana hadiye wani abu me tauri.

"Allah ya kyauta" ruqayya ta fadi tana kewayeshi ta wuce ciki abinta,ko babu komai ya gani da idanunsa,bata bude baki ta fadi ba bare ace sharri ne da yarfe irin na kishiyoyi.

Batasan yadda suka qare ba,saidai har alwalarta ta bushe bai shigo ba,sai daga bisani ya shigo yana ware hannun rigarsa,fuskar nan cike fal da bacin rai,saidai bata bari hakan yaci gaba da damunsa ba ,don bayan sun gama sallar sai data tabbatar ta mantar dashi komai ta hanyar biye masa ya sauke sauran nauyin da Zainab ta dibga ma cikinsa ba tare daya sani ba,sannan ta shiriritar dashi suna wata daddadan hirar gado wadda ta musammance data warewa lokuta irin wannan. Lokutan da suka gama kasancewa da juna a lokaci irin wannan da babu kowa daga shi sai ita. Yanason irin wannan moment din da take creating musu,yana sakin jiki qwarai yayi sirrika masu tarin yawa da ita,suyi shawara da juna ta kuma sauke masa damuwar da yakejin duk duniya ita daya keda wannan power din.
*_KURMAN BAƘI_*⚫⚫⚫

*HUGUMA*

PAGE 08


GIDAN HAJIYAR MATA daya daga cikin jerin gidaje guda goma sha biyar kenan dake layin.

Faffadan gida ne dake da soro makeke guda,yalwataccen tsakar gida dake da bishiyar mangwaro a tsakiyar gidan,sai dakuna guda biyar manya,wanda kowanne cike yake da kayan jere na alatu wadanda suka fi qarfin a zubasu a gida kamar wannan,duk da gidan fes yake,baya rabo da fenti da 'yan gyare gyare kodon saboda baqi dake yawan zirga zirga a gidan.

Kusan duk sanda zaka shiga gidan zaka samu dakuna hudun nan a rufe,musamman uku daga cikinsu,har gwara dayan ana yawan budeshi saboda baqi dake zuwar mata. Daki guda kuwa kulli yaumin yana a bude,saboda shine ainihin ma'assasar neman kudi da dukka wata taqama na hajiya zeena din. Akwai masu aikin dake zirganiya daga dakin zuwa tsakar gidan sanye da riguna koraye masu dauke da tambarin HAJIYAR MATA musamman idan ta kammala hada magungunanta za'a yi packaging.

Saidai ko su din akwai wasu kebantattun lokutta da bata barinsu shiga dakin har sai ta kamala hada magungunanta saboda boye sirrin kasuwa kamar yadda takance

"Mutane ba amana,kasuwa ai sirri ce"

Ko a yau din ma masu aikin nata na zaune a tsakar gida suna hirarrakinsu tare da jiran hajiyan dake dakin ta sallami baquwarta ta kuma gama hada magungunan nata su shiga suyi aikinsu,don yau din akwai kaya da yawa tace musu akwai matar da zata sara.

Daga cikin fallen babban dakin da yafi kowanne girma mata ne zaune saman kujeru guda biyu,dayar kana kallonta kasan itace matar gidan,don kanta daurin ture kaga tsiya ne tayi,qwaiwayayyen gashinta ya bullutso ta qasan daurin,yayin da d'ayar ke sanye da hijabinta saidai ta sabashi saman kafada

"Shi carwash din yanzun saidai botiki uku?,botiki biyar naso saboda zanyi sabulun tsarki dashi me yawa wallahi"

"Masu nema ne sukayi yawa hajiya,kuma kalolin da za'a sakawa koren ne babu,ke kuma koren kike da buqatar yayi ko?"

"Eh mana,yo banda abinki ta yaya za'a yarda sabulun magarya ne babu koriyar kala?"

"Ba matsala zanyi qoqarin hada miki cikin satin nan in sha Allahu"

"Shikenan,zan jalauta haka" ta fada tana ninke takardar lissafin nasu,ta jawo wata lalita a qugunta ta zuge ta lissafo kudade ta miqa mata

"Gashi babu kare bin damo,idan kin kawo sauran koren na baki kudinsa iya shi kadai" kudin ta jujjuya a hannunta

"Haba hajiya,na zaci zaki bani kudinsa shima kafin na kawo"

"Kije kiyimin irin ta wancan lokacin ko?,saiji nayi kin bawa wata,to kar nake kallonki"

"Karmuyi haka dake mana,duk zaman nan ace ba aminci tsakaninmu?,kudin nan fa kafin ki tashi a nan na tabbatar kin maida ninkin baninkin dinsu" daurin dankwalinta ta sake turowa gaba ta bararraje tana jawo wani farin botiki dake cike da garin masara me azabar fari da laushi da yasha tankada da kyau,hakan ya nunawa matar da take kira da saude ba zata cika mata din ba

"Kinga miqomin botikin zumar can" dariya saude ta sheqe dashi

"Zuma ko dafaffen sugar cakude da dan zaqi?(sweetner)" Baki ta tabe cikin nuna halin ko in kula

"Koma menene ke kika sani,miqomin nayi nayi na hada,basira zata shigo sari tace akwai gidan sunan da zata je yau din"

"Hajiyar mata hajiyar mata" saude ta fada gana dire mata botikin.

"Ahto,meye amfanin sana'ar da babu riba,tunda dai sunyi imani kuma yana musu aiki aimu alhamdulillahi......ina fiddausi?,zoki hada dan matsin nan yasha iska kafin anjima" ta qwalawa biyu daga cikin amintattun masu aikin nata kira.

Wani kwali ta jawo dake dauke da zanen mace babu komai a jikinta sai pant,an fiddo abinda zai nuna maka tallan abubuwan da zasu qara masa girma akeyi

"Balle capsule dinnan ki watsa a hadin garin qara girman nonon can za'a kai niqa"

"Kinsan sirrin kasuwa hajiya" saude dake dariya ta fada

"Yo mu din na wasa ne?,ke kinga yadda mata suke wasoson garurrukana?,to kina sha zai fara aiki,su dama haka sukeso,wannan zai fara miki aikin da idan hadin Allah kikayi musu sai yayi wata uku mace tana sha bataga canji ba,yanzu zakiji an bata miki kasuwa ana cewa bashi da kyau,bayan shine me kyan,tsabar gaggawa ce dasu to kinga gwara kawai kayi musu abinda sukafi ganewa,wanann garin duk yawansa bazaikai jibi be qare ba" ta fada hautsina garin masarar dake cikin botiki,da niqan aya da saqe saqen da batasan adadin yawa da kuma dame dame ta game waje daya ba. A hakan garin masarar yafi yawa,ganin yayi haske da yawa saita debi garin kala me dan duhu ta watsa

"Yauwa,sai a dauka tsabar soyayyar ayace da ta wadata" hajiya ta fada a ranta tana qissima yawan ribar da zata fitar a wannan hadin da tayi.

*******A nutse ta kammala komai,hatta da abincin dare harda farfesun kayan cikin da saleem ya aiko daga kasuwa. Ta shirya tsaf cikin atamfar black prince me kyau data dace da kalar fatarta. Wani irin sassanyan dressing,ita din gwanace gun hada ado da yakan dace da kowacce kalar unguwa. Hannunta riqe da key din motarta ta fito babban falon gidan da zai wuce da ita harabar gidan.

Sauka idanunta yayi akan sassan zainab. A rufe yake gam,ta kusa awa hudu da tafiya tuntuni. Aike ta dinga yo mata ba qaqqautawa akan ta fito su tafi,ita kuma ta aike mata ta tafi kawai ta taho. Hakanan al'adar zainab take,indai taji batun fita gurin wani sha'ani ko taro jikinta har rawa yake,ba kasafai ranar abincinta ke ciyuwa ta dadin rai ba idan ma ta tsaya tayin. Wani murmushi ya qwace mata data tuna wani abu,ta girgiza kai kawai tana isa ga motarta,tabbas ta yarda wasu matan basu da wayo kam.

Minti talatin ya kaita unguwar,suna akeyi na 'yar qanwar mahaifiyar saleem din. Kana gani kasan gidan cike yake,don kuwa duk da gidan yalwatacce ne amma har ta waje kana iya hango zirga zirgar jama'a. Tunda ta ajjiye motarta ta fito taketa gaisawa da mutane cikin mutuntawa da ganin kima,can qasan zuciyarta mamaki yana dan mamayarta,tana sake gasgata cewa tabbas ME HAQURI YAKAN DAFA DUTSE HARMA YASHA ROMONSA. Mutanen da wasunsu a baya suka daina magana da ita,wanda ita tasan ba komai bane ya jawo hakan sai saboda zainab da saleem ya auro da suke ganin 'yaruwarsu ce sunfi kusa da ita akan ruqayyan,duk da tarin kyautata musu da ruqayyan keyi amma suka shafawa idanunsu kwalli,sai gashi lokaci yanata nuna kansa, gaskiya kuma tanta halinta bayan ta watsar da damuwar kowa ta maida hankalinta ga addu'a da mu'amala da kowa da zuciya daya.

Gaisawa ta dinga yi da mutane,bata kuma zauna ba har sai data lalubi dakin da surukarta take da wasu daga cikin qannen hajiya din.

Da sallama ta shiga cikin kamala da kuma kunyar da har yanzu batajin ta gushe a tsakaninsu,duk da irin abubuwan da suka faru a baya,da irin ababen da ita hajiyan tayi mata masu dimbin yawa dake da soya zuciya da saka me rauni ya tsani mutum. Taji babu dadi ta kuma koka matuqa da gaske,saidai ko sau daya bata taba jin ta tsaneta ko zata iyayi mata rashin kunya ba,saboda me?. A koda yaushe tana duban hajiyan a matsayin wani tsani na dukka matakin da tahau a rayuwarta,duk tsiya duk kuma inda za'a je a dawo itace dai ta haifa mata saleem din da zuciyarta ke matuqar so take kuma son ta kyautata masa wanzu tare ila yaumil qiyamati,ta bashi tarbiyyar da har ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login