Showing 51001 words to 54000 words out of 66328 words
Chapter 18 - Kurman Baki Hausa Novel Complete
A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING ZAFAFA BIYAR*β€βπ₯β€βπ₯β€βπ₯
*_KURMAN BAΖI_*β«β«β«
*HUGUMA*
PAGE 25
Ranta a bace ta soma sauya kayan jikinta,cikin ranta tana tunanin abinda Zainab keso a tattare da ita. Ta gama kintsawa ta dawo falon don su bude kyaututukan yara kafin daddynsu ya dawo,abundai bai yiwa wasila ba har sai da ruqayyan ta sake magana da ita
"Wooo wasila!......abinda tayin kina nufin ba wani abun ta taka ba a qasa?,idan kare yana haushi ai baka kulashi,ka barshi idan ya isa ya kawo maka cizo mana ya gani?,mai gidan ai zai dawo ko?,zaiga kuma komai,kanta ta haqawa rami ai ba ni ba" daga wannan ta watsar sukaci gaba da sabgar gabansu.
Tafi awa tana sauraren ta jiyo ruqayya ko wasila ko wani nata yana maganar ta janye mota ko abinda ya danganci haka,ta rantse da Allah yau din sai tayi mata wankin babban bargo,saita basu mamaki(ni kuwa nace hmmm,bayan wanda kike basuπ),haka ta qaraci tanadin masifarta ta haqura ba tare kuma data janye motar ba.
Tunda akace mata daddy yana kiransu a falon tsakiya tasan ba lafiya ba,tunda ya saba duk wadda ba girkinta bane yana leqawa ya sameta har sassansa su gaisa bayan ya shigo gidan sannan ya wuce sashen me girki.
Ta gama alwalar magariba kenan duk da akwai sauran lokaci,sai ta qarasa gaban madubi ta tsane fuskarta ta shafa lotion kadan sannan ta shafa powder,sannan ta qara mulke jikinta da oil perfume ta fito.
A tsaye ta samesu shi da zainab din tana riqe da qugunta. Ta dauki idanunta daga kanta kamar bata ganta ba ta zagayeta ta tsaya daga damansa
"Daddy yada haka a tsaye?,ka zauna mana kaman ba cikin gida muke ba?"
"Ba ruwanki da tsaiwarsa ko zamansa tunda ba ranar girkinki bane wannan ba huruminki bane" banza ta baiwa ajiyarta ta janye masa pillow din dake kan kujerar tace
"Have a seat please daddy" tayi maganar a sanyaye cikin tausasawa ta yadda har tsakiyar zuciyarsa sai da yaji wani sanyi ya saukar masa,ya kuma shiga kokwanton maganganun da zainab din ta tare shi dasu bayan yabi ba'asin me yasa akayi wrong parking,ga wata motar kuma a qofar gida basa tsoron yara su kakkarceta.
A nutse ya zauna din yana sauke numfashi can qasa,rashin ganin fuska daga kowannensu ya hana zainab din ta sake cewa komai,saidai ta qulu iyaka
"Me ya hada zainab da ke da wasila?" Yayi tambayar calmly
"Wani abu tace ya faru?,nidai a iya sanina bansan komai ba,ko magana ta fatar baki basuyi ba bare ace ma wani abu ya hadasu"
"Dole kice haka mana,ki sakata tana sakarmin baqaqen maganganu tana min kallon raini,to wallahi kashedint......."
"Ke da Allah malama dakata,da mijina muke magana ba dake ba,idan kuma kin gwammaci nayi magana dake din to daidai nake dake,ki kiyayeni ki fita idona don ni ba sa'ar yinki bace.......shashasha mara kunyar qarya da wofi ke duk tsiyar da kika shuka kina da bakin yin magana inda ace ke din me kunya ce?,kina nufin inda na barki da wasila zaki tsira ne?, wallahil azeem da wannan rashin kunyar da kika tsaya kina yima baki isa ki yita ba"
"Ya isa ruqayya......"
"Ai ba dogon magana na fito nayi ba dama,ka jawa matarka kunne,taci gaba da ji da abinda ya dameta,don ni bani da lokacinta ina da masu jimin da ita idan hakan ta kama" tana gama fada tayi gaba abinta
"Kaji ko?,tabbacin ita ta sakata tayimin diban albarka"
"Ya isa haka da Allah" saleem ya fadi cikin gajiya da soki burutsun qorafe qorafen zainab din.
Tayita zuba idanu ruqayya ko zataji wani abun ya sake tasowa amma taji shuru,batasan yadda suka qarke ba,don ko abinci ma ranar cewa tayi bata ci,qememe taqi fita,saima tayi kwanciyarta ta tura yara. Koda ya shigo da kansa ma laga laga tayi tace masa batajin dadi haka ya koma. Wannan ya bata ran zainab,don ta shirya abubuwa masu yawa a zaman cin abincin amma ruqayya taqi bata wannan damar,don tun daga ranar ma sai ta janye zaman cin abinci,idan ta gama zata shirya musu ta koma sashenta,idan ya shigo zaiyi qorafi takance yau batajin dadin cikinta ko qamshin abincin ya cika mata ciki ba zata iya ci ba don zata iya amai. Sai ya zamana duk ran girkin ruqayyan suna gama cin abincin yake tattarawa ya wuce sashen ruqayyan sai kuma da asuba idan ya shigo tayar dasu sallar asuba.
Yadda taga hankalinsa kamar yana sake karkata ga ruqayyan ya tashi hankalinta matuqa,ta kasa zaune ta kasa tsaye,hankalinta ya kasa tsaiwa guri guda. Hatta dasu haneefa yanzun duka sukeci a wajenta,ta kasa zama da kowa lafiya saboda tana ganin ubansu kamar baya yi mata adalci.
Komai da yasan zasu buqata ya kammale waje daya kafin tafiyarsa,mutum ne tsayayye wajen kula da hidimar iyali da buqatunsu,ya danqawa kowacce adadin abinda zata buqata na cefane da hidimar gida,don ba zasu dawo ba sai ranar jajiberin sallah.
Tuni zainab tayi nisa wajen hada kudin dinkin da za'a yi mata,ta zabge fiye da rabin kudaden da saleem ya bata ta sakasu a lissafin. Ta riga ta tsara abinda zata diba cikin kayan abincinsu ta saida ta sake hada wasu kudaden masu kauri,wannan karon sam ba zatayi wasa ba,tanason sanda saleem ya tsoma qafarsa a qasarnan ya dawo hannunta,ya koma mata bita zai zai,tanason ranar daya dawo dakinta daukacin al'ummar gidan su shaida,muryarsa tayi kururuwar da kunnuwan ruqayya zasu jiyo,ta gogewa idanunta dukka wani sauran bacci da ya rage mata,bayan wayewar gari kuma taci karo da gagarumin sauyin da zai ruguza duk wata kissa tata da take taqama da ita. Tanason ruqayyan ta zame masa kamar namiji dan uwansa,duk sanda zasu kasance da juna ya dinga jinta tamkar abincin da babu maggi ba gishiri,tayi imanin indai wannan buri nata ya tafi a haka komai zaizo mata a yadda takeso.
Ana ya gobe zasu tafi ta yiwa wasila waya tazo ta tayata zama,saboda yanayin laulayi,kuma tayi imanin ba wanda zai iya zama da halin Zainab dai dai da halin nata sai wasilan,saidai ta sanya ta bawa umma wayar cikin zolaya take cewa umma
"Zan dauke miki auta har zuwa sallah,amma ki jawa auta kunne wallahi kar tazo ta zaka kishiya ta babbakani" Dariya umman ta dinga yi,saboda tasan barkwancin wasila da ruqayya baya qarewa.
Da daddaren ranar cikin girkin Zainab yake,wanda a washegari inda yana qasar nata girkinne. Tsaf ta shirya qananun jakankuna data masa qananun siye siye da tasan zaya buqata a can,ta kuma yi masa packaging na qananun snacks da ba zasuci masa guri ba ire iren wadanda tasan yana so.
Bata jima da fitowa a wanka,don wani dogon bacci tayi,har ya shigo nemanta ya fita ma bata sani ba. Wata sabuwar doguwar riga ta siya me sulbi cikin ribar business dinta. Sunyi nacin rigar ita da zainab sosai,shima kuma yaso siya musu don tayi masa kyau amma wasu hidimomin suka shigo ciki sukayi gaba da kudin rigunan kusan 60k. A lokacin har sabani suka samu shi da zainab akan hakan,tace ya sanya musu rai dama dai baiyi niyyar siya musu ba. Wannan kalmar ta qona masa rai matuqa da gaske,saboda shi din duk wanda ya sanshi yasan me fada da cikaawa ne,muddin kaga bai cika ba to akwai babban dalili.
"Bari naje gurin daddynsu muyi sallama,don shida na safe sun fita a gidan nan"
"Okay bari nima na amsa wayar wannan dan anacen" ta fada tana miqewa. Kai ruqayya kawai ta girgiza,dole tayi bakin qoqarinta adan zaman nan da zasuyi da wasila ta canza tunaninta.
Yana daga cikin bedroom dinsa yana hada kaya zainab na zaune a gefe tana qara masa wani sabon lissafin,don so take kota halin yaya ta sake samun wasu kudaden da zata maida asarar da basira ta janyo mata,ta hada kudin dinkinta tsaf,ta kuma fidda kudin hidimar gidan dai daya bayar.
Sallamar ruqayyan ta ratso har dakin,ya amsa yana bata izinin shigowa,saidai dan tsayawar da tayi tana gyarawa haneefa assignment dinta na islamiyya ya bawa zainab damar yin magana
"Ya muna daki zakace ta shigo mana fisabilillahi?" Bai kalleta ba yace
"Bedroom dina nace ta shigo ba naki ba,ke shigarki nawa bedroom dina na sashenta?,kin taba ji tayi qorafi?" Tasan magana ya yaba mata,lokacin amarcinsu idan taso tsiya ma tana tuburewa ne tace tsoron sashenta takeji a nan zata kwana,wani lokaci saidai yabar mata nan din su kwana a bedroom din ruqayyan. Haka taci gaba da faruwa har sai ranar da ruqayyan ta gaji tayi maganinsu sannan aka samu sauqi.
Da sallama ta shigo,idon zainab ya fara sauka a kan rigar jikin ruqayyan. Tashi daya fuskarta ta sauya,ta gane rigar sarai,tashi daya zuciyarta ta bata saleem ya zagaye ya siya mata,ko kuma ya bata rabin kudin a bayan idonta.
"Aiki kake da kanka" ruqayya ta fada tana murmushi sannan taja stool ta zauna tana masa barka da dare. Cikin kulawa ya amsa duk da yana takatsantsan,yasan tsaf zainab din zata jawo wani maganar da rayuka duka zai baci.
Tana so ta saka masa hannu a gyaran kayan amma tana gudun magana,don duk hirar da sukeyi zainab din na wajen,ita bata tanka ba ita kuma bata fita ba,hakanan bata tayashi da komai ba.
Ta dan jima suna hirarrakinsu sannan ta miqa masa ledojin
"Gashi daddy ba yawa" ita da ba ita aka bawa ba amma ta riga saleem din sanya idanunta akan ledar cikin son bin diddigi da tantance meye a ciki.
*_ZAFAFAN DAI_*π«‘π«‘π₯π₯π₯π₯
*_NEW HOT BATCH 2024 DA ZAI TASHI KANKU FIYE DA NA BAYA IN SHA ALLAH_*π₯΅β€βπ₯β€βπ₯β€βπ₯π₯π₯π₯
*_KASANCE D'AYA DAGA CIKIN ZAFAFA FAMILY NA WANNAN SHEKARAR TA 2024 TA HANYAR SIYAN TIKITIN SHIGA GROUPS NASU NA ZAFAFAN LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA_*
π₯π₯π₯π₯π₯π₯π₯π₯π₯π₯
_WANNAN DIN WATA DAMA CE TA MUSAMMAN A GAREKU WAJEN ZAMOWA CIKIN AYARIN IYALAN ZAFAFA_
*_LITATTAFAN SABUWAR SHEKARAR SUNE KAMAR HAKA_*
*KWANKWASON JIMINA miss xoxo*
*TSUTSAR NAMA Billynabdul*
*GUDUN K'ADDARA Huguma*
*AMEENATU Mamuhghee*
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA LALE DA MASOYAN ZAFAFA BIYARππ―π... ZAFAFA BIYAR NAKU NEπ_
*_KURMAN BAΖI_*β«β«β«
HUGUMA
PAGE 26
"ma sha Allah,me muka samu?" Ya fadi yana dan murmushi. Murmushin itama tayi cikin salon tsokana
"Gani ya kori ji ai daddy duk da babu yawa" . Ledar ya qaraso ya dauka,har sannan idanun zainab na akai tana son ganin qwaqwaf.
"Kin gama komai ai,dama sauran abinda ya rage naketa tunani ban siya ba sai gashi kin kawomin,Ma sha Allah,ma sha Allah,Allah yayi albarka na gode qwarai" ya fadi yana buda kayan sosai.
Tsam zainab ta miqe tsaye tana maganganu qasa qasa kafin daga bisani tace
"Wannan ai cin fuska ne,me ya hana sanda ya shiga gurinki tun dazun ki bashi har sai da kika biyoshi gabana saboda tsabar iyayi da son nunawa?" Kallon tsaf ta yiwa zainab din,tana da amsoshin maida mata masu tarin yawa,to amma idan ta tuna gobe xai tafi ya barsu tare,kome zasuyi dashi zai tafi a tsaye cikin ransa sai kawai ta kauda kai ta bawa banza ajiyarta,ta kuma miqe a nutse tana dubansa
"Zan wuce daddy,saida asubar?"
"Alla ya tashemu lafiya maman twince"
"Na gode abban twince" ta maida masa tana murmushi ta gota zainab din
"Au aina dauka kwana zakiyi da sai na tattara nabar muku dakin"
"Hakanma ba laifi bane tunda mata kuma uwar gidan saleem nake" ta amsa mata ba tare data waiwayo ba tana qarasa fita a dakin.
Amsar tayi masifar qona mata rai,ga sunan da ya kirata dashi na maman twince sai take ga kamar gatse yakeyi mata,wannan ya hadu ya sakata rushewa da kuka.
Tamkar baya ma dakin gaba daya,ko gezau baiyi ba bare ya nuna yasan da wanzuwarta ita da kukanta a wajen,ko sau daya tak bai daga kai ma ya kalleta ba bare ta sanya ran zai tanka ta Hankali kwance yaci gaba da hada kayanshi,har sai data gaza don kanta
"Ko bakayi haka ba dama nasan ka gaji da zama dani matarka ce a gabanka,twince kuma itama ba ita baiwa kanta ba,wanda ya bata nima shi nake fatan ya bani" saita miqe ta bude zaninta tana bar masa dakin.
Bai motsa ba har ta fice sannan yabi qofar da kallo,shi kansa da yake namiji yana mamakin sokonci da dolanci irin na Zainab din,mijinki zaibar qasa a gobe maimakon ki tattalashi ku rabu lafiya amma inaaa.......baki ya tabe,ko kadan fushinta da bar masa daki ba wai wani baqon abu bane a wajensa,qauracewar zainab daga gareshi ya riga ya saba da hakan tunda dadewa(karki soma hora mijinki da irin wadan nan abubuwan,hanashi kanki don ya bata miki rai da sauransu,duk sanda ya saba da hakan zai zame masa jikine har ya dinga jin hakan ba komai bane,kuma muddin kina hakan tabbacin baki cika mace bane,ba kuma ki iya horo ba).
Tunda ta tashi sallar asuba ta kirayi wayarsa kamar tasan zainab din bata kwana a dakin ba. A lokacin ya idar da sallah yana shirin shiga wanka kenan,ta gaidashi cikin kulawa ya amsa mata
"Ka shirya ne daddy?"
"Waye zai shiryani tunda ba wajenki nake ba,komai da kaina nakeyi banga ma me shirin ba bare na saka rai"
"Uhmmmm" kawai tace dashi don tuni ta fuskanci inda maganarsa ta sanya gaba. Bata fiya jan zancan zainab ba a tsakaninsu don haka tace masa
"Idan ka gama shiryawar kayi min magana mu fito rakiya"
"Alright" ya amsa mata har cikin qirjinsa yana jin kewarta. Yayi imani inda a bangarenta tafiyar ta riskeshi gata babu kalar wanda bazai gani ba.
Koda ya fito dakin shuru sai ya kasa jurewa,ya daga waya ya sake kiran ruqayyan
"Har me?"
"Na kusa gamawa,ki kawomin manki zan shafa"
"Daddy mai kuma?,ina umman haneefa akwai gurinta"
"Naki nace ki kawomin" dan jim tayi tana kallon agogo,kaman yayi safiya da yawa ta shiga mata sashe,to amma tunda shi ya kira ba damar masa musu.
Man shafawar nata ta dauka wanda tasan daman time to time yana shafawa shima suna sharing. Har zata gifta kitchen wani tunani ya fado mata,tasan ba lallai ta bashi wani abun da zai sanyawa cikinsa,don haka ta tsaya ta hada masa black tea a gurguje ta fito masa dashi.
Sanda ta isa shi ya bude mata qofar ta wuce ciki,har ya kammala shirinsa saidai singlet ne kawai jikinsa da boxer,tana gama ajjiye kayan ya jawota jikinsa ya rungumeta tsam yana sauke ajiyar zuciya. Jikinta ta janye gefe tana noqe kafada
"Umman haneefa fa"
"Ba wani umman haneefa,gari ya kusan yin haske,a qa'ida ma an shiga ranar girkinki ai......i missed you a lot ruky na" ya fada yana lumshe idanunsa. Murmushi ta saki,duk sanda ya kirata da wannan sunan yana tuna mata da wasu abubuwa masu dadi da suka shude a tsakaninsu.
Duk da tana daddojewa amma haka ya jata sai data tayashi shiryawa
"Kayi haquri ba ranata bace,kaima kanka kasan da cikin hurumina kake ko......" sai tayi shuru kawai tana girgiza kai
"Yanxunma ai ni nakine ko?"
"Ni da wata,dole kuma a fidda mata haqqinta" ta amsa masa kai tsaye tana duban idanunsa,sai yadan kau da kai. Sau tari idan tayi wata maganar yana jin ta daureshi ne da jijiyar jikinsa ko kuma magana take maida masa a fakaice(uta tsarguwa fa ba dadi maganar gaskiya ππππ).
Abinda ya daure mata kai har ta tayashi ya kammala shiryawa ba zainab bare motsinta
"Daddy ka tasheta,bai kamata ace bata nan gurin ba yanzun,zan jiranka a waje" ta fada tana yin wuf ta fice don tasan idan bata haka ba zai tsaidata ne,kuma idan zainab din ta ganta ranta ba zaiyi mata dadi ba. Ballantana ita da ba haquri ne da ita ba ki dauke kai akan abubuwa.
Da sallama ya tura qofar dakin,sai ya hangeta magashiyyan tana bacci abinta Jamar dazun mai mata knocking yace ta tashi tayi sallah ba. Takaici ya kamashi ta miqe tana hada rai ita ala dole jiya an