Showing 21001 words to 24000 words out of 43918 words
ladingo Sweet Baby*💋
Yar mutan Niger🤙🏻
*Bismillahir Rahamanir Rahim*
*Chapter 10*
.....Wani irin kallo Adamcy ya juyo ya watsama Ma'azzara, hakan yasa tayi shuru ta fasa taɓarar da tayi niyya, kai yasa ya fita ita kuma ta tashi bethroom ɗin ɗakin ta shiga ta kunna shower aɗan tsorace ta farayin wanka, tana gamawa ta janyo towel ɗin ta saba goge jikinta dashi, wanda Aunty Hussaina tanuna mata a matsayin kullum da tayi wanka ta goge jikinta dashi.
Haka ta goge jikinta tsaf bayan ta fito wani body lotion ta janyo a gaban mirror ɗin tafara shafawa wani sanyin daɗin kamshi kefita daga cikin shi, saman fuskar powder ta shafa sannan tasa lip glow mai sheki saman lips ɗinta sannu ta fito kamar tauraruwa baƙinta layit ya ƙara dacewa da yanayin ta, riga da siket na atamfa ta saka dinkin das ya mata a jikinta. Tafiya take a hankali har ta sauko downstairs.
Dai-dai lokacin Adamcy ya k'ule sai faman duba agogo yake lokaci zuwa lokaci, kamshin daya daki hancin sa mai sanyi dadi yasa ya dubi inda yake fitowa, tana isowa ta nufi inda yake zaune kusa dashi ta zauna cikin sangarta tace" morning uncle" kallanta yayi cikin yanayin sa na basar wa yana yamutsa fuska, bai de yi magana ba, atamfar tayi mata kyau sosai ainun masha Allah. A hankali cikin tsare gida yace "Morning bani hankalin ki kiji abinda zan fadi miki." Ya fad'a yana zuba mata narkakun idanunsa masu launin zaiba.
Ma'azzara da sauri ta kauda kanta tana mai ajiyar zuciya ta lumshe manyan idanunta, cikin sanyi tace" uncle zan nutsu ka fad'a min ina Anty hussy nah?" Adamcy ya kauda idanunsa daga kallon ta ya tab'e baki yace"Sai yanzu kika tuna da ita Ko?" Ma'azzara ta sake matsawa kusan k'afar Adamcy ta kamo hannunsa tana jan zoben hannunsa, tace "Sorry My uncle ni yo ai na zata kuna tare ai kullum tare fa kuke kamar cingum..." ta fad'a tana 'yar siriyar dariya, tana murza zoben hannunsa.
Adamcy ya d'ago da sauri ya kalleta, cikin amon muryasa me dadin saura re yace"Ok ba kyaso ki ganmu tare da Auntynki Hussy?" Da sauri a tsorace!! Ta d'ago ta kalleshi, karaf idanunsu ya had'e guri d'aya, Adamcy ya d'auke kashin yana cewa"Zaki nutsu na miki bayani koko shirman zakici gaba dayi?" Ma'azzara da gabanta yake faduwa tin karfi ta sadda kanta k'asa tana wasa da hannun Adamcy, ta shagwab'e murya yace"Allah my uncle se na had'aka da my Hussy, ince kace banson ganinku tare." Ta karasa maganar tana kwantar da kanta saman guiwar Adamcy, still tana wasa da zoben hannunsa.
Adamcy ya mata yar tsawa yace"Wai ke Amana baki san kin girma ba kome na yara yan 8 year kike yi , ni d"agani to." Ya fad'a yana hararar ta.
Ma'azzara tayi fushi ta saki hannun Adamcy, ta d'auke kanta ta matsa gefe tana zumburo baki.
Adamcy bai san lokacin da wani sihirtaccen murmushi ya kuf ce masa ba, yace"To ki nutsu zan fara bayani...
Bayani Adamcy fara mata game da makarantar da sa tayi, da nasiha a kan ta kula da karatu inda yake cewa" look ƴar amana kinaji ko an samar maki makaranta abinda nake so dake bana son shashanci ki maida hankalinki kan karatunki inhar kina so mushirya dake, kin jiko" a hankali ta ɗaga mashi kai jikinta duk a sanyaye yaci gaba da cewa" duk wanda kikaga yayi nasara a rayuwa to ya kasance saida yasha matuƙar wahala dan haka ki dage wajan ƙoƙarin maida hankali akan karatunki dan shine gatanki kuma shine jigonki! a rayuwa.
Suna cikin haka sai ga Hussaina ta safko sanye take da riga da siket na shadda maroon colour tayi kyau sai baza kamshi takeyi, hannu ta ware wae ƴar amana ta taho, Ma'azzara ta dafa guiwar Adamcy ta mik'e cike da murna ta tafi da gudun ta rungume Hussaina, inda Hussaina ta rungumeta tana dariya, ta bata kiss a kumatu hagu da dama, sannan taɗan janyeta suka karasa cikin parlour ɗin.
Kallan Adamcy tayi tace" mon trésor mi ake tautaunawa da ƴar amanar ne?" Adamcy ya kauda kansa wai shi yayi fushi bata bi ta kansa ba, ta saki murmushi dan tasan zancan. Tashi tayi daga inda ta zauna ta isa gaban shi ta bashi pack a goshi ta kama hannunsa nan ma ta bashi pack ɗin, murmushi yayi yace "Nayi fushi" kunnuwanta takama tace" Tuba nake yi mon trésor Adamun Hussaina" hannu da tariƙe kunnan ya cire mata a kunnan yace "zauna" kusa dashi ta zauna har suna gogar shalder ɗin juna, suna sakarwa juna murmushi .
Tuni Ma'azzara ta sadda kai dan duk sai taji wani iri duk bata jin dadin hakan.
Nan Adamcy ya gaya mata kome, ta ƙara yiwa ƴar amana nasiha dangane da karatu nan Hussaina cikin janta a jiki da nuna kulawa taƙara mata nasiha inda Adamcy yace su shirya suje Hoapital dan ƙara duba lafiyar Hussaina danjiya bataji daɗi ba sosai, Hussaina tace" daga nan sai mubiya ayo ma ƴar amana siyayya kayan makaranta" yace "ok".
Tsaf suka fito cikin shiri sunyi kyau kamar taurari Ma'azzara sai satar kallan Adamcy take ai kuwa da sun haɗa idanu sai ya sakar mata harara, ita kuma ta sadda kai wani pravete Hospital sukaje an dubata bata da matsala fiver ce kawai ta masu juna biyu, bayan an gama dubata aka ɗan rubuta masu magani pharmacy suka biya suka siya sannan suka nufi wani danƙareran super market wanda daman siyayya agurin sai wane da wane food flast da school b, sandal sock's da biro pancil dadai sauran karikitan makaranta komi Hussaina na bajinta take jidar mata, inda Adamcy ke tsokanarta yana cewa" kekam duk sai kinbi kin shagwaɓa yarinya hankalinki zai kwanta" tayi murmushi mai ƙara mata kyau tace"in ban yiwa my ƴar amana ba wazanyi mawa?" Adamcy yace "gani" dariya sukasa gaba ɗaya ita dai Ma'azzara na sauraransu.
ɓangaran kayan ciye ciye kuwa sai da Adamcy yace ma Hussaina tabarsu haka dangin chocolaty bescut cingam da sweet kamar zata haɗa ƙaramar tireda, haka suka dawo gida komi fitan yasanya musu rest of mind kowa upstairs ya haye dan sakarwa kanshi shower, oga Adamcy da Hussaina andaɗe ana soyewa kafin daga baya suka gaji da shiriritar suka yi wanka tare da ɗaura alwalla dan ana gap da kiran sallar la'asar.
Ma'azzara ta riga su saukowa down zaune take a parlour ta kurawa tafkekiyar Tv ɗin bango idanuwa inda suke wani news a tashar aljazeera cikin harshen turanci, zamata ba daɗewa Hussaina ta safko "sweety ƴar amana har kin fito?" murmushi tayi tace" eh Aunty" yawwa matso kiji wani abu kinga Adamcy baya san kina kallon nan ko? to ki dinga dauke kanki daga kai koda kuwa bake ce kika kunna ba, dan banaso ki dinga san ya ran uncle yana ɓaci kinji ƙawanta" taƙare maganar tana mai lallaɓata itama Ma'azzara kai ta langaɓar tana amsawa da "to"nasiha tayi ta mata mai shiga jiki cikin wayo da dibara.
*Washe gari* monday takama ranar ne kowan ne ɗalibi ke yiwa makaranta shiri na musamman, kamar yadda yake a gurin Ma'azzara a ranar tun *6* kowa na gidan ya motsa domin a lokacin ne oga Adamcy yake fita bank kuma ga shirin makarantar new commer ta gidan su, haka suka hau shiri inda Hussaina ta shige kitchen ta kunna hittle ɗin ruwan zafi shayi na musamman, ta haɗa mai citta da kananfari da na dangin kayan shayi banda kamshi ba abinda ya keyi mai daɗi kamshi ya isa ya kwaɗaita maka san shan sa, ga irash ta soya da kwai ga cif tayi da fey fey sosai, inda hadiza mai aiki ke taimaka mata nan da nan suka ƙarasa tsaf ta fito cikin gwon rigar uniform ɗinta mai ruwan toka da ciki kuma fara mai dogon hannun kanta ba kallabi ya sha kalaba ƙanana ciwistik masha Allah daman tana da yalwar gashi har gadon bayanta, baƙi siɗik ga samtsi *6:30* am Adamcy ya sauko, yana ganin ya makara daidai lokacin kuma ita ma ta safko down ɗin tana ɗan sauri kallanta yake cikin uniform ɗin dan kyau ya mata kyau amman ya bayyana surar jikinki sosai, haka ya kudurta ma ransa tunda dole ne sanya uniform ɗin to tabbas zai koma ya siyo mata over size, tunda yaga wannan sun bayyana mata surah jikinta, ɗan tsaki yayi kaɗan inda bama tasan yana gunba duk da taji kamshin turaransa amman hankalinta ya tafi ga kitchen gurin su Aunty Hussaina ɗan wagowa kaɗan tayi tadawo baya da sauri ta tsaya kamar zata shiga jikinsa, ta shagwab'e tace"uncle morning nayi missing dinka ba a ganinka kullum." A hankali yace morning ke ni bana son shirme jeki sabgar gabanki ." Kara matsosa tayi kusan sa zata kamo hannunsa tana dariya, ya ce"Wlh kina tab'a min zobe zaki sha mari" ya fad'a a dan tsawace.
Ma'azzara taja baya tana gunguni, shiko ya tab'e baki yana nufa kan dining inda aka shirya breakfast .
Ma'azzara ta koma gun Hussaina ta fad'a mata uncle ya hanata ta tab'a zobe, Hussaina dariya kawai take.
Tare suka nufi kan dining d'in da Hussaina, chear ta janyo ma ƴar amana tace"baby ƴar amana zauna oya a yi breakfast a fice school iyeeee kaga ƴan makaranta"duk cikin barkwanci tayi maganar inda Ma'azzara tasa hannu ta rufe fuskarta tea kawai tasha taja cheir ɗinta baya, fuska a haɗe Hussaina ta kalleta tace "zamu ɓata fa zauna mana oya" tsaki Adamcy yaja gaba ɗaya suka kalleshi yaci gaba da cewa "wato Hussaina bazaki daina shagwaɓa yarinyar nan ba abincin ma sai kin wani lallaɓata zata ci"dariya tayi taɗan faɗa saman shi ta kura masa idanu cike da so da kaunarsa, tace" to ba dole mu lallaɓa ƴar amana ba cinkulinta yayi ta zille tana dariya.
Tare suka fito parking lot amman Ma'azzara ta ɗanyi masu nisa, inda takejin daɗin uniform ɗin tunda tasa ba nauyi bakomi gashi ya mata cif-cif oga Adamcy kuwa ganin yadda jikinta ke juyayawa yace a ransa yarinya daga yau kin daina sa kayanan over size zaki koma sawa har wani iyayi kike kina faman juya jiki, Allah yana gani ba dan so abinda zai cutar da amanar da d'aukar Allah.
Allah sarki ita kuwa tsakaninta da Allah take tafiyarta saboda halitar tace hakan, tamakar tana yanga, itako ba haka abun yake ba, bada wani manufa, take ba, a salima bata yanga Ma'azzara.
Gaban manya-manyan car ɗin suka tsaya inda ya nufi wata black jeep sai meko take kamar ranar aka yage mata leda, back seat ta shiga dan yaune farko zai fice da ita daga baya kuma direba zai dinga kaita zama tayi tana lumshe ido saboda wani kamshi mai daɗi game da sanyin Air condition ɗin daya ratsata saida suka gama shin shine shin shinansu, ta tsotsi bakinsa son ranta, shiko ya murza breast dinta saboda mayan breast ne, harda buɗe riga wai zaiyi sallama da *Babynsa* Hussaina ta lallab'ashi, sannan ya shigo yana wani tsare gida ita kuwa dama tunda ta shigo bata ganin komi domin tinteck ne.
Anutse ya kunna motar ya fizgeta ya nufi kofar tamgameman get din gidan. Yana sulala motar waje ya fara driving cikin nutsuwa, cikin 'yan mintoci kaɗan suka iso inda sai karantse motar ɗin ba tafiya take ba, saboda yadda bakajin ƙara komai ba kajin komi saboda lafiyar motar.
*ALGOZA INTERNATIONAL JUNIOR SCHOOL NAIMEY NIGER*
haka aka rubuta ajikin ƙaton get ɗin da yayi covering din school ɗin, wani sanyi taji ya ratsa ƙarƙashin zuciyarta lokacin da aka wangale masu get ɗin suka danna hancin car ɗin cikin school ɗin parking space ya parking a hankali ya danna remote ɗin inda ƙofofin suka dinga buɗewa kamar murfin food flast sauka yayi, itama tabi bayansa nan suka nufi office ɗin pc ɗin inda daman anyi clearing komi haka ba dadewa aka mata ƙaramar enterviw inda ya kama za a sanyata j.s two tunda balefi brain ɗinta naja aka kaita class ɗinsu inda take farin ciki ya kamata tace "wayyo ni Ma'azzara Agashina da Aunty Hussaina da Uncle Adamcy yau nice a makaranta irin wannan gani cikin jansi da yare iri iri Alhamdulillahi", kasan cewar makarantar babu yaran da babu domin ba Niger kawai bane akwai Nigeria akwai turawa da larabawan Algeria da Ghana, ka sancewar ba yaran da babu a koyawa a makaranta kamar france english hausa ajami arabic islam dadai saura yaruka haka ma tafiz ce sannan kuma tana da cikakken foundetion mai kyau inda ƙasashe da dama suka jinjina mata kuma suke rubibin kawo yaransu haka da wuya kasamu mutum ya gama karatunshi a makarantar bai san abinda yake yi ba, sannan in kaga scondry kana buƙata akwai kuma jami'a duk dai a ciki shiyasa idan kafito da kwalinka in dai a makarantar kayi karatu zakaga ana rububin daukarka aiki, dan ansan ba kuɗin banza za a baka ba, idan lokacin salary yayi treaning suke mai kyau.
Aroud 4:28 Adam ya kira wayar Hussaina ciki muryarsa mai daɗi yace "hello sweet hussy kina jina?"cikin muryar bacci tace "eh" da saure yace "my hussy are sick!!" no am ok" Hussaina ta dan murmusa tace" kawai na tashi daga bacci ne my Adamcy" a hankali ya saki ajiyar zuciya yace "ok 4:40 kisa direba ya ɗakko ƴar amana a school ni daga bank zan wuce company muna da wani aiki akwai kaya za a fitar kuma akwai wanda za a shirya , so in har ba nine da kaina nayi aikin ba to bana ganin dai-dai suma wai sunfiso ayi komi a gabana, dan haka ki kular min da kanki kin jiko "cikin tausayi da jin ƙai tace to insha Allah kakula da kanka my coeur je t'aime i love u bye". Murmushi Adamcy yay yace"moi aussi je t'aime Bcp mon bebeta bisous bye."💋💋💋ya tsinke kiran.
Nan take ta kira layin direban ta sanar dashi bayan sun gaisa cikin girmamawa.
ranar su Ma'azzara an sha karatu dan gaskiya gaba ɗaya ta maida hankali kan abinda ake koyawa, dan ta daukarwa kanta alƙawarin mai da hankali za tayi bakin koƙarinta wajan ganin taba mara ɗa kunya, saboda Hussaina taƙara kwaɗaitar da ita mahimmancin ilimi kai harma da Uncle Adamcy, ranar taga mutane kala kala wasu bakaƙe wasu farare wasu kuma wankan tarwaɗa.
a gajiye aka dawo gida Aunty Hussaina na mata dariyar raguwa ce murmushi tayi dan tagaji babakin surutu da shirme.
a kwana a tashi haka karatun Ma'azzara yake tafiya cikin nasara, inda ta maida hankali sosai ko Hussaina na yabawa ƙoƙarinta, yayin da shima Adam na lura da yadda take gudanar da harkokin karatun nata, lokuta da dama zata keɓe kanta a ɗaki tayi tabita haka ma yanzu bata wani damuwa da kallo amman fa ko pic tagani na masoya sai sun birgeta hankalinta ya fara tashi tana matse k'afafunta, haka mafarkinta da Adamcy har yanzu bata daina ba sai abinda yaci gaba yau da kawa tara da suka wuce ta fara froide, ranar sun shiga mugun tashin hanakli dan wani mugun ciwon ciki ne ya kamata tana school kafin kace me har ta suma, aka nufi asibitin da take cikin school din aka kirawo Adamcy ya shiga tashin hankali, amma da doctor ya masa bayanin abinda ta fara shine sanadin ciwon kuma ko wace mace da yanda Allah yake doro mata ciwon wata kuma bata mayi sai de taji yazo, ita alamu sun nuna tana karfin sha'awa, irinsu da wuri ya kamata ai masu aure, nan saida zufa ta karyoma Adamcy, dan shi yana da burin ya sama mata ilimi kafin Allah yake hadata da miji na gari, dan ba kowa zainba auranta sai ya sami tsayayyan namiji, dole ya rage damuwa ya cika da mamaki dan shi duk tunaninsa Ma'azzara ta jima da fara jinin Al'ada, se da tayi kwana biyu bata zuwa school tana gida dan ba kramin ciwon ciki take ba, Hussaina harda kuka ta koya mata kome a nutse, sosai yanzu Ma'azzara take jin kunyar Hussaina,
dan ta rage shishige ma Adamcy da yawan shirman da take zuba masa domin kullum ƙara girma da fuskanta miye rayuwa take, amman duk da haka in tayi wani abinda sai ka rantse ƴar shekara bakwai ce, haka yanzu Aunty Hussy bata kunna boolywood da mbc action ko kuma mbc drama da duk wasu tasho shi da suke sanya fina-finan soyayya duk sanda takema tashar tana hakura dan batasan abinda zai daukewa ƴar amana hankali akan karatu, amman in tayi baccin rana dare yayi bata komi takan kalli maimaici.
Ma'azzara ce zaune tsakiyar bed ɗin ɗakinta daga ita sai farar bes kasancewar yau weekend, kuma ana ɗan zafi zaune take tana ta wani calculation wanda ranar monday za ayi sometting.
parlour kuwa Adamcy ne da Hussaina suna hira cikin so da kauna, inda yake cewa"wai ina yarinyar nan??" idan ka kalli yadda yayi maganar sai ka rantse da Allah dole aka yi masa. Da murmushi akan fuskar Hussy tace"ai beby ƴar amana tamana komi mon coeur dan tayi matuƙar maida hankali akan karatu bata sanya" yace "nima nalura da haka" da ɗan sauri ta miƙe tana ceaw "bara in gano ta" tayi baje-baje kalabar bamalin ta duk ta zubo mata a kafaɗarta, sannan ga jikinta yayi wani kyau alamar hutu kirjinta yatada yaɗan fara tudu alamun budurci sunfara bayyana a tattare da ita Hussaina ta zuba mata ido duk da kasancewarta kyakyawa amman tasan Ma'azzara tana da kyau wanda in ta zama buduruwa tana da yaƙinin siriki sai ta zaɓa kamshin turaran Aunty Hussy ne ya sanar da ita zuwan Aunty, dan ko ƙaran handle bataji ba domin gaba ɗaya hankalinta ya tafi wata duniyar ta daban, da sauri tasa hannu tayi baya da kalabar data rufe mata ido tace"oyoyo Aunty Hussy "dan harta kara wayewa bata cewa Auntu Hussaina kasancewar cuɗanya datake da ɗalibai kala-kala bata kuma kai kanta ga kowa tsabar maida hankali a karatu yasa nan da man tayi suna duk