Showing 3001 words to 6000 words out of 47249 words

Chapter 2 - Exiled Prince Book 2 Hausa Novel Complete

Meerah   

13 Dec 2024

283

, amma ya na neman ya daura min abun da ya fi karfi na , ni gaskiya ba zan iya mulkar mutane ba "

Yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " gaskia kam ba za ka iya ba , da wannan shagwabar za ka zama Malik , ko Tesnim ba za ta gwada ma ka shagwaba ba "

Hararrar wassa ya wurga mata ya na shirin magana ta mike tsaye ta mika mishi hannu ta na fadin " let's go see Abbi mu yi mishi magana a tare "

Da sauri ya mika matta hannu ya mike tsaye ya na murmushi
Ya na mikewa ya ji kamar karar faduwar karfe a wajen kofar shigowa wajen
A tare su ka kai duban su a wajen kafin Amir ya fara takawa a hankali ya nufi wajen da ya jiyo karar
Cikin nitsuwa Ta tsayar da shi da cewa " ina kuma za ka je ka bar alkyabar ka " ta fada ta na fara takawa ta nufi table din ta dauki alkyabar sannan ta nufo shi ta ce mu tafi ko
Ba musu ya bi bayan ta su ka bar wajen a tare ta na rike da Alkyabar shi

Su na barin daya da ga cikin dakarun da ke tsaron wajen ya juya ya bar wajen da sauri sauri
Sai da ya karaso kassan wata katuwar bishiya cen bayan masarautar inda babu kowa ko me wucewa babu sannan ya tsaya ya Zube saman guyiwowin shi ya na sunkuyar da kai ya ce " gaisuwa na ke ya shugaba na "

Wani mutun ne zaune kassan bishiyar ya na sanye da wasu kaya bakake Dukan su , Idanun shi kadai a ke iya gani saboda ya rufe fuskar shi da wani bakin harami baki shi ma
Cikin wata murya cike da isa ya ce " ya a ke ciki ne ? "
Ba tare da ya dago kan shi ba ya ce " ya shugaba na , na jiyo Amir na fadin zai fara shiga Fada tare da Malik "

Da sauri mutuman ne ya katse shi da cewa " sai in ya na raye zai shiga Fadar "
" Haka ne shugaba na "
" gobe ina son in ji labarin mutuwar Amir , idan kuma ta wuce gobe kai za ka mutu a madadin shi Meli "

Murya na kerma Meli ya ce mishi " in sha Allah ba za a samu matsala ba shugaba na , duk wani shirye shirye da za a yi mun yi shi , lokaci kawai mu ke jira "

Jinjina kan shi mutuman ya yi kafin ya ce " ina jiran albishir mai dadi Meli , ni kuma zan cika maka alkawarin ka "

" Godiya na ke ya shugaba na , Allah ya ja zamanin ka , Allah ya kare gaba da bayan ka ya shugaba na "

Daga mishi hannu mutumin nan ya yi kafin ya ce " ya isa haka tashi koma bakin aikin ka "
" godiya na ke ya shugaba na " Meli ya fada kafin ya mike kai a sunkuye ya bar wajen
Ya na barin wajen mutumin nan ya bushe da wata shegiyar dariya ya na fadin " sai dai ka yi hakuri dan uwa na amma dole Mulkin saudiya ya dawo cikin tafin hannu na , ko da kuwa Malik din da kan shi zan kashe " ya kai karshen ya na sake bushewa da dariya kafin ya bace bat a wajen


* MISALIN KARFE 8 NA DARE


Wani katuwar dining room dauke da wata kyawatatar dining table Fara kal dauke da wasu chair goma sha biyu suma farare kal gwanin burgewa
Table din shake ta ke da abincin kala kala da Fruits wannan abincin sai ya ciyar da gida je goma su ci su koshi har su samu na breakfast
Nan na hango mutanan gidan zaune saman chair su shidda ne mata hudu da namiji biyu
AMIR NAWFEL da wani dattijon wanda na san Shi ne MALIK din dan kamanin shi daya sak da AMIR NAWFEL har Hazel eyes din su
MALIK ya na zaune saman chair din da ke tsakiya , geffen shi na dama RIANNA ce zaune tare da MALIKAT INAS sak kamanin ta da RIANNA

Geffen hagun shi kuma AMIR NAWFEL ne zaune tare da TESNIM , sai MALIKAT AL'UMU ta so ta dan yi kama da AMIR NAWFEL amma ba sosai ba

A hankali MALIK ya dago kai ya kali AMIR NAWFEL da ya sunkuyar da kai ya na cin abincin shi , amma da ga gani ka san ba dan ya na son abincin ba ya ke cin shi

Dan karamin murmushi MALIK ya yi kafin ya kali yarinyar da ke zaune geffen shi ya ce " TESNIM yaushe za ki tafi Daular Ottoman , mun yi waya da kakan na ki ya ce ya shirya miki wata tsaraba ta musaman "

Kunbure fuska TESNIM ta yi ta turo dan bakin nan nata gaba ta ce " Abbi ba AMIR ne ba na ce mishi yaushe za mu tafi ya ce wai shi ba zai je ba "

Slowly AMIR ya dago kai ya kali TESNIM murya kassa kassa ya ce " dole sai da ni za ki je , ba ki san hanya ba ne "

" NAWFEL laifin me ta yi maka da ga ta ce ka raka ta " MALIK ya fada ya na kallon AMIR

Dan karamin tsaki ya yi kafin ya mike tsaye ya juyo ya fara takawa cike da nitsuwa ya bar wajen
" NAWFEL ina za ka je ba ka Kamala abincin ka ba " RIANNA ta fada

Ko amsa mata bai yi ba ya ci gaba da tafiyar shi
Sai da ya bar wajen sannan ta juyo ta kali MALIK ta ce " Abbi don Allah ku janye maganar nan ta AMIR ya hau mulki wlh ba ya so "

Daga mata hannu MALIK ya yi ya katse ta kafin ya ce mata " RIANNA ke da NAWFEL na ga bakin ku daya , idan bai hau mulki baya na ba wa zai hawa , ku nai sheda shi kadai ne yarima da na mallaka , ya tafi ya hura miki kunne ko , ya zuba miki shagwabar da ya saba ko "

Marairaice fuska RIANNA ta yi ta na fadin " please Daddy , ku ba shi damar ya zabi abun da ya ke son yi , kar ku condemend din shi saman abun da bai da ra a yi , wlh Abbi tun da ya nuna ba ya son Mulkin nan wlh ko ya hau ba zai tsaya ya kula da saudiya kamar yadda ku ke yi "

" RIANNA tashi fice min da ga gani sai ki bi bayan shi dama ke ce ke darme mishi gindi ya na abun da ya ga dama , to sai ki je ki rarrashe shi , ki kuma fada mishi gobe ya shirya bi na Fada "

" Abbi ......... "
Da sauri Malik ya daga mata hannu ba tare da ya ce komai ba
Tashi ta yi ta na dan kananan magaganun ta bi bayan AMIR ita ma ta bar wajen
Su dai Malikat kallon shi kawai su ke dan sun san halin Malik idan ya yanke shawara to babu wanda ya isa ya sa shi ya sauya shawarar nan dama haka nan ya ke da magana guda a ka san shi , duk irin halin da zai tsinci kan shi , shawarar kan shi kawai ya ke dauka , bai taba neman shawarar wani ba , Idan kuma abu ya shige mishi duhu shawarar Matan shi kawai ya ke nema


Bayan RIANNA ta baro dining room din su kai tsaye wani kyawatencen parlour ta nufa nan ta isko AMIR zaune saman chair din Malik ta gold zalla ya daura kafa daya bisa daya ya kurawa Tv ido

Dan zaro idanu RIANNA ta yi ta na kallon shi da sauri ta nufe shi ta na fadin " kai AMIR kujerar Malik za ka hau haka , maza sauka tun bai gan ka ba , ka fi kowa sanin bayan shi babu wanda ya isa ya hau wannan kujerar "

Slowly AMIR ya juyo da kan shi ya kali RIANNA ya na dan lumshe idanun shi kamar mai jin barci , cike da izza ya ce mata " da ga yau ta zama tawa " ya kai karshen ya na meda kallon shi kan Tv

Dan zaro idanu RIANNA ta yi ta na kallon shi baki sake , tun da ta ke da AMIR ba ta taba ganin ya yi mata kwarjini kamar na yau ba
Ta na shirin magana ta jiyo Muryar Malik a bayan ta ya na fadin " yanzu sai ka tashi me ita ya zo "

Dum ta ji gaban ta ya buga da sauri ta juya ta na kallon shi ta na dan zazzaro idanu
Shi dai AMIR ko motsi bai yi ba asali ma ko kallon inda Malik ya ke bai yi ba ya ci gaba da kallon Tv ................... ( ku tsaya na dubo abun da ke cikin Tv din nan gaskia )
Ba komai ba ne face masarautar ya ke kallo ta cikin kananan camera da a ka boye ta ko ina cikin masarautar , shi dai kawai ya na kallon abun da ke faruwa a cikin masarautar ne amma hankalin shi na nesa

Har sai da Malik ya karaso gaban shi ya tsaya ya na yi mishi magana bai sani ba
Kawai sai ji ya yi an buge mishi kafar shi ta sama ta fadi kassa ,
Slowly ya lumshe idanun shi kafin ya bude su ya na kallon Malik ido cikin ido kafin ya ce " What ? " a takaice

Ba Malik kadai ba har RIANNA da ke tsaye a bayan shi sai da ta zaro idanu ta na kallon AMIR
" NAWFEL sauka da ga saman kujera ta " Malik ya fada cikin nuna isa

Shiru AMIR ya yi na dan mintina kafin ya meda kallon shi kan Tv din ba tare da ya ce komai ba
" Akhie ............ "
Kut maganar ta yanke sakamakon daga mata hannu da Malik ya yi
" Idan ka na son zama saman wannan kujerar , dole sai ka yarda ka amshi sunan ka na yarima mai jiran gado ka fara bi na Fada domin ganin yadda a ke kula da masarautar nan sannan za ka iya zama saman wannan kujerar "


Slowly AMIR ya mike tsaye ya fara takawa a hankali ya karaso gaban Malik ya tsaya ya na kallon shi cikin ido ya ce " kujera ce dai sai na hau ta , sannan ni ba zan je Fada ba , ba na bukatar shawarar kowa ba na kuma bukatar sannin yadda a ke kula da masarautar , duk ranar da a ka nada ni a matsayin Malik tsari na kadai zan bi dan haka ka daina min zancen wata fada ni babu inda zan je " ya na gama fadar haka ya juya ya koma saman kujerar nan ya zauna ya daura kafa daya saman daya ya ci gaba da kallon Tv din gaban shi


Shi dai Malik sumar tsaye su ka yi shi da RIANNA
Sai ya kare mishi kallo da kyau sannan ya ce ma RIANNA ta ba su waje
Ba musu ta juya ta bar parlour dama part din Malik ne su ke ciki sai ta bar part din baki daya dama su Malikat su riga ta tafiya TESNIM kuma ta tafi yawon birididin da ta saba , ba ta wannan part ba ta wacen duk in da ta kama ta tafiya ta ke yi


A hankali Malik ya nufi wata Sofa da ke daman kujerar da AMIR ke zaune a kai shi ma ya zauna ya na kallon AMIR

Kamar ko ya san kallon shi ya ke yi ya ce mishi " lafiya ka na kallo na haka "
Girgiza kan shi Malik ya yi ya na murmushi ya ce " Mulki ya na kama ka AMIR why kullum ka ke abu kamar mace , sai dan karan shagwaba , ko takobi sai da RIANNA ta matsa sannan ka fara koyo , da ba hakan ba yanzu ko makiyi ya zo maka ba za ka iya kare kan ka ba "

Shiru AMIR ya yi bai ce mishi komai ba
Dariya Malik ya yi kafin ya dauki wani pillow saman sofar ya tila wa AMIR
da sauri AMIR ya kauce pillow din bai same shi ba
Dan karamin murmushin geffen fuska ya yi ya ce " Abbi , ni fa fada ne da makami ba ya burge ni , na fi son fada da hannu "

" hmmm , hakan ba shi ba ne mafita ba , ya kamata a ce duk wani makami a duniya ka iya fada da shi , ba ka san ta yadda makiyin ka zai zo maka ba , bare kai da ka ke cikin gidan sarauta "

Cikin nitsuwa AMIR ya katse shi da cewa " Idan kuma makiyin ya zo maka ta baya ? "
Shiru Malik ya yi ya rasa amsar da zai ba shi
Jin ya yi shiru ya sa AMIR juyo da kan shi ya kali Malik
Dan karamin murmushi ya saki kafin ya ce " ba ka san ta yadda makiyin ka zai zo maka ba , amma na san wani abu , duk mai sanin ganin bayan ka , ba zai soke ka ta gaba , dole ta bayan idon ka zai soke ka , saboda ya san ka fi karfin shi ta gaba "

" wait ! Maganar me ka ke yi min haka " Malik ya fada dan shi bai san abun da AMIR ke fada ba

Meda kallon shi AMIR ya yi kan Tv sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce " ba komai kawai ina nufin ka zama me tsare bayan ka a kodayaushe saboda ba ka san ta inda makiyin ka zai zo maka ba , Idan kan ce ka za kare gaban ka kadai , to ta bayan ka zai zowa , dan haka ka zama mai kare gaba da bayan ka , saboda ba ka san da wa ka ke tare da shi ba , Makiyin ka zai zo ma ka da sufar aboki , aboki kuma da sufar makiyi "


Dariya sosai Malik ya yi kafin ya ce " shi ya sa ban yarda da kowa cikin masarautar nan , ko a fada ba shawarar kowa ba ke doka ba "

" Duk da hakan , yanzu idan na tambaye ka cikin fadar nan wanda ke zaune da kai da zuciya daya za ka iya fido min su "

Shiru Malik dan ba kariya ya fada ba
" Shi ya sa na ce ka zama mai tsare gaba da bayan ka , ba ka san wanda ka ke tare da shi ba , ko da ya na zaune da kai da zuciya daya , wata rana zai iya juya maka baya "

Dogon nunfashi Malik ya ja kafin ya ce " kai ni fa hirar nan ta ka mara ma'ana ta fara isa ta "

Murmushi kadan AMIR ya yi kafin ya ce " ban rike ka ba tashi ka tafi "
" ban son shirme , part di na ne ka ke ciki "
Dariya AMIR ya yi ya na fadin " ba wajen matar ka ba za ka kwana , tashi ka je ni a nan zan kwana "

" kai eh fa haka ne ka ma tuno min , bari na tashi na tafi wajen baby na " ya kai karshen ya na mikewa tsaye

Da sauri AMIR ya taro shi ya na fadin " Wait, Abbi wa ka ke kira da baby "
Hararrar wassa Malik ya yi mishi kafin ya ce " Mummyn ka mana " ya kai karshen ya na kashe mishi ido guda

Dariya sosai AMIR ya yi har da dafe ciki idanun shi na kawo ruwa
Shi ma dai Malik yar dariya ya yi kafin ya tako kusa da AMIR ya dan sunkuyar da kai
Ya rage sautin Muryar shi kamar mai rada ya ce " Ka na ji na ko , ita fa mace yar shagwaba ce ka bar ganin dan ta haifi zankadeden saurayi kamar ka , kullum ta na son a dinga ririta ta , a na shagwaba ta kamar baby , dan ba ka da matar ne shi ya sa ba za ka gane ba "

" ba ni ma son na gane " AMIR ya fada ya na yar dariya

" hmmm AMIR ina guje maka ranar da so zai maka mugun kamu , wlh sai ka yi kuka "

Dan matsowa AMIR ya yi kusa da face din Malik murya kassa kassa ya ce " Har yanzu ba a yi macen da za ta Mallaki zuciyar AL-AMIR NAWFEL BIN JAABAR d'a tilo ga MALIK HICHAM BIN JAABAR jikan MALIK ABDOUL LATIF BIN SAUD , Har yanzu ba ta shigo duniya ba "

Jinjina kan shi Malik ya yi kafin ya ce " Gaskia ne kam , izza a jinin ka ta ke , amma ka sani , mace ce ta haife ka , kamar yadda ta haife ka haka zalika , za ta haifi wadda za ta malake zuciyar ka , duk wannan izzar da ka ke nuna wa sai ta zube a gaban ta , ka jira ka gani "

" Abbi , dubi wuce ka tafi wajen babyn ka , ni kyale ni film zan kala "
Yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya kai bakin shi ya sumbaci forehead din AMIR sannan ya ce " ai kai ma baby na , I love you "

Dan murmushi AMIR ya yi kafin ya ce " I LOVE YOU dad "
Jinjina mishi kai Malik ya yi kafin ya mike ya juya ya fara takawa
Har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login