Showing 18001 words to 21000 words out of 47249 words

Chapter 7 - Exiled Prince Book 2 Hausa Novel Complete

Meerah   

13 Dec 2024

289

ka zo gida su ka tafi da shi "

Gyada kan shi ya yi a hankali kafin ya ce " ina fatan ba ki da matsala da hakan "
Girgiza mishi kai ta yi allamun babu
" okay , Gabe za ki bi shi masarautar su ya gabatar da ke ga Familyn shi , Idan kuma a nan ki ke son zama ba matsala za a ware muku part "

Da sauri ta ce mishi " ni a nan zauna tare da Mama da Inaya , ba zan iya yin nesa da su ba " ta kai karshen kuka ya na kubce mata

A hankali AMIR ya hannu ya janyo ta jikin shi ya rungume ta dan ya san ba komai ba ta ke yi wa kuka ba face malam , ko shi hakan ya ji cikin zuciyar shi da ya kira sunan shi amma ba yadda zai yi dole ya danne

Sai da ya ji ta yi shiru sannan ya sake ta ya ja hannun ta su ka koma cikin runfar nan
Ya na zuwa ya mikawa Diya hannun ta
Murmushi Diya ya yi kafin ya riko hannun ta ya janyo ta ta zauna tsakiyar su shi da Abdoul ta na sunkuyar da kai

Shi kuma ya koma geffen Inaya ya zauna ,
Ya na zama Azim ya karaso wajen ya Zube gaban AMIR ya na fadin " gaisuwa na ke ya shugaba na , mai martaba na son ganin ka a Fada yanzun nan "

Shiru AMIR ya yi na dan mintina kafin ya ce " za ka iya tafiya "
" godiya na ke ya shugaba na " ya na gama fadar haka ya tashi da sauri ya bar wajen

Ya na barin wajen AMIR ya daga kan shi sama ya lumshe idanun shi
" AMIR ba za ka je ba ne " Diya ya fada mishi dan ya ga allamun ba ya da niyar tashi
Shiru AMIR ya yi bai ce mishi komai ba , bai kuma saukowa da kan shi ba
Ya na a haka ya ji kawai an kontar da kai saman cinyar shi
Slowly ya sauko da kan shi ya bude idanun shi , ya na kallon ta
Allamun barci ta ke ji dan har ta lumshe idanun ta , ta daura kafafun ta saman Sofar
Bai ce mata komai ba ya daga kan shi ya lumshe idanun shi

" Rouksar tashi mu tafi ko ? " TESNIM ta fada ta na mikewa tsaye
Karewa AMIR da Inaya kallo Rouksar ta yi kafin mike ta bi bayan TESNIM su ka bar wajen
Su na barin wajen shi ma Abdoul ya mike ya na fadin " Diya ina mama ta ke ina son ganin ta "

Cikin nitsuwa AMIR ya riga Diya cewa " ta na part din MALIKAT HOUDA "
Gyada mishi kai Diya ya yi kafin ya mike ya riko hannun Nesrine ya ce su tafi Abdoul na biye da bayan su , su ka bar AMIR da Inaya a wajen

sannu sannu har AMIR da Inaya su ka share wajen good on hours a haka
ita ta yi barci shi kuma ya tafi duniyar tunanin shi , Allah kadai ya san abun da ya ke tunani

ya na a haka kawai ya sake jiyo Muryar Azim ya na yi mishi sallama
Dan karamin tsaki ya yi kafin ya sauko da kan shi , shii ya ma manta da cewa a na jiran shi a Fada

gaishe shi Azim ya yi kamar yadda ya saba sannan Ι—aura da cewa Malik na son ganin shi a part din shi
"Okay " ya fada a takaice kafin ya sa hannu a hankali ya sauke kan Inaya da ga saman cinyar shi ya mike tsaye

sannan ya juya ya dauke ta cak kamar baby ya juya ya fara takawa ya bar wajen Azim na biye da bayan shi dan wannan karan Malik ya ce kar ya dawo ba tare da AMIR ba

shi kuma AMIR kai tsaye part din MALIKAT INAS ya wuce da Inaya
da sallama cen kassan makoshi ya shigo parlourn MALIKAT INAS
nan ya tardo ta zauna ita da RIANNA su na hirar su

su na ganin shi dauke da Inaya su ka mike su ka nufe shi a rude su na tambayar me ya same ta
bai bi ta kan su ba ya wuce ya kontar da ita saman Sofa sannan ya juyo ya kale su ya ce " barci ne ta ke yi " ya na gama fadar haka ya raba ta geffen su ya wuce ya fice part din

wani cool murmushi RIANNA ta yi kafin ta tako ta zauna kusan Inaya ta ce " Ammie , ina ji a jiki na yarinyar nan she is so special for AMIR , duba ki yadda ya ke kula da ita kamar baby "

ita ma MALIKAT INAS wani dan karamin murmushi ta yi kafin ta koma inda ta taso ta zauna ta na fadin " dole ya kula da ita saboda ya na son ta , zalar so ya ke yi mata amma har yanzu ya kassa yarda da hakan , Idan har AMIR ya bude baki ya ce ya na son yarinyar nan zan fi kowa farin ciki , she is so innocent , abun da na lura da shi ta fi yar uwarta nitsuwa , za su dace sosai da juna , Sai dai kashh ya ki karbar soyayyar da ke cikin zuciyar shi "

" To yanzu Ammie ya ki ke so mu yi "

shiru MALIKAT INAS ta yi na dan lokaci kafin ta ce " ba abun da za mu yi , kawai za mu sakawa ikon Allah ido , Tun da har ya hada su , Haka zalika zai sa soyayyar da ke cikin zuciyar AMIR ta fito fili , na mu kawai mu taimaka musu idan za mu iya "

kara fadada murmushin ta RIANNA ta yi ta na fadin " Ammie Allah ma ya ce tashi na taimake ka , dole sai mun saka Hannu cikin lamarin su "

" To ya ki ke so mu yi , ni fa ban taba jin AMIR ya bude baki ya ce ga kalar matar da ya ke so bare har mu yi wani kokarin sauya ta "

" no Ammie ba wani sauyawa , a hakan ma ta yi , ni dai na san AMIR ya na son mace mai kwaliya , ba ki lura da irin kallon da ya ke yi mata dazu da safe , ni dai na san ko bai fada ba , kwaliyar ta ta burge shi "

yar karamar dariya MALIKAT INAS ta yi kafin ta ce " Oh dama kin san da wannan shi ya sa ki ka shirya ta tun da safe haka "

" me ki ke tunani na sani mana , ai duk fadin masarautar nan babu wanda ya san AMIR sama da ni , ke dai ki sha zama kawai za ki sha kallo " RIANNA ta fada cike da kwarin guyiwa allamun ta shirya wata a kassa

ita dai MALIKAT INAS ba ce komai ba kawai ta zuba wa Inaya idanu


β–ͺAMIR


bayan ya fito part din MALIKAT INAS kai tsaye part din Malik ya wuce , kafin ya shiga sai da ya cire Alkyabar shi ya mikawa Azim da ke biye da shi sannan ya shiga building din
kai tsaye hawa na biyu ya nufa , nan ya tardo Malik tare da wasu manyan mutane biyu

ko gaishe su bai yi ba , sallamar shi ma shi kadai ya ji abu ne
kai tsaye ya nufi wata sofa ya zauna , zaman nan irin na gasaita

sai da ya zauna sannan Malik ya ce mishi " AMIR , Azim bai fada maka ka same ni a fada ba "

cikin ko in kula AMIR ya ce " ya fada min "
" Me ya sa ba ka je ba to , saboda kai musaman na shirya zama amma ba ka zo ba " Malik ya fada ya na nuna bacin ran shi
a hankali AMIR ya gyara zaman shi ya na fadin " Next time "

dan murmushi Malik ya yi ya na gyada kan shi kafin ya ce " okay na san ba za ka manta da wadanan nan ba , Sarkin Dogarai Hussein Bin Hashim da kuma Sarkin Bayi Mohammed Magid "

gyada kan shi a hankali AMIR ya yi kafin ya ce " Yes ban manta da su ba , ba wannan ne ba ya taba tsula min bulalar bayin shi ba " ya fada ya na nuna Sarkin bayi da ido

a tare duk su ka yi dariya sannan Sarkin bayi ya ce " To ina neman Afuwar Yarima , akasi ne a ka samu a ranar "

dan tabe baki AMIR ya yi ya na kauda kan shi gefe
sai da su ka tsagaita dariyar su sannan Malik ya ce " Kar ka manta matsayin uncle din ka su ke "

cikin nitsuwa AMIR ya katse shi da cewa " Abbi ba sai ka fada ba na sani , wannan shi ya ke auren MALIKAT MANISHA yarinyar MALIKAT HOUDA , Wannan kuma Yarinyar MALIKAT YOUSSRA " ya fada ya na nuna Sarkin bayi da ga karshe

Jinjina kan shi Hussein ya yi kafin ya ce " Ashe dai ba ka manta da mu ba "
" no " ya fada a takaice kafin ya mike ya nufi lift ya shiga ya nufi hawa na uku , ya na hawa ya wuce kai tsaye bedroom din shi

A cen kassa kuma inda ya baro Malik , sai da su ka Kamala tatauna war su a kan matsalolin da su ka shafi masarautar sannan ko wane ya tashi ya kama aikin gaban shi


β–ͺNESRINE


bayan sun baro AMIR da Inaya kai tsaye part din MALIKAT HOUDA su ka nufa
A tare duk su ka yi sallama kafin su ka karaso cikin parlourn inda MALIKAT HOUDA ke zaune saman sofa ga table a gaban ta shake da fruits

a gaban ta su ka zube saman guyiwowin su sannan Diya ya ce " gaisuwa na ke ya shugaba ta "

dan karamin murmushi MALIKAT HOUDA ta yi kafin ta ce musu su tashi ita ba ta son wannan gaishe gaishen na shirme

yar karamar dariya Diya ya yi kafin ya ce " An gama ran ki shi dade , dama mun zo ganin mahaifiyar su ne "

" ka ce yaran Amina ne , Masha Allah , sannun ku to , tashi ku je ta na cikin daki na uku " MALIKAT HOUDA ta fada ta na murmushi , matar nan ba ta da matsala sam ita kowa na ta ne dalilin da ya sa ma AMIR ya ce a kawo mama wajen ta

ba musu su ka tashi su ka nufi corridor din bedrooms su ka shiga ta uku
nan su ka tardo mama zaune saman gadon ta , ta kurewa waje guda ido kamar mai tunanin wani abu

Nesrine na ganin ta yi gudu ta fada jikin ta na sakin kuka
sai a lokacin mama ta dawo cikin hayacin ta , ta daura hannun ta guda saman bayan Nesrine ta na fadin " lafiya ki ke kuka tun da safe haka "

a hankali Nesrine ta dago da ga jikin mama ta kai hannu ta fara goge hawayen ta , ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " ba komai mama kawai na yi kewar ki ne "

dan karamin murmushi ita ma mama ta yi kafin ta juya ta kali Diya da Abdoul da ke tsaye bakin kofa ta ce " Abdoul , Moussa ku nan za ku tsaya "

yar karamar dariya Abdoul ya yi kafin ya karaso cikin dakin ya na fadin " mama ba fa sunan shi Moussa , sunan shi Diya "

" Toooo , da gaske ne malam Moussa " Mama ta fada ta na kallon Diya

dan karamin murmushi ya yi kafin ya gyada mata kai allamun eh da ga haka kuma ya ce " ni zan koma , zan dawo inda na samu dama " ya na gama fadar haka ya juya zai bar dakin

sai da ya fita sannan mama ta kali Nesrine murya kassa kassa ta ce " ba za ki tashi ki raka shi ba "

turo dan bakin nan nata ta yi ta na shirin magana mama ta riga ta cewa " idan ba ki tashi ba sai na sabba miki "

ai ko ta na jin hakan ta yi sauri ta tashi ta bi bayan Diya
ta ko yi sa'a bai gama fita corridor din ba sai ta yi mishi gyaran murya sama sama

cak ya tsaya ya juyo a hankali , ya na ganin ita ce ya saki wani cool murmushi ya ce mata " lafiya ? ki na bukatar wani abu ne "

A hankali ta girgiza mishi kai kafin ta fara takowa gare shi a hankali ta tsaya gaban shi ta dan sunkuyar da kai ita ta ma rasa abun da za ta ce mishi

dan karamin murmushi ya saki kafin ya kai hannu saman habar ta ya dago kan ta , ba shiri ya kai dan bakin shi saitin kumatun ta ya yi mata kiss sannan ya ce " ni ma zan yi kewar amma ba zan jima ba " ya na gama fadar haka ya janye hannun shi ya juya ya ci gaba da tafiyar shi

ita dai malama Nesrine ta yi sumar tsaye abun da ta zo fada daban abun da ya gane daban , a hankali ta dago hannu ta daura saman kumatun ta
ba ta san lokacin da wani cool murmushi ya subce mata ba , da sauri ta kai hannayan ta biyu ta boye fuskar ta ta na ci gaba da murmushin ta wai ita ta ji kunya

( da ga baya kenan 🀣🀣🀣🀣 )

sai da ta gama tsayuwar ta sannan ta juya ta koma dakin mama
ta na shiga ta Haye saman gadon baki daya ta konta ta tada kai da cinyar mama
dan karamin murmushi mama ta yi kafin ta daura hannun ta saman kan Nesrine ta ce " ina ku ka baro min auta "

murmushi mai dan sauti Abdoul ya yi kafin ya ce " su na tare ita da Zayd "
" ina son Ganin su don Allah " mama ta fada ta na marairaice fuska

yar dariya Abdoul ya yi kafin ya ce " mama ni dai yanzu tsakani na da Zayd sai dai gaisuwa , wlh ba zan iya tafiya ba na ce ki na neman sa , karfi na bai kai cen ba , ita dai Auta ba matsala Nesrine sai ta kirawo miki ita "

" To abun har ya kai haka yaushe ka fara jin tsoron Zayd " mama ta fada cikin zolaya
[16/09 Γ  09:57] M.N.M:

❀⚘ EXILED PRINCE ⚘❀


(LOVE MEETS POWER ) πŸ‘‘πŸ”₯




πŸ’”πŸ₯€ ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) πŸ’”πŸ₯€





πŸ‘‘β€ MALLAKIN MEERAH β€πŸ‘‘



【THE ROYALTY LOVE πŸ‘‘πŸ•ŠπŸ’–γ€‘




Marubuciyar littafin
【TAURIN ZUCIYA πŸ’–πŸ’πŸŒΊγ€‘





【 BOOK …………………… 2 ❀ πŸ‘‘γ€‘





____________________πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š___________________




ο½›PAGE _______8❀πŸ”₯}





ta na gama fadar haka ta bace bat a wajen
( bari dai mu bi ta mu ji ina ta tafi πŸ€”πŸ€” )

sai ga ta nan tsaye ta bayan masarautar wajen da ko guards babu a wajen ita kadai tsaye kasan wata katuwar bishiya
ta na tsaye a haka wani mutun ya fito zaune a kassan bishiyar , Ya na sanye da wadanan kayan na shi bakake , kamar dai kullum fuskar shi a rufe ta ke , da rawanin nan baki , idanun shi kadai a ke iya gani

a hankali ya bude baki ya ce " lafiya ki ka kirawo ni "

cike da bacin rai Rouksar ta ce mishi " Damba , akwai matsala fa , yarima ya na tare da wata shegiyar yarinya da ta lake mishi , shi kuma ba ya ce mata komai "

cikin ko in kula Damba ya ce mata " sai me , kema ba mace ba ce ki jawo hankalin shi mana , kar ki sake kira na da wannan shirmen , ba da zama ki ka shigo masarautar nan ba , mulkin saudiya za ki amso mana dan haka ki tashi ki yi aikin da ya kawo ki , ko kuma "
ya na gama fadar hakan ya ga wani dankareren maciji ya nufo shi ya na neman ya sare shi

cikin zafin nama ya damko kan macijin nan ya na kallon Rouksar ya ce mata " ke Medusa , ki kula da abubuwan wasan ki " ya na gama fadar haka ya tila mata macijin a fuska da ga nan ya bace a wajen ya bar nan tsaye
kamar da wassa macijin nan ya koma cikin gashin ya bace bat cikin jelar , nan take ita ma ta bace , sai ga ta dawo cikin toilet

kofar ta nufa ta bude ta ta fito , kai tsaye bedroom din ta fito ta dawo cikin parlourn inda ta bar tesnim ko motsi ba ta yi ba , ko sannu ba ta ce mata ba ta nufi wajen da ta taso ta koma ta zauna ta dauki wayar ta


* AMIR


zaune su ke cikin dining room din part din Malik , kamar dai kullum abincin dare a tare su ke

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login