Showing 30001 words to 33000 words out of 45645 words

Chapter 11 - Hauwa Kulu Book 2 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

135

Innar Hauwa da Hauwa a yau ba sai gobe ba, koma musu yayi kamar sabon kamun hauka, don cewa yayi da matar ba inda zai bari ta je sai ta hada shi da Innar Hauwa, ta ce itafa bata san gidan mai maganin da aka kaita ba, sai yace to su kai shi gun makwabcin nata da ya kai ta Albasu ne koma ina ne, in ba haka ba itada makwabcin na Inna zai yi karar su ga hukuma kan cewa sun batar da bayin Allah.
“Yau nake ganin abun da ya gagari Kakata” in ji Tafada mai Tuwo, daga abun arziki zaka daura min jakar tsaba kaji su bi ni, ni fa tsakanina da Innar Hauwa mutunci ne kawai, Allah ya gani ko a kwanciyar nan da tayi sau biyu ina taya Hauwa kinkimar ta ta kai ta asibitin Kuroda amma bata yarda ta kwana, yadda kake tunanin mu muka batar da su, to akan me? Daga zaman amana???”
Malam Isa ya lallashi Tafada yace, “kada ki damu ba kya ganin a fusace yake? Ina ne gidan makwabcin nasu?” Ta nuna gidan dake jikin na Innar.
Aka yiwa makwabcin su Inna sallama ta hanyar tura yaro cikin gidan sai gashi ya fito, suka gaggaisa da Malam Isa yace “Tafada ya akayi? Tace ga masu neman makociyarka nan, har suna neman kala mana sharri wai mun batar da ita”. Malam Sani Albasu yayi dariya yace, “Innar Hauwa mai jama’a, ho! Tana can kauyen mu gidan Malam Bagobiri mai maganin gargajiya na Albasu, in kuka je Albasu duk wanda kuka tambaya gidan Malam Bagobiri ya sani, ko daga tashar Albasu ne kukayi tambaya za’a kai ku har gidan sa”.
Sarham yace “me zai hana ka daure ka rakamu kawai, ina ganin zaifi sauki, tunda kai ka kai ta?
Malam Sanin ya yarda zai rakasu har Albasu, Amma yace saidai su dawo gobe yanzu yamma tayi.
Sarham, Wanda hakurin sa ya tuke a lokacin sai yace da Malam Isa su je kawai su yi tambayar har su samu gidan. Malam Isa ya yarda don yaga damuwar sa karara, ya yarda cewa wannan bawan Allah Sarham, da gaske ya damu da Innar Hauwa Allah kadai ya san tsakanin su.
Musamman filin gidan su da ya saye dinnan ya hau ginewa, duk da bai yi masa wani bayani ba ya fahimci yana da niyyar sake mayar musu da gidan su ne. Wanda baya ko tantama kulafucin ta da gidan, da unguwar bakidaya, da mutanen ta na arziki da aka raba ta dasu rana daya, sannan da makancewar tilon diyar ta rana daya, da kuma damuwar batan mijin ta Malam Bilyaminu dare daya, su suka taru suka haifar mata da kamuwa da ciwon zuciyar da ake cewa tana fama da shi a yanzu.
Malam Isa ya tuna Innar Hauwa yanzu mijin ta ya fi Shekara biyar da bata, me zai hana ta yarda tayi GAIBA in ya so shi ya aure ta ya rike mata 'yar ta guda daya ya killace su a gidan sa su daina rayuwar sayarda abinci a Tasha?
Shi kadai yake wannan tunanin na babu gaira babu dalili har suka isa Albasu.
Malam Isa ya tafi tunani bai san har sun shiga garin Albasu ba, sai da Sarham yayi masa magana yace “gamu cikin Albasu” suka tsayar da motar a gefen titi Malam Isa ya tambayi wani mai Amalanke ko ina ne gidan Malam Bagobiri mai maganin gargajiya?”
Mai Amalanke yace “kun baro gida can farkon shigowa gari, ku koma da baya ku tambaya” Sarham yace “in dai ka san gidan shigo ka kai mu, zan baka kudin Babur ka dawo”.
Hakan kuwa aka yi, mai amalanke ya shiga bayan motar yana nuna musu hanya har kofar gidan malamin.
Wato abun babu kyawun gani, Yaa Subhanallah! Marassa lafiya ne rututu a zube a kasa tun daga zaure, cutututuka iri daban daban masu tasa tsigar jiki. Sarham sai da ya dauke numfashin sa na lokaci mai tsaho sabida kazantar gidan da cunkoson marassa lafiya. Tausayi da haushin Inna ya kama shi, wato har yanzu tana nan da halin ta na rashin yarda da asibiti kamar bai isa ace ta dau darasi tun akan Hauwa ba?
Ganin cewa jinin sa na neman hawa, sai ya umarci Malam Isa ya yi musu sallama da malamin, aka ce ai sai sun hau dogon layin ganin sa yanzu kuma dare yayi, saidai su dawo gobe da safe.
Malam Isa yace da Tafada “shiga kawai ki fito mana dasu, ya gansu hankalinsa ya kwanta, don ni kam ban iya kwana garin nan”.
Tafada ta shiga gidan da sallama, wani ikon Allah da Hauwa ta fara tozali, wadda ke bakin kofar dakin da Inna ke kwance, Hauwan kuma nan da nan ta dauki muryar ta, ta kira sunan ta da ‘yar dusassar murya.
“Tafada, kamar muryar Tafada nake ji”.
Tafada ta isa ga Hauwa da sauri, wadda tayi kozai kozai tayi zuru-zuru, rabon ta da wanka yau kwana bakwai, wato tun kawo su da Malam Sani yayi kauyen nan ya tafi, ya kuma karbe duk ‘yan kudaden hannun su da sunan yana biyan mai magani, amma kullum jiya I yau, babu wani sauki a tare da Inna sai na Allah. Yau kam wuni tayi tana suma babu wanda ya tsaya a kanta sai Hauwar da ba gani take ba, itama an gaya mata dai uwarta na suma.
Don haka yau Hauwa ta wuni kuka wurjanjan har ta gode Allah, idan ta rasa Inna, bata san yaya zata cigaba da rayuwa ba.
Tafada ta gaisa da mutanen data gani a zazzaune kafin ta kama Hauwa ta ce “nice Tafada, ina Innar taki wani ke ta son ganin ta tun daga Kano ya sako mu a gaba saida muka kawo shi nan, kamar dai dan uwanku ne”. Babu wanda ya zo wa Hauwa a rai da zai biyo bayan su har nan, cikin ‘yan uwan su duka sai Yaya Jamilu! Watakila yayi ta tambaya ne a kansu har ya gano inda suke.
Tafada tayi mata jagora suka fito, a yadda Hauwa ta lalace ba don yayi mata farin sani ba da bazai gane ita ce ba, sabida yadda tayi baki ta kuma rame, Sarham ya runtse idon sa cikin tausayi marar misali, muryarsa na shakewa da sarkewa yace.
“MAI-JID-DAH!”.
Sai tayi sak! Da rai da kwakwalwarta cikin son tuno inda ta san sassanyar muryar, da kuma inda ta taba jin an kira ta da wannan kebantaccen sunan. Duk fadin duniya mutum daya ne ya taba kiran ta da “Maijiddah”, ya kuma ce sunan nashi ne shi kadai, bai yarda kowa ya kwaikwaya ya kira ta da shi ba wato LIKITA SARHAM!!!
Hauwa-Kulu ta yi shiru na wucin gadi, kwakwalwarta na faman processing tattausar muryar data kira sunanta. Muryar Likita Sarham ce tabbas, wadda ko mutuwa tayi ta dawo bazata manta ‘accent’ dinta ba. Wani kwayan mutum guda daya da komai nisan shekaru bazata taba mantawa da shi ba, saboda kyakkyawar rawar da ya taka cikin rayuwar ta da gudunmuwar da ya basu, a lokacin da rayuwarta gabadaya ta dauko nakashewa. Duk da a cewar Hauwa, shi Sarham din shi ya karasa mata idanu, wato shi ya karasa makantata, amma bayan faruwar hakan ya kyautatawa rayuwar su, ya kuma taimaka ya hana rayuwar ta karasa rugujewa, ya karfafa mata da cewa kada ta bari ta durkushe a dalilin makanta.
Rawar da Dr. Sarham Abbas Shanono ya taka cikin rayuwar su, duk da cewa ta dan lokaci ce, to fa hakika mai girma da muhimmanci ce domin ya nuna musu kauna da mutunci na masu ilmi. Da wuya ka samu mutum irin sa a wannan zamanin da yake yiwa talakawa da yafi matsayi da ajin rayuwa kamar su daukar mutane. Balle don wani tsautsayi ya faru a dalilin aikinsu su tsaya su yi waiwaye a kai. Ta tabbata da ace bai tafi inda ya tafi ba, da ba’a kawo wannan matakin ba a lafiyar Inna, da karatun ta, da komai ma na rayuwar su, ta tabbata zai cigaba ne da tsayawa rayuwar su kamar Baba da Zulkiflu na raye. Da bazai bari Zakari ya tozarta rayuwar su ba ya raba su da farin cikin su.
Bata yi masa farin sani ba, saboda ko sanda yake tare da su kullace take da shi, bata tsaya ta saki jiki dashi ba, balle ta saba da shi, ko tayi masa kyakkyawan sani, amma ko daga sanin nesa nesa din data yi masa a gidan su ta shaida cewa shi din mutumin kirki ne, mai taimako ne, mai yawan alkhairi ne, ya san (human dignity), kuma yana matukar kaunar su sosai.
Sai hawaye ya soma zubo mata, don ji tayi ma kamar BABANTA MALAM BILYAMINU YA DAWO! Tamkar wani ‘SAVIOUR’ (mai ceto) ya iso cikin rayuwar su, koko tace kamar wani Mala’ikan rahma ya riske su, a lokacin da Inna ke kan gargarar mutuwa cikin rashin gata, kuma a lokacin data fidda rai da tashin Inna.
A can cikin kunne da kwakwalwarta, Hauwa ta tsinkayi muryar nan ta Dr. Sarham mai sanyi da gardi tana tsokanarta, zolaya irin wadda baya rabo da ita, kuma ya saba yi mata don ya samu ta kula shi. Aka ce a bar hali a ci me? Dr. Sarham har yanzu yana nan da (jovial personality) din sa. Hausawa suka ce in ka shekara baka ga mutum ba, ranar da kuka hadu, tambaye shi wani abun daban amma banda halin sa.
Wato a nufin bahaushe halin mutum baya taba canzawa sai dai ko mu ce Sarham ya rage wasu daga cikin halayen sa na sakin fuska, da yawan magana, a dalilin girma da nauyin iyali da yanzu ya hau kan sa.
“A yi magana ki ce an yi miki “GORIN IDO”, dubi kwala-kwalan idanun nata a jike jagab, jawur dasu, kamar kosan da ya soyu a cikin mai don kuka, maimakon ta saki far’a tace “Jabbama-jabbama…lale-maraba da bakon KANO. Ko tace YAYA SARHAM SANNU DA ZUWA”.
A’ah ta tsaya tana mana ambaliyar hawaye, watakila anan garin nasu na Albasu, da haka ake saukar bako”.
Sarham ya fada cikin zolayar Hauwa-Kulu, don rabata da hawayen dake ta satatar mata, da kokarin sa na hadiye nasa hawayen. Ba kankanin abu ke sa shi kuka ba, amma a yau ya san in bai yi da gaske ba ‘he cannot control his tears’ a gaban Hauwa, abinda bazai so hakan ba ko kadan. Kokarin gaske yayi da ya iya hadiye hawayen sa a kan idon Hauwa, wadda yake ma kallon kanwa ta jini, kamar Sumayyah, yadda ba zai iya bari Sumayyah ta ga raunin sa ba, haka ba zai bari Hauwa ta gani ba, ba don haka ba da tuni ya sake su sun shatato shima akan kundukukinsa, kamar yadda Hauwan ke faman yin nata, amma fa ita nata na farin ciki ne.
Ganin yanayin wahala da rashin lafiya da ya same su ciki kuma a kauye ya karya zuciyar sa, wanda ba cikin sa ya tafi ya barsu ba.
Cikin muryar kuka Hauwa ta ja sheshsheka ta ce “Likita sannu da zuwa”, tana mai yi ma saitin da muryarsa ke fitowa kallon ga ZULKIFLU YA DAWO.
Sarham ya matso gaban ta har tana iya shako kamshin hamshakin turaren sa na ‘Oud Abyad’ ya ce “to ko ke fa Maijiddah! Amma kawai daga ganin mutane sai ki balle da bokitin hawaye? Ai sai su Malam Isa da Tafada su dauka baki yi maraba da zuwa na ba sam”.
Tayi murmmushi, har kuncinta ya lotsa ciki sosai, wani abu da ke kara ma Hauwa’u kyau, yace “maza je ki kwaso kayan ku, Inna Tafada taimaka min ki dauko Inna don Allah a sa min ita a bayan mota, in yi maza in kaita asibiti, a kula min da ita da kyau”. A yau yana dakacen inama shi ba likitan ido bane, na zuciya ne! So that ya iya duba Innarsa da kansa”.
Hawayen dadi ya sake kecewa Hauwa, don ita ai tayi-tayi Inna ta yarda ta zauna a asibitin Murtala a cigaba da dubata ta ki, tace in mutuwa ce ta isko ta, a barta ta mutu a cikin dakin ta yafi mata, ta fi so ta mutu a gida akan gadon asibiti, kada taje a kai gawarta mutuware a ajiye a firinji, a kuma jinkirta yi mata janaza.
Kuma ita har gobe bata yarda da maganin asibiti ba, don bata ga ranar da ya yiwa idanun Kulu ba, aikin Kulu yasa ta kara nesanta kanta da asibiti, dama dole ce ta kaita a kan Hauwa dinma, shi yasa tunda ta fara ciwon nan suke dambarwa ita da Hauwa akan zuwa asibiti, daga bisani Hauwa ta dauko shatar mota tace mata zasu je asibitin Kuroda a bata magani kadai su dawo, da suka je asibitin, kallo daya likita yayi mata yace kwanciya zasu bata.
Hauwa bata ankara ba sai ji tayi Inna ta tashi tsaye tace ta tashi su tafi, data tsaya yi mata magiya da gardama kan ta tsaya sai Inna ta kamo hanya abinta, ta kyale Hauwa a tebirin likita, dole Hauwa ta taso ta biyo bayan ta tana kira. Tausayi yasa ta dakata ta kama hannun ta, a lokacin suka taho gida.
Hauwa bata daddara ba, washegari tayi ta rokon ta kan su je asibitin Murtala, ta tabbatar mata su bazasu kwantar da ita ba, da kyar da nacin kukan Hauwa Inna ta yarda suka je Murtala, nan suka hau layi har suka samu ganin likita, anan ne likita ya yiwa Hauwa bayanin dole Inna ta kwanta ayi mata aiki a zuciya, domin ta samu rami (hole) a zuciyarta. Ai jin haka Inna ta mike ta fice ta bar Hauwa da likita suna kiranta (again), Hauwa ta biyo bayan ta tana kuka da roko, sai Inna ta dakata da tafiya tace da Hauwa.
“Idan kin manta haka aka ce min za’ayi miki aikin ido ki warke daga hakiya, amma kin warke din?
To ni yanzu in aka yanka min zuciya kina da tabbacin zan mike?
Ba tsoron mutuwa na ke ba domin kuwa a shekaru hamsin me nake jira banda neman hanyar dacewa da cikawa da Imani?
Ke nake ji Hauwa-Kulu, in babu ni, rayuwar ki zata shiga wani hali na garari da walagigi har da da bara akan titi, don baki da mataimaki da mai yi miki jagora bata idanu kadai ba harma da rayuwar ki gabadaya, sai Allah da ya halicce ki”.
Abinda Inna bata sani ba, ko babu ita Innar, ita HAUWA-KULU (modern makauniya ce), bata bukatar dan jagora don zuwa wani waje, kanta tsaye take zuwa ko’ina, iyakaci kai in ka fahimci bata gani kai ka kauce mata, wata irin brainlliant ce mai kaifin kwakwalwa da kaifin basira, gata da ji mai karfi irin na wadanda suka rasa idanun su da kuruciyar su Allah ya bata. Don dai UWA-UWA ce amfaninta yafi ga haka, wato ya wuce ta rayu don ta yi mata dan jagora, sai dai don ta zama GARKUWAR ta a rayuwa bakidaya kuma cikon farin-cikinta ta.
Tun daga ranar bata kara yarda Hauwa ta ja ta asibiti ba, tayi ta kwanciya a gida suna cinye dan jarin nasu a sayen abinci kullum, tunda ba juyawa ake ba yanzu kashewa ake yi yasa kullum daurin kudin su sai kasa yake yi, kafin makwabcinta Malam Sani mai irin ra’ayin ta kan traditional medicine ya ce da gaskiyar ta, tazo ya kaita gidan mai magani inda zata samu magani na kowacce cuta ba tareda an tsaga kirjin ta ba.
Aka fito da Inna daga cikin gidan ranga-ranga da daurin kayan su a bakko, aka sa a bayan motar Sarham, Tafada da Hauwa suka shiga, suka sa Innar a tsakiyar su, wadda bata san ma ko su waye a kan ta ba lokacin. Rabin jikin ta na kwance jikin Hauwa. Malam Isa na gidan gaba Sarham ya ja motar cikin nutsuwa da hanzari suka hau titin da zai maida su cikin birnin Kano.
Suna tafe a hanya suka fahimci Inna ta farfado daga suman data yi, suka yi ta yi mata sannu da jiki. Malam Isa nata yiwa Inna fada da dacin rai, na yadda ta shiga duniya ta bar makwabtan ta masu kaunar ta, wai ace yanzu ta gwammace rayuwar sayar da abinci a tasha a kan zaman gidan sa, yace to yanzu me kika tsinto a tashar duk sana’ar taki ban ga kinyi arziki ba, ban ga kinyi kiba ba, na gan ki tsiya-tsiya rakace-rakace wutsiya a zage cikin ciwo.
Rayuwa bata raggo bace. Haka azzaluman mutane ba’a kyale su su cigaba da aikata zalinci son ransu ga marassa karfi a doron kasa musamman mata da kananan yara kamar Kulu.
Da kin zauna mun tashi tsaye mun hada karfi da karfe mun kwato miki hakkin ki, yadda makwabtanki suka fusata a lokacin da kin tsaya, in yafi karfin ki ai bai fi karfin shari’ah da Alkali ba, cewa fa mukayi ki tsaya zuwa wayewar gari mu shigar da kararsa maimakon mu dau Shari’ah a hannunmu.
Kuma ni da kin zauna kin yi gaiba, na rufa miki asiri na killace ki a gidana karkashin inuwar aure in taya ki kula da ‘yar makauniyar ‘yar ki, amma ina! Ke ga ki kububuwa sarkin masu zuciyar duniya, kika dauki ‘ya ba ido kika bar BADALA!”
Sarham ya rage gudun motar sa a dokar daji, a fusace yace “wallahi Malam Isa in

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login