Showing 12001 words to 15000 words out of 45645 words
daga can saman bene, tsaye a jikin balcony, ya harde hannayen sa a kirjin sa ya juya bayan sa daga kofar shigowa, don haka bai ga shigowar ta ba, da alama yayi zurfi a cikin tunani.
Madinah tana tura kofar cikin sa’a ta taddata a bude, don haka kai tsaye ta sa kai, ta kuma haura ta matattakalar benen ta cimmasa har inda yake.
Kamar cikin mafarki, kamar kuma irin gizon da ta saba yi masa cikin ido biyu, haka ya ga Madinah Attahiru tsaye a gaban sa, (for the second phase) na rayuwar su. Tana sanye da shudiyar abaya kirar Dubai da mayafin ta, ya sha mamakin biyoshin data yi, a irin sanin da yayi mata wajen tsare mutuncin ta da tsare ajin ta, wato tun saninsa da ita… maintaining self-esteem dinta yana sama da komai a gareta, a kuma irin yarfawar da yayi mata dazunnan.
Wadannan, dama wasu dalilan, su suka sa ya kasa wofintar da ita, ko bar mata wajen kamar yadda yayi niyya da farko. Musamman ganin kyawawan idanun ta sun cika taf da kwallah, gab suke da ballewa bisa sassalkan kundukukinta, tace cikin rishin kuka.
“Yau ma in ci albarkar garin MADINAH……Madinah garin Manzo, in ci albarkar kasancewa ta MADINAH AL-MUNAWWARAH, mafaka ga kuncin dukkan musulmi, a lokacin da suka shiga cikin matsin mushrikai, da abokan gaba, suke neman inda zasu samu tsaro da kwanciyar hankali, Madinah ta zamo mafaka ga Manzonmu (SAW), don haka nake rokon albarkacin ta ka saurare ni, ka bani mafaka daga kuncin zuciyar dana ke ciki a cikin kirjina”.
Bai ce komai ba, amma a fuskarsa wannan karon akwai sassauci, a idanun sa wannan karon akwai rahma, kai har da wani boyayyen sirrin da baya so ta ankara da shi. Yace.
“Me zan saurara daga gareki Madinah? Kada ki manta ni Sarham ba kowa bane, ba kuma dan kowa ba, dan Malaman makaranta ne, wadanda basu aje ba, basu kuma ba wani ajiya ba,” Madinah ta runtse ido kalamansa na mata zafi, tace “ka saurare ni ko na minti biyar ne, in labarta maka duk abubuwan da suka faru dani a lokacin”. Sarham yace “abu daya zan saurara daga bakin ki shine, meye DALILIN KI na kin nema na duk tsayin wannnan lokacin?”
Madinah ta ce “ban da dalili, bani da hujjar kare kaina” “then why are you here?” Tace “saboda in baka hakuri, in kuma kai ka gaban Daddyn nawa, don ya dade yana neman ka, ya gana da kai”. Sarham yace “ai in baki sani ba, duk wani mumini sau daya maciji yake saran sa a rami guda bisa kuskure ko kaddara, amma sara na biyu, saidai idan shi ya kai kansa da kansa”.
Madinah ta ce “duk da haka Sarham, na kuma yarda da kai. Wancan lokacin haka nazo na daukeka na kaika gabansa ba tare da sanin zai ci mutuncin ka da zarafinka ba, to yau ma hakan, at the same time, wannan lokacin ma ban san meyasa yake neman naka ba. But do me this favour, ko da itace alfarma ta karshe da zaka yi min a rayuwarka!”.
Daga wannan Dr. Sarham bai san meyasa bai kara musawa ba, ya samu kansa da bin bayan Madinah zuwa motar ta tamkar rakumi da akala.
**** **** ****
SULHU
S
un zauna shi da Daddyn Madinah a falon ganawa da bakin sa, Alhaji Attahiru yace “Sarhamu ba wani abune dalilinta ba, wanda ya hanata nemanka all this while, face BIYAYYAR IYAYE, ina fatan hujjarta wadda ta isa hujja a takaice, ta samu karbuwa a wurin ka, tunda kaima kana burin naka ‘ya’yan watarana su yi maka biyayya irin wadda Madinah take yi min.
Autata Madinah mai gudun zuciyar iyaye ce da son gamawa dasu lafiya, shiyasa bata daga ido akan duk wani umarninmu zuwa gareta, ba don ta daina son ka bane taki neman ka, a duka shekarun nan tana dakon soyayyar ka ne, ni da bata fadawa hakan ba amma nine shaidar hakan, amma a haka na rufe ido nayi mata aure da wanda hankali na ya kwanta da shi.
Wani irin dago kai Sarham yayi cikin slow motion, jin furucin Baban Madina na karshe, Alhajin bai damu da reaction dinsa ba ya cigaba da bayani,
“kafin Allah ya nuna min ayar sa a kan ku, wato kafin in kai ta gidan mijin ya dauke abin sa, a hanyar sa ta zuwa daukan ta zuwa gidan sa, ta sanadin hadarin jirgin sama.
Idan nace maka I was extremely shocked da mutuwar AVM as at that time, kaima ka san yayi kadan ya bayyana dimuwar tawa.
Da albarka ta yau nake cewa idan har yanzu kana ra’ayin auren Madinah to kaje ka turomin mahaifan ka su karba maka auren ta, bana bukatar komai sai sadaki”.
Duk da haka, duk da wannan ban hakurin da dattaku da Daddyn Madinah ya nuna a yanzu, da cewa da yayi yayi nadamar abinda yayi masa, ya kuma ce baya bukatar komai na auren Madinah daga gareshi sai sadaki, bai wanke zuciyarsa ba. Madinah ta sha matukar wahala kafin Sarham ya sauko, wato kafin ta samu ta shawo kansa ya sakar mata fuska ma kadai, domin wata ‘yar karamar zautuwa ce ta same shi akan maganar auren ta da marigayi AVM.
Duk da maganar ta zo masa bagatatan, amma bai yi mamakin jin ta ba, sabida shi kansa ya san Madinah ba matar bari bace ga maza ‘yan uwansa, ya kasa sake mata fuska in ya tuna wai har aure aka daura mata, shi bai yarda bama wai bata je gidan mijin ba, watakila Daddynta ya fada ne don ya rage masa zautuwa, amma dai ko yaya Madinah take Madinah ce a wurin sa, ya sani ba zai iya daina son ta ba, ko da kuwa ‘ya’ya goma ta haifawa AVM din, yaki yarda sam ya koma mata ‘jovial Sarhamun sa’, duk wani annuri ya kau daga kyakkyawar fuskarsa.
Rabuwar su ta wadannan shekarun da maganar daura mata aure da mahaifin ta ya sanar da shi sun sa ya canza da yawa daga halayen sa data sani na sakin fuska dayawan walwala, ko ace ita Madinah ta canza shi, ta mayar dashi tattaura, mai tsauri, kuma mai wuyar sha’ani. Duk da haka yana nan a ‘jovial’ Sarham din sa, wato mai far’a da faram-faram da mutane amma banda ga ita Madinah, sau tari sai yayi ra’ayi zata ga hasken hakoransa, ko inda wasu mutane daban yake tare. Duk Madinah ta jure wannan punishment din da bata da laifi, ta san wuyarta kawai su yi aure kawai komai zai zama labari.
Wani irin kishi ke cin ransa akan maganar auren Madinah da wanin sa, kuma taki su magantu akai sam, da ya kawo zancen zata bata rai, ta ki tankawa. In ya takura da tambayarta wani abu akan aurenta da AVM ko makamancin haka sai kawai ta saka masa kuka. Ko yaki ko yaso dole ya bar zancen.
Ba kamar can baya ba da kullum zaka tadda fararen hakoran sa (in yana gaban Madinah) a warwaje, ya kasa rufesu, kamar na mai tallan makilin dinnan ‘colgate’.
Yanzu kam saidai ka ganshi bay abo ba kuma fallasa, fuskar ta koma kadaran-kadahan a gaban Madinah. Itama dole yasa saida ta rage nata far’an gareshi, ayi mutum kamar mutanen farko ba yafiya ba afuwa ba manta abinda ya shige? Aka koma kadaran-kadahan din ita da shi, amma dai suna tare koyaushe a cikin asibiti ko a cikin campus, ko a gidansu a weekend, haka suka kasance har zuwa ranar da Surayyah ta gaya masa ‘graduation’ din ta daga BUK.
A ranar ne kuma Daddy, wato Alhajin su Madinah ya tabbatar masa ya bashi auren Madinah halak-malak, yaje ya zo masa da iyayen sa a tsayar da magana kawai.
Ko yaki ko yaso, hakika yaji farin cikin hakan maras misaltuwa akan wannan albishir din na Alhajin kamar yanzu ya fara jinsa, komai pretending dinsa kuwa, musamman da Daddyn da kansa ya kira shi a waya ya gaya masa da bakin sa da nasa, don haka ya ajiye maganar kishin matacce a gefe, yana cewa da sannu zai rama ne. Madinah bazata ci sadakin maza biyu abanza ba dole ta gane shima yanada ajinsa in ta shigo gidan sa, sai ta gaya masa ko sau nawa AVM ya samu alfarmarta, kafin ya yarda su yi rayuwar farin ciki irin wadda ya dade da yi musu tanadi.
Da wannan shawarar da yayi da zuciyarsa ya ajiye kishi a gefe ya koma na shirin tahowa gida, domin ya kammala kwas din da ya kaishi Jeddah gabadaya, a ranar yayi booking, zai taso a washegari, suka yi sallama da Madinah a asibitin Sarki AbdulAzeez, yau kam taga ‘yar walwalar Sarham, domin da zai tafi har yake ce mata duk ta yi baki ta rame, ina dalili?
Madinah taji wani irin sanyi a ranta sai ga hawaye sun digo. Shi bai san yadda canza matan da yayi completely da yadda yake treating dinta yanzu ne wai don ta auri wani kafin shi bisa rubutacciyar kaddarar ta ya ramar da itan ba, ya kuma maida ita bakar ba?
A lokacin sai bata bashi amsa ba, maimakon hakan, sai ta mika masa kyakkyawan kwalin dake sunke a hannun ta, mai dauke da kyawawan furanni da katon HAPPY BIRTHDAY card mai zanen zuciya. Sai a lokacin Sarham ya saki dariya don shi ya manta ma wai yau ne ya cika shekaru talatin da uku a duniya.
Tunda ya hawo jirgi yake tunani, Allah dai yasa Surayyah na kaiwa su Inna kudin da yake aikowa ta account din ta da yace ta dinga baiwa Sumayyah tana kai musu, ta san gidan, don sun taba zuwa tare, ya san dai Innar Hauwa jarumar uwa ce, cikin kowanne hali zata kula da kanta, kuma zata kula da Hauwa-Kulunta, ba zata bari ta zama (drop out from school) ba.
Dan abinda yake tura musu duk wata ya san zai ishe su cin abinci har wata ya zagayo, duk da ya san Inna bazata zauna haka babu sana’a ba, Allah yasa Sumayyahn kuma tana jure kai musu, kodayake Sumayyahn sa ba daga nan ba, wajen aikin zumunci da taya shi son duk abinda yake so, balle wadannan bayin Allah data fahimci sun mamaye rabin zuciyar sa!
Jirgin su ya taso daga Jeddah a washegari bayan sun yi sallama emotionally shi da Madinah a filin jirgi, yanata kissima abubuwa daban daban a ransa, wadanda zai je ya tarar a Kano, akan dai Inna da Hauwa, da rayuwar da suka samu kan su a bayan babu shi. Sarham ya sa a ransa ba zai koma Jeddah dauko matar sa Madinah ba wannnan karon sai ya mallakawa Inna wayar tafi da gidan ka komai kankantar ta, don dai ya dinga jin lafiyar su kai tsaye, ba tare da ya saka ‘third party’ a tsakanin su ba.
**** **** ****
T
axi din da Dr. Sarham ya dauko shata daga filin jirgi bata sauke shi a ko’ina ba sai a kofar gidan su. Wanda ke cikin rukunin gidajen malamai na sabuwar jami’ar Bayero.
Surayyah ce ta fara hango shi daga tagar dakinta, daidai lokacin ta dage labule don samun iska kasancewar ‘nepa’ sun yi mata halin su na dauke wuta tana tsaka da shaqar barcin rana cikin A.C, wani hucin zafi ya tada ta, don haka ba shiri ta tashi ta dage labulen ta don ta samu ‘natural’ iska ta shigo mata, wannan ne yasa duk gidan ita ta fara ganin sa yana fitowa daga mota.
Banda ‘jini’ sunan sa ‘jini’ da Surayyah bazata gane Bhaiyan Sumayyah ba sam, ko ta ce Yaya Doctor yadda take kiran sa ita, sabida girman da ya kara da irin canzawar da yayi a shekaru ukun da ya kwashe a kasar Saudi-Arabia, ilhamarsa da cikar zati sun karu, sun ninku akan wadanda ya bar gida dasu. Yayi haske kadan, fatar jikin sa ta yi ‘fresh’ kamar wanda ya shiga injin wankin fata.
Karadin Surayyah shi ya tashi Sumayyah dake falo a gaban TV tana kallon diramar Hausa, ta yo dakin nata a guje don ta dauka wani abu ne ya same ta, da karfi Surayyah tace, “Summy Bhaiyan ki ne, Yaya Doctor ke shigowa”.
To amma me? Sai ta tuno wani abu, wanda yasa nan da nan ta nutsu, ta daina murnar dawowar Bhaiya, gashi dai ya dawo ‘unexpected’, gashi ta masa babban laifi, tace cikin damuwa.
“Summy na dauka ba yanzu zai dawo ba, na saka a raina kafin lokacin da zai dawo na hada kudin nan na baki sakon nan na mutanen nan kin kai musu duka a dunkule”.
Sumayyah ta ce cikin mamaki “wane sako? Wadanne mutanen?” Cikin damuwar data fi ta baya Surayyah ta ce. “Ki min afuwa Summy, ban taba gaya miki Yaya Doctor yana aiko kudi ta account dina in baki ki dinga kaiwa mutanen nan nasa talakawa da ya likewa na kofar Na’isa ba, ni wallahi na ma manta, sai yanzu dana ganshi na tuna”.
Ta kara da cewa “Summy don girman Allah ki rufa min asiri in ya tambaye ki kice ina baki duk wata kina kaiwa, in yaso zan dunkule duka abinda ke hannu na a yau in baki ki kai musu kafin ya je gidan, wallahi cosmetics (kayan kwalliya) and other stuffs kawai nake karawa da su duk wata, saboda Mama bata yarda ta saya min irin wadanda nake so.”
Idon Sumayyah har rawa yake don bacin rai, da tsoro da mamakin abinda ‘yar uwarta ta aikata, har ta fara hango irin hukuncin da Bhaiya zai mata, ta fara hango shi ya dauke Surayyah da mari kodayae Bhaiya baya duka baya zagi, amma fa bai iya fushi bay a kuma kware da (silent punishment), fatar bakinta ma rawa take yi, ta kasa murnar dawowar tasa ma don haushi da mamakin Yayar ta Surayyah, da kyar Sumayyah tace,
“kin ci amana amma, Yaya Surayyah kin ci amanar Bhaiya, na rantse da Allah babu ruwa na, count me out of your dirty game”.
Daga haka Sumayyah ta fice da gudu tana “Oyoyo! Bhaiya, Mama Bhaiya ya shammace mu”. Sai ga Mama ta fito daga dakin ta itama kan ta ko kallabi babu, tace “really?” Surayyah kuwa bayan gida ta shige ta boye kanta, jikin ta ba inda baya rawa.
Sumayyah ta kusa kai Sarham kasa sakamakon tsallen da tayi ta shako shi da sunan murna. Haba! Sarham sai ya balle da fada blah! Blah! “Sumayyah meye haka? Baki san kin girma bane? Ko an ce miki da da yanzu ma daya ne? Bana son irin wannan haukan welcome din, an wuce wajen, kada ki kara”.
Mama ta iso falon tana cewa “kai mai hali dai baya fasa halin sa, kai kuma daga zuwa sai fada kamar tsiduhu? Shekara uku ba kwana uku ba basu saka ka a idon su ba, ba dole su yi murnar ganin ka bagatatan yau ba?”.
Sarham ya mike ya isa gareta ya kama hannayen Mama ya rike cikin tafukan sa, yana murmushin farin ciki ya kai su ga fuskar sa kan sajen sa, wanda a baya kafin ya tafi bashi da shi yace “My Mommah, I missed you badly kin sani. Amma autar ki bata san ta girma ba, kullum tana nan jiya I yau shiyasa bazan daina fada ba”.
Kafin kace meye wannan gida ya kacame da murnar dawowar Dr. Sarham. Da Abba Prof. ya dawo murnar tafi armashi, a ranar har dare suka raba a falo suna hirar yaushe gamo, amma an nemi Surayyah an rasa a falon, tunda ta zo ta yi masa sannu da zuwa ta gudu gidan Kakar su Haj. Kulu a gadon kaya, don tayi-tayi Sumayyah ta karbi ‘yan kudin da ke hannun ta ta kai Kofar Na’isa, ta roke ta kan ta rufa mata asiri tayi maza ta kai musu tun kafin Yaya Doctor ya huta ya waiwayi zancen, wadanda ko kwatan abinda ta kashe daga abinda yake aikowa din basu kai ba.
Sumayyah ta ki amsa, ta kuma ce in ta takura mata ta cigaba da saka sunanta cikin laifi nan wallahi zata tona ta, “kawai ki yi harkar ki Yaya Surayyah ki rabu da ni, ni ba maciyiya amana bace kuma ba’a shirya rashin gaskiya da ni”.
Duk da ta san Sumayyah ta gaya mata bakar magana sosai amma ta kasa cewa komai wannan karon, girma da mutunci ai madara ne, kuma mutum shi yake rike kayan sa, ta yarda ita ta zubar da girman ta har Sumayyah kanwar bayan ta yau ta nemi zagin ta (in disguise). Don haka Surayyah ta ga gara ta gudu gidan Hajiya, inda ba abinda Sarham ya isa yayi mata in dai a gaban Hajiya ne koda ta bare da ita.
Washegari walima sosai Mama ta hada musu a babban falon ta, ta murnar dawowar Sarham da kammala zurfafa karatunsa, wato kwas din da ya je yi na tsayin shekaru uku a (KAU, Jeddah) ta kasar Saudi