Showing 6001 words to 9000 words out of 45645 words
nasu na Sarki Abdulazeez, bayan ya gama sha, ya tashi ya nufi kantar biyan kudi, ya zaro khamsoona riyals dinsa daga aljihu zai biya, kawai ya ji cashier din ya ce ai an biya kudin gahwar da ya sha.
Ya juya cikin tsanaki da mamaki, nan yayi ido hudu da Madinah Attahiru, his ex Madinah Sorondinki, tana masa kallon ashe kana duniya?
Zuciyar sa ta harba. Makwallaton wuyan sa ya motsa, amma ya kasa hadiyar miyau. Donhaka wani abu ya tokare a wuyansa. Madinah muguwa ce ta karshe ya sani in dai akan soyayyah ne, idan ta samu dama zata iya kisa, har lahira kuwa, don haka nisa da ita shi ya fi wa bawa kamarsa kwanciyar hankali.
Juyawa Dr. Sarham yayi cikin daure fuska kamar bai san ta ba, ya soma takawa don barin mud’am (restaurant) din gabadaya.
Madinah ta saki malalacin murmushinta, ta riga ta san halin kayanta bashi da jarumta in dai a kanta ne, tanada yaqinin bazata sha wuya ba wajen dawo da shi ruwa tsundum cikin soyayyah. Ba da sanin sa ba Madinah har sujjadah ta fadi ta yi a nan inda take zaune, (for the second phase) na rayuwarta ta sake haduwa da Sarham Shanono, a muhallin da ta fara haduwa da shi a can baya.
Ta tako cikin kasaitar ta har inda yake tsaye yana shirin barin wurin shan coffee din, ba tare da ko an gode yace ba, daga abinda aka biya masa. Madinah ta sha gaban sa, ta kashe shi da murmushin nan nata kamar na koren furen fulawa, da ya dade da daina gani, zuciyar sa kuma bata bar mararin ganin murmushin ba all those years, Madinah ta ce,
“ai in da alkawari zai zamanto cewa ko gaisuwar musulunci ce akwai a tsakanin mu Dr. Sarham, idan ta SO da KAUNA ta gushe ko tayi fading, a matsayin mu na dalibai duka, sannan ‘yan kasa daya kuma ‘yan aji guda, dana tabbatar abinda nazo yi shi ka zo yi, ba laifi bane don hanya ta hada mu mun tsaya mun yi gaisuwar musulunci”.
Wannan karon ma bai yi niyyar bata amsa ba yasa kai zai wuce abinsa, a ran sa yana fadin “Allah ya shiga tsakanina da ke Madinah!
Mumini na kwarai sau daya maciji yake saran sa a rami guda”. Amma sai Madinah bata yi fushi ba, ta sake shan gaban sa. Ta ce,
“Assalamu alaykum warahmatullah wa barakatuhu!”
Kamar yadda ta dade da sani, Sarham Abbas nada wani hali daga halaye masu kyau, wato baya iya maida gaisuwar musulunci a kwandon shara, ta hanyar kin amsata, wato duk inda ya ji ta sai ya amsa koda ba da shi ake ba, ba don komai ba sai don cika sunnar Manzo SAW.
To yau ma hakan ce ta faru kuma yanzun ma. Sarham ya kasa kin amsawa don cika umarnin addinin musulunci, sai ya ce kasa-kasa kamar yaci madaci,
“wa alaykumus salam warahmatullah wa barakatuhu”.
Daga wannan sai aka shiga kallon-kallo, koko in ce ‘kallon kuda’ kallon debe shakku ko debe tsammanin gizo ido ke yi, kallo ake babu ko kiftawa haka babu kakkautawa tsakanin SARHAM DA MADINAH. Suka yi wa juna kiriii da ido.
Kallon da ya dawo masa da duk abinda ya faru cikin shekarun soyayyar kurciyar su kan idon sa, koko ince, kan idon kowannen su, komai da ya gabata (in the past) ya zo yana gilmawa a idanun kowannen su, tamkar yadda sinasinai ke wulgawa a majigi, suna tariyo kan su, suka kuma shiga warware tsohon kullin dake zuciyar Sarham akan Madina, tamkar ana tariyo tsohon kaset na faifan bidiyo.
A hakikanin gaskiya Sarham na kullace da Madinah kullata mai yawa, wadda ta janyo ya maida kansa ba namiji ba, ta hanyar daina sha’awar soyayya da sha’anin mata gabadayansu.
Madinah tasa ya hada su itada sauran matan duniya yayi musu kudin goro da cewa dukkansu maciya amanar kauna ne, kuma basu san darajar soyayya ba, mata irin Madinah in ka bari ka fada komarsu zasu iya kashe ka har lahira akan soyayya.
Yana tuhumarta ne da rashin alkawari da cin amanar kaunar da suka yi wa juna.
Son data ke ikirarin tana yi masa yayi ittifakin ko kusa bai kai rabin nasa ba, shiyasa ta iya bari har aka raba su cikin matukar sauki haka, kamar kwace goriba a hannun kuturu.
Abu daya ya sani kuma yake da tabbacin sa; Madinah Attahiru, bata taba raina shi ba, wai don shekaru biyu ko uku kawai ya bata a haife, Madinah bata taba raina arzikin mahaifin sa ba, wai don bai tara dukiya kamar nata mahaifin ba, baya ga kasancewar sa malamin makaranta/malamin jami’a.
Yana son Madinah har gobe, domin ta hada duk wasu halaye na kwarai da nagarta da kyawun sura dake sawa a so mace, a yi mata So na musamman. Duk wasu ‘attributes’ da yake so a matar aurensa Madinah ce ta hadasu ita kadai ranta.
Ya ci buri mai yawa a kan Madinah Attahiru, haka ya sha wahala lokacin da ya rasa ta farat daya. Haduwar su ba zato a yanzu, karo na biyu cikin shekarun girmansu, a lokacin da suke da cikakken hankalin su bata nufin komai sai fami a kan gyambon da riga ya warke.
Kafin wannan lokacin sun yi alkawarirrika masu dimbin yawa shi da ita, kai har yawan adadin ‘ya’yan da suke burin haifa ra’ayin su ya zo daya, wato ba masu yawa ba, shi da Madinah kamar Lailah da Majnoun ne. Daga cikin manyan alkawuran su na can baya, har da na yin aure daga zarar sun kammala MBBS, koda basu samu ayyukan yi ba a Jeddah, sun ajiye a ransu zasu yi ko ayyukan philanthropy ne a private clinics na Jeddah don rufa asirin juna indai zasu rayu tare.
Rana daya Madinah bai san ya aka yi ba, bai san me ya faru ba Madinah ta yarda mahaifin ta ya ci zarafin sa, ya kuma canza mata makaranta, duk dai don ya raba su, ya rasa mai yasa Baban Madinah ya ki jinin sa ya kuma raina arzikin su shida iyayensa har haka, tunda daidai gwargwado iyayensa nada abin yin su, da rufin asirin su basa nema a hannun kowa, ko da yake ya taba gaya masa fuska da fuska;
“me na sama ya ci bare ya baiwa na kasa? Kuma yayi yarinta da auren ‘yarsa a lokacin” Shine kawai hujjarsa.
Babban laifin da Madinah ta yi masa shine, bayan an canza mata makarantar, bai kara ji daga gareta ba, Madinah bata kara waiwayarsa ba, bata kara neman sa ba, koda da gaisuwar zumunci ne. Ai yasan Madinah nada email adireshinsa, da adireshin sa na gidan wasika, da lambar talfon din gidan su, amma ko sau daya, bata taba tunanin gwada neman sa ba, wanda ke nufin ta datse duk wata alaqar soyayya da sanayya dake tsakanin su.
Koda ba don maganar alkawarin aurensu ba, ai ta nemi inda yake ta ji yana raye ko ya zarce ta dalilin kisan gillar soyayar da suka taru suka yi masa itada mahaifin ta, tunda dai ta kwana da sanin irin son da yake mata, ba irin wanda zai gushe farad daya bane.
Wannan shine babban laifin da Madina tayi masa da ba zai yafe shi ba wato kin neman sa ko sau daya cikin shekaru bakwai da rabuwarsu, tun bayan komawar ta Yamboa inda a can tayi nata consultancy din, tsayin shekaru biyar, da komawar sa shima zuwa gida Najeriya na dan wani lokaci, inda daga baya ya dawo shima yayi consultancy dinsa ya sake komawa gida.
Wanda ya yi shi ne da kyar da sudin ludayi shikadai a [KAU] a dalilin rashin Madinah tare da shi.
Saboda tunda suka fara MBBS suke tare, har zuwa karshen sa. Karatun dukkansa, da aikin gida (assignment) da halartar lacca duk tare suke yin komai. A lokutan jarrabawa kuwa duk zaka same su tare a library, sun dukufa basa komai sai fatan isa ga ‘goal’ din rayuwarsu. Don haka shekaru goma kenan ya kwashe a cikin hidimar dakon son Madinah Sorondinki, idan har lissafin sa daidai ne; yayi shekaru biyar tare da ita cikin fafutukar hada MBBS, shekaru biyar kuma cikin jinyar soyayyar ta, lokacin da yake consultancy, tun bai san so ba akan Madina ya koye shi, wato tun farkon tashen balagar sa da soyayyar Madinah ya budi idanu.
Wannan shine tarihin soyayyar su shi da Madinah wanda ya tuna a wannan ‘yan dakikan da suke kallon debe tsammani shi da ita.
**** **** ****
Da tunanin sa ya zo nan, sai ya dauke kai daga kallon kudar da suke yi wa juna, ya juya da zummar cigaba da tafiya ya bar ta a wurin, ba tare da ya kara tankawa ba.
Madinah bata yi fushi ba, ta hakurkurtar da ranta da cewa fushin fari ba nata bane, Allah na nufin su da wani al’aamri maigirma da ya sake hada su (at appropriate time), ta sake biyo bayan sa jiki babu karsashi, yana saka kafa tana mayas da tata duk inda ya cire tasa, cewa tayi cikin muryar dake raurawa.
“Sarham, yaya bayan rabo?”
Cikin dakiya da tsare gida yace “bayan rabo kuma? Sai tarin alkhairi” “Kamar baka gane ni ba?” Madina ta fada kamar zata fashe da kuka wannan karon, idanun ta na kallon kasa, sun kasa rike hawayen yanzu, suna cigaba da tafiya zuwa dakin karatu, hawaye na tsirgo mata. Sarham yace.
“Madinah kenan, ni kuwa na gane ki, ko ba Madinah Attahiru diyar masu Bankin Musulunci na Duniya bace? Idan na gane ki sai me hakan zai kare ni da shi, ni Sarham dan yaku-bayi?”
Madinah tana hawaye tace “zaka iya fadin komai a kaina ba tare da na ga laifin ka ba Sarhm, laifi kan laifi na san na yi maka amma ina da DALILI na.
Abu daya nake so ka gane yanzu, Daddyna daka sani a da can, to bashi bane yanzu. Wannan sabon Attahiru SoronDinki ne, wanda duniya ta biyar dashi, yanzu ya gane cewa rayuwar kanta da dan adam kansa komai mukami da mulkin sa, da dukiyar da yake tinkaho duka ba a bakin komai suke ba.
To cut it short, Daddyna ya dade yana neman ka ido rufe domin ya nemi afuwar ka, ya kuma baka damar da ya dade yana hana ka”.
Murmushin da Dr. Sarham Shanono yayi irin wanda yafi kama da a kira,
“na dade da baiwa wannan tatsuniyar baya” ne.
A fili kuma yace “Madinah Soron Dinki, takamaimai me kike so da ni yanzu a takaice, da yasa kike min wannan binbinin haka?”
Ai jin haka Madinah ta tabbatar yanzu kam Sarham ya gama da babin ta, yau ita Sarham ke cewa tana masa binbini! Wannan ba Sarham din data sani a baya bane halinsa duk ya canza, wancan jovial ne mai saukin kai da dadin sha’ani, ko dai wani ne mai tsananin kama da shi da irin sautin sa ta gamu da shi saboda yadda ta saka shi a ranta???
Sai kawai Madinah ta durkushe anan inda take tsaye, cikin korran grass carpet (ciyayi) ta saki kuka mai cin rai.
A can zamanin baya Sarham ba abinda ke daga masa hankali irin damuwar Madinah Attahiru, amma wallahi yanzu bai ji ko gezau ba wai an tsikari kakkausa, ya yi kuka har fiye da wannan da take yi yau akan rashin Madinah, da kuma wulakancin da mahaifin ta yayi masa ranar da yace “ba zai taba baiwa dan almajirin gwamnati (dan malamin makaranta) ‘yar sa ba”.
Ita nata kukan kuwa a yanzu ai na jin dadi ne, abinda bai sani ba, kukan Madina yau ya kunshi abubuwa masu dimbin yawa, har da wadanda tunanin sa da tsinkayen sa bai bashi ba.
Bata taba daina son sa ba, a duka wadannan shekarun daidai da rana daya, ta yanke alaqar su ne domin ta samu damar yin biyayya ga mahaifin ta, wanda ba abinda bai yi mata a duniya ba, ya kuma fifita soyayyar ta akan ta ‘yan uwanta maza bakidaya kasancewar ita kenan masa diya mace, kuma auta a cikin ‘yan maza bakwai. Wannan shine dalilin nata.
Sarham bai tsaya Madinah ta gama kukan bay a cika bujensa da iska ya bar wurin, sai dagowa tayi bayan ta share hawaye ta neme shi a filin wajen ta rasa.
A lokacin ta cigaba da tuno rayuwarta ta baya tare da Sarham, abinda ya faru shekaru bakwai da suka gabata, ta tuno asalin ta, haduwar su, lokutan su tare a campus, da abubuwan da suka faru da ita bayan rabuwar tasu…….
**** ***** ****
WAIWAYE ADON TAFIYA! (2)
DR. MADINAH ATTAHIRU
A
salin mahaifin ta Bakano ne dan asalin Soron Dinki, Soron Dinki wata karamar unguwa ce mai tsohon tarihi a jihar Kano, wadda ta haifi fitattun malamai da alkalai a tarihin jihar. Tana nan dab da gidan Sarki (Emir’s Palace).
Mahaifin Attahiru wato Kakan su Madina tsohon Alkalin Alkalai ne na jihar Kano kuma fitaccen mutum akan sha’anin shari’ah a Kano. Tun a tsakiyar shekarun 80’s Attahiru Habibu Sorondinki ya tafi Jeddah kan wani kwas na aikin Banki, tare da matar sa Hajjah Ramlah da manyan ‘ya’yan sa maza uku a lokacin, Abubakar da Omar, da Osman inda daga wancan lokacin ya fara aiki da wani tsohon bankin kasar ta Saudi-Arabia.
Da tafiya tayi tafiya, zamani na garawa da shi a harkar aikin banki a can, har zuwa lokacin da aka bude ISDB wato (Islamic Development Bank) Allah kuma ya zabe shi ya kai shi ISDB a babbar ‘headquater’ din su dake birnin Jeddah. Ya rike kananan mukamai da dama a cikin ta, kafin ya iso wannan matakin na yanzu. Domin kuwa a halin yanzu mahaifin na Madinah Alhaji Dr. Attahiru Soron Dinki yana rike da matsayin (Chief Financial Officer) na ISDB. Alh. Attahiru na auren Hajjah Ramlah, wadda ta kasance ‘cousin’ a gare shi, ta cika masa gida da kyawawan ‘ya’ya maza har su hudu, Abubakar, Omar, Osman da Aliyu, a Kano ta haifi manyan su uku, wato Abubakar, Omar da Osman. Da suka zo Jeddah ba jimawa ta haifi Madinah da Aliyu anan.
Akwai ratar haihuwa sosai tsakaninta da Osman kafin su samu haihuwar auta “Madinah”. Daga Abubakar har Umar har Aliyu da Usman ma’aikatan bankuna ne a kasar Saudi-Arabia, saboda mahaifin su dake da wuka da nama a harkar aikin banki.
An haifi Madinah ne a garin Madinatul-Munawwarah lokacin sun je aikin omrah duk gidan, shi yasa Baban ta ya kira ta da suna Madinah.
Madinah ta ga gata tun daga haihuwar ta har girman ta, Madinah bata taba sanin wahala ko babu a rayuwar ta ba, ta tashi a gida na ilmi da tarin dukiya, wanda ya sa koda ta shiga jami’a maza ke rububin ta, da yawa ko don su rabi alfarmar ISDB, da yawa kuma saboda kyawun ta ne.
Amma wani ikon Allah babu wanda tasu ta zo daya irin coursemate dinta Sarham Abbas Shanono, wani siririn sardidin yaro, dan ajinsu, wanda ta fahimci yafi kowa a ajin su kokari, kamun kai da kula da abinda ya kawo shi, shima kuma ya fahimci Madinah Attahiru tafi duk matan ajin su kokari, ga aji ga kasaita kamar wadda ta hada jini da sarauta, amma shi bata yi masa ko daya sai ma wani ‘special respect’ da take bashi, sai suka hade daga haka, suka zama abokan karatun juna, daga abotar karatu da karawa juna sani abin nasu ya fara, kafin ba da jimawa ba ya rikide zuwa zazzafar soyayyah wadda ta isa a bada labarin ta a ko’ina, amma irin soyayyar nan ta sa’annin juna. Wadda bata fiya ‘actualizing’ ba. Domin kuwa shekaru uku kacal Sarham ya baiwa Madinah Attahiru.
Duk da kasancewar Madinah irin mutanen nan da basa so ka shiga harkarsu, masu halin da kai tsaye za’a ce na nasara ne kamar ba tashin Saudi Arabia ba, amma duk da wannan hali nata bata da wulakanci da raina mutane. Personality dinta kawai za’a ce na nasara ne (musulma mai halin nasara), tanada wani zazzafan hali na kada ka sake ka shiga harkar ta, itama kuma bata shiga harkar kowa, saboda mugun jan ajin ta, ta kasance mace ‘yar I don’t care attitude.
A hali iri na Madinah ko kai waye wajen isa, ko wane irin laifi kayi mata, ko wane irin aibu kake da shi, Madinah bazata zauna tana gulmar ka da wani ba, tafi karfin haka, saboda she is frank, bata iya boye me take