Showing 9001 words to 12000 words out of 45645 words

Chapter 4 - Hauwa Kulu Book 2 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

129

ji akan mutum, zata tare ka ne gaba da gaba ta gaya maka, da dai ta zauna tana zunden ka da wani.
Wato dai a takaice Madinah bata iya munafurci ba, sannan bata so a yi mata.
Wadannan halaye nata sun taimaka kwarai wajen ribato zuciyar kyakkyawan Bakanon matashin Sarham Shanono a kan ta, babban jigon son da ya samu kan sa da yi mata shine yadda gatan data ke da shi bai hanata tsayawa tsayin daka wajen yin karatun da zai amfani al’umma ba.
Sarham Abbas da Madinah Attahiru duk abokanan karatun su na MBBS sun san su tare, ko’ina tare suke zuwa, soyayyarsu mai tsafta, mai ban sha’awa ta ‘yan bokon da, ba irin ta wannan gurbataccen zamanin ba, Madinah kullum kawo ta ake a kuma zo a dauketa a motar gidan su, shikuwa a nan kusa da makaranta ya kama hayar gida mai daki biyu (flat).
Sun tsayar cewa da zarar sun yi bikin kammala karatu zasu yi aure, Madinah ta yarda zata bi Sarham Najeriya ta zauna cikin iyayen sa da kannen sa duk da cewa itada kasar Kano sai da ziyarar dangin su kawai su kan shigo ta, ita dinma sai suyi shekara hudu-biyar basu zo ba.
A wani dan tsakani da ya kasance sun kusa zana jarrabawar karshe a MBBS Madina ta baiwa Sarham iznin fara zuwa zance gidan su, ba don komai ba sai don iyayenta su san da zaman sa, kasancewar soyayyar tasu iya makaranta suke yin ta ba wanda ya san shi a gidan su har zuwa lokacin banda Yayan ta Osman dake zuwa kawota da daukan ta.
Zuwa na farko, na biyu dana uku Alhaji Attahiru ya fahimci akwai mai zuwa wajen Madinahr sa, Hajjah Ramlah ma ta gaya masa wani ya fito neman auren Madinah amma bata san ko waye ba, saidai ga dukkan alamu Madinah tana yi da shi, ko daga girke-girken da take faman yi masa in zai zo.
Daddy ya umarci Madinah data turo masa yaron dake zuwa wajen ta yana so zai yi magana ta gemu da shi, ba tare da tunanin komai ba a washegari Madinah ta gabatar da Sarham a tankareren falon mahaifin ta, daga nan ta basu wuri don su gana.
Sarham yayi wani kuskure zai ce ko katobara, koda yake a wurin sa is normal, wato yawo da farar jallabiyya ta larabawa a garin Jeddah, maimakon da zai je gun siriki yayi shiga ta cika ido da kima sai yasa jallabiyyar sa abinsa wadda taji wanki da guga da turaren sa na Oud Abyad. Kallo na farko da Alhaji Attahiru yayi masa yaga yarintar sa da rashin cika ido, sannan kuma babu tantama dan talakawa ne ko daga sittirar jikinsa amma duk da haka bai yanke hukunci daga abinda ya ganar da kansa ba, sai da ya tambayi Sarham.
“Yaro kai dan ina ne?”
“Kano”
“wane gari a Kano?”
“Shanono”
“Waye mahaifin ka?”
“Prof. Abbas Shanono”
“daga jin Farfesa malamin Jami’a ne kenan?”
“Eh!”
“to kai kuma meye taka sana’ar?”
“dalibi ne ni”
“Dalibi dan Farfesa, ilmi na dukan ilmi, amma dame ka shirya rike min ‘ya ta yaro da kai haka? Ko bata fada maka daga gidan data fito ba?”
Sarham ya kasa hadiyar miyau, don bai zaci wadannan kalaman marasa kan gado daga babban mutum mai ilmi kamar sa ba, Daddyn Madinah ya cigaba da cewa “yaran zamani in zaku yi abu sam sam ba kwa tunani, yo me na sama ya ci bare ya baiwa na kasa?
Yaushe zan ajiye ‘ya ta zaman jiran girman ka da yin arzikin ka kafin inyi mata aure?
Ai kawai yaro kaje ka nemi daidai kai diyar malaman makaranta”.
Sarham hatta jijiyoyin kansa saida suka mimmike, suka fito rada-rada, tun kafin ya tashi a wajen ya gayawa ran sa ya hakura da Madinah ko itace autar mata, don mai taba Abban sa ya zauna lafiya a hannun sa sai dukan ruwan sama. Shima don ba zai iya rike shi daga taba jikinsa bane.
Duk da haka wannan tsohon baturen zai ce ko tsohon nasara ya ci arzikin Madinah-Munauwarah. Amma da ba haka ba?! Da yayi masa raddi daidai da nasa. Ya girgiza kai ya mike. A kullum Madinah na cin alfarmomin sunan ta a wurin sa, wato, yana son garin Madinah sosai, duk sati biyu yake ziyara Masjid Nabawy daga Jeddah, don haka ko cikin hira yana gaya mata cewa tana cin albarkacin sunan ta na Madinah garin Manzo, garin da ya zamewa Ma’aiki (SAW) mafaka (refege) kuma wajen yin hijira daga inda yayi masa kunci, don haka sau tari ya kan ce da ita, ko sunyi aure ta bata masa rai komai girman laifin zai iya yafe mata shi saboda sunanta, zata cigaba da cin albarkar city of Madinah, za kuma ta cigaba da samun wannan alfarmar har gobe a wurin sa.
Don haka bai ce komai ba baya ga godiya ga mahaifin Madinah da barin gidan su ba tareda ya tsaya Madinah ta ga yanayin sa na lokacin ba.
Shi uban da kansa ya gaya mata ya sallami wannan yaron, in bata da hankali shi da hankalin sa, ba daga turu aka fito da shi ba, kuma ta sani daga yau ta bar King Abdul Azeez University kenan, don ya fahimci irin ‘ya’yan talakawan nan ne masu hurewa ‘ya’yan manya kunne da ‘I love you’, su dau advantage na iyayen su don su samu abin yi mai maiko, in sun kama kasa su auro daidai su, ‘ya’yansu su koma na ladan noma.
Madinah couldn’t control her tears, ta bi bayan Sarham da gudu amma bata cimmasa ba. A washegari kuma Babanta bai barta ta koma [KAU] ba, yasa Abubakar ya karba mata ‘transfer’ zuwa Yamboa ya kuma je ya kaita da kan sa, yace in ta kara neman wannan yaron ko a waya kota wata kafar sadarwa kowacce iri ce zai saba mata ko ya bar kasar bakidaya da ita.
Madinah na matukar son birnin Jeddah don anan aka haife ta, amma haka Baban ta ya raba ta da shi saboda Sarham zuwa Yamboa.
Madinah na matukar son Sarham, so irin wanda bazai misaltu ba, amma haka ta hakura da shi saboda ta yiwa mahaifin ta biyayyah.
Madinah na matukar son mahaifin ta shiyasa ta zabi farin cikin sa a kan nata, wato ta zabe shi akan soyayyar dake zuciyar ta, ta kuma bi umarnin sa.
Wannan kadai ya nuna Madinah mai biyayyar iyaye ce ta kuma ci ribar biyayyar tun a lokacin, domin duk da zuciyar ta tafi dare duhu, amma haka mahaifin ta yayi ta saka mata albarka, yana ankarar da ita illar auren ‘ya’yan talakawa gasu yara masu gata kuma ‘ya’yan manya kamar ta, yace basu da alkawari ‘yan taking advantage ne kuma basa juyuwa ta sauki ga matan su, taurin kansu kadai dafadin rai ga matayensu sai ta gwammace kida da karatu, sannan basa taba zama da mata daya.
Duk Madinah tayi biyayyah ko a fuska bata taba nunawa mahaifin ta har lokacin Sarham yana ranta ba. ta kuma san duk abinda ya fada akan Sarham ba haka bane, Sarham akasin duka wadannan expectations dinne.
Sai ta tattara komai ta fauwalawa Allah ta maida hankali ga fuskantar karatunta a jami’ar Yamboa, ta manta da komai, a shekara daya da Sarham ya gama nasa karatun itama a shekarar ta fita daga Yamboa University, ta fita da flying colours a specialization nata, ta zama cikakkiyar likitar fidar ido (ophthalmic surgeon) mai lasisin yin aiki a kasar Saudi-Arabia.
Shima Sarham ya fiddo nasa kwalin daga (KAU), ba tare da sanin me kowannen su yake ciki ba. Daga nan ya tattara ya koma gida. Inda ya kama aiki a karkashin gwamnatin jiharsu.
A lokacin ne AVM Adamu Alkali ya fito neman auren ta.
Ba kuma ta kanta ya bi ba, ya tafi ne kai tsaye ta kan mahaifinta, shikuma a sanin irin biyayyar da Madinah keda ita bai bata lokaci wajen neman yardarta ba, saboda wannan shine daidai da ra’ayin sa, irin mijin da yake mata fata yake mata addu’a, gashi Allah ya bata a lokacin da ya dace tayi aure, miji wanda bazai yi kaico da aura masa ita ba, wato na saman da ya ci ya hantse yake watsowa na kasan sa, dama duk wadanda ke jikin sa koda sun kasance suma masu wadatar ne.
Don haka Daddy bai ja lokaci mai yawa ba wajen sanya auren Madina da AVM (Air Vice Marshall A. Alkali), wanda shima dan Kano ne gaba da baya, amma mazaunin jihar Lagos, inda a can yake aikin sojan saman sa.
**** ***** ****

L
okacin da mahaifin ta yayi mata bushara da hakan, wato ya gaya mata da bakinsa ya saka auren ta da AVM Alkali, Madinah ko tada kai bata yi ba balle ta ce a’ah, saidai bayan maganar da kwana biyu ta kwanta zazzabi mai zafi, wanda har ya kai ta da kwanciya a asibiti.
AVM yayi amfani da wannan damar ya zo duba Madinah, ranar ne ma ta fara ganin sa a gadon asibiti, ba wani kallon kurilla tayi masa ba amma ta fahimci babba ne sosai, ba za dai tace sa’an baban ta bane amma hakika ya manyanta don zai girmi babban Yayansu wato Yaya Abubakar, babu mamaki ya aje diyar data kusa giramanta.
Madinah ta dauke kai daga duban sa, yayi mata sannu da jiki ta amsa fuska ba yabo ba fallasa, babu wata fuska da zai neme ta da zance, dole ya gabatar da kan sa ya tafi. A washegari manya suka tsayar da ranar daurin aure.
Sadakin Madinah kawai da aka kawo dankunne ne da sarka na ‘Emerald’ wato koren yaqutu, sannan AVM ya yi alkawarin ‘launching’ sabon asibitin ido nata na kanta da zai bude mata a jihar Lagos inda zata zauna da zarar ta sauka a kasar Najeriya.
Iyaye nata shirye-shirye ta kowanne bangare ka’in da na’in, haka ta fannin matar AVM wato Hajiya Juwaira itama tana ta shirin zuwan amarya don ta saba da shiga ta fitar su shiyasa bata ko damuwa idan yace zai kara aure. Amaryar kuwa a lokacin duk da shekarun nan masu dama da suka gabata zuciyar ta na ga Sarham.
Tarihi ba zai manta da soyayyar su ba, amma babu tantama da zuciya daya yau ta hakura da Sarham da aka damka sadakinta, ta yarda zata auri zabin mahaifin ta.
Aka daura auren DR. MADINAH ATTAHIRU da AVM A. Alkali a wata ranar juma’ah, a masallacin Haraam, bayan saukowa sallar Juma’ah, iyaye da dangi aka shiga shirin biki na garari da kasaita kafin lokacin da za’a mika amarya nanjeriya.
Daddy yace ma AVM shi da kan sa yazo ya tafi da amaryar sa bayan kammala biki kenan, bai yarda da mata su rakata zuwa kai amarya Lagos ba irin yadda ake yi a al’adar Kanawa.
Air Vice Marshall Adamu Alkali Sambo, ya biyo jirgin su na sojin sama zuwa birnin Jeddah, irin jirgin su na helicopter, jirgin ya fadi a wani tsibiri/tsauni. A cewar wasu kuma ‘yan uwan sa sojojin sama ne suka harbo jirgin nashi bisa wata matsalar aiki da suke ciki da shi da su kadai ta shafa kuma su suka santa.
Koma dai yaya ne an tabbatar babu wanda ya fita da rai a wannan hadarin jirgin saman daga shi har staff dinsa guda hudu da matukin jirgin na biyar.
**** **** ****

“Innalillahi wa’inna ilaihirajioun…”.
In ji Daddy, kafin ya saki kan wayar a kasa ya durkushe akan kafafun sa, Hajjah Ramlah na tambayar ba’asi amma ya kasa gaya mata mijin Madinah yayi hadarin jirgi akan hanyarsa ta zuwa daukan ta.
Madinah wadda aka gama shiryawa cikin ‘SARI’ na ainahin matan indiyawa, hatta bular nan ta dankunne a hanci an yi mata da karfen zinare, ta zama kamar ba’indiyar gaske, dama tana da irin suffar su, isowar AVM kawai ake jira su daga Najeriya, sai ga Baban ta ya shigo dakin afujajan, yace mata “Madinah kiyi tawakkali”, Dady ya nisa kafin ya sake cewa “Ya ke ‘ya ta mai albarka, Allah ya karbi AVM”.

Albarkar da har gobe ta tabbatar tana bibiyar ta, domin watanni goma bayan rasuwar AVM A. Alkali, ba tare da ta yi masa ko gani na uku ba, mahaifin nata da kansa ya kira ta, har zuwa lokacin bai gama fita daga ‘shock’ da firgicin mutuwar AVM ba, wanda har ciwo ya kwantar da shi, ya kuma maida shi salihin bawa akan yadda ya dauki duniya a baya.
Ita kuwa Madina duk da taji mutuwar, tofa bata kara saka wani tunani na daban akan rasuwar sa ba, bayan na tunanin zuwa karo zurfin ilmin ta a KAU, don har zuwa lokacin ruhin ta bai bar makarantar nan tasu ta baya ba.
A yau da Daddy ya kirata dakin sa domin su yi magana ‘heart to heart’ irin ta Da da mahaifi shi da ita, ta zauna tankwashe da kafafu a gaban sa.
Ya fara da neman gafarar ta, kafin yace “na so in yi abu na son zuciya ta, gashi duk yadda naso faruwar sa Allah bai kaddara gidan ki bane ba.
Gashi ya yanke hukuncin da ya san yafi daidai da rayuwarki.
Na sani Madina biyayya kawai kike yi min, amma zuciyar ki naga wancan yaron, don haka yau bisa umarnina, na amince ki nemo wannan yaron Sarham a duk inda yake, in har yanzu yanada niyyar auren ki ya zo zan bashi. Bana neman ko kwandalar sa”.
Madinah ta girgiza kai ta ce “Daddy! Ai ni tuni na hakura da Sarham, na dade da mantawa da shi, kai ma ina rokonka ka manta da shi, ka sake yi min duk mijin da kaga dama, da yardar Ubangiji wannan karon ma bazan baka kunya ba”.
Shi kuma ya dage Sarham zata nemo, bas hi ba kara yi mata auren dole, auren soyayya yake son tayi wannan karon, da wanda zuciyarta ta aminta da shi, ba auren biyayyar sa ba.
Madina ta yi masa rantsuwa kan bata ma san inda Sarham yake ba a yanzu, don haka tana rokonsa alfarmar ya barta ta koma karo karatu a King Abdulazeez University.
Shikuma babu ja’inja ya lamunce mata, yana mai saka mata albarka.
Mafarin dawowarta KAU kenan, sai gashi ko sati bata yi ba ta hange shi a zaune a mashayar coffee, yana jira a hada a miko masa. Madinah ta mike ta je ta biya kudin coffee din tun kafin ya gama sha ya tashi.

“SARHAM!!!”

Madinah ta fada a hankali, bayan gushewar shekaru bakwai yau ta sake sanyashi a idanun ta, duk da canzawar halittar sa bazata taba kasa gane shi ba.
Wannan sirantakar da rashin kumarin, yanzu duk sun hade da tsoka da muscles, ta bada surar kakkarfan matashi lafiyayye mai wadatar jini a jika.
Wanda zuwa yanzu zamu iya cewa ya gama samun rayuwa daidai da burin sa, hankalin sa a kwance yake, saboda tsarin rayuwar sa ta masu tsantseni da gudun duniya ce tun sanin data yi masa, ba wai irin ta tara yaki halal yaki haram ba, sun tsaya ga iya gumin su, sun tsaya ga cin halal da moriyar ilmin su kadai.
Yayi jiki daidai misali wanda ya karawa tsayin nasa haiba, ya tashi daga siririn yaron nan zuwa (handsome man), son kowa, kin wadda ta san ba zata samu ba.
Madinah (couldn’t control her tears) wadanda (emotion na radadin soyayya) yayi sanadin zubowar su, a lokacin da zai bar wurin ne ta bi bayanshi shine ya yi mata wannan yarfawar. Shin meye laifin ta a duka wannan tsarin da Ubangiji ya yiwa rayuwar ta? Me tayi ma Sarham da yayi zafin da gaisuwar musulunci ma sai da kyar zai amsata tsakaninsu?
Ba mai bata wannan amsar sai SARHAM din. Ta sani bai dace ta bi shi har gidan sa ba, kai baima dace ba mace kamar ta ta dinga bin namiji komai tinkahon sa yana yarfata irin haka, balle ita Madinah Attahiru, da bayan aji har ajujuwa gare ta. Amma haka ta take PRIDE din nata, da kafarta ta taka zuwa gidan da ta san acan yake da zama, bata da tabbacin har yanzu acan din yake, ko kuma ya canza gida, amma dai tace bari ta fara duba can din ko zata dace. Ubangiji da kan sa yace “SULHU ALKHAIRI NE!”

To gata ta zo neman sulhun abin kaunar ta yau da kafafunta, kamar yadda tasan tana cin alfarmar sunan ta kullum a wurin sa, haka yau ma take da wannan kyakkyawan fatan, tana da yaqinin wannan karon ma zata ci wannan alfarmar daga gareshi, wadda tafi ta koyaushe girma a wurin sa, wato ya sauke fushinsa ya tsaya ya saurareta ko na minti biyu ne albarkacin sunanta da yake girmamawa na MADINATUL MUNAWWARAH… Madinah garin Manzo, Madinah mafaka ga dukkan musulmi, duk da tabbas ta san an bata masa, kuma laifi kan laifi ta san ta yi masa. Ko tace sun taru sun yi masa itada Daddy dinta.
Ilai kuwa tana tura karamin gate din ta hange shi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login