Showing 36001 words to 39000 words out of 45645 words

Chapter 13 - Hauwa Kulu Book 2 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

139

mu ta farko kenan ba”. Hauwa tace itama likitar ido ce?” Dr. Sarham Yayi dariya yace “exactly! Amma ya akayi kika sani?”.
Tace “na dade da sanin likitoci basa aure sai da liktoci ‘yan uwan su, watakila don kada a shafa musu cuta?” Sarham me zai yi ba dariya ba yace “wato shi likita bashi da cuta a jikinsa Maijidda?” Tace “da sauki dai” anan ma ta kara bashi dariya sosai, yace “ni kuwa da har na yi miki takwara, na dauka kema likitar zaki so zama?” Kafin Hauwa ta kara magana sai Malam Isa ya fito yana musu sallama zai wuce gida, tare da Salele.
Salele yaga Sarham, nan da nan ya shaida shi, ya hau yage baki don bai manta shi ba da tarin alherin da ya dinga yi masa don ya dinga raka Hauwa Makaranta.
Suka gaisa da Salele suka yi sallama da su suka wuce, shi da Hauwa suka koma wajen Inna. Hauwa na tambayar sa cikin mamaki.
“Da gaske likita ka yi min takwara da ‘yar ka?”
Zancen a kan kunnen Inna, ta dago tana kallon shi da mamaki itama, tace.
“Sarhamu kayi aure ne banida labari?”
Sarham ya sunkuyar da kai yana dan murmushi yace “eh Inna, har an samu karuwar Hauwa’u, HAUWA-KULU!”. Ya dauko wayar sa daga aljihun sa ya nunawa Inna hoton Waheedah cikin pink shawul daya dauketa dazu. A takaice ya basu labarin yin auren sa da Dr. Madinah bayan ya kammala karatun da ya kai shi Jeddah, da irin neman da yayi musu kamar ya zautu bayan dawowar sa.
A ranar ya jima tare da su suna ta labarin rayuwar su a kurna, rijiyar lemo da kuma unguwa uku, da ta karatun Hauwa da aka samu kammalawa da kyar, da sudin ludayi, ta gaya masa Hauwa ta fiddo da kyakykyawan sakamako sosai, wanda ba kokarin kowa bane nasa ne, madallah da shi, madallah da haihuwar ’ya’ya irin sa, masu zamewa al’umma fitilar rayuwa kuma bango abin jingina, madallah da tarbiyyar iyaye irin nasa, madallah da shigowarsa cikin rayuwar su”.
Sarham (feeling overwhelmed with joy and happiness) saboda ya sha addu’a yau a bakin Inna, ‘yar sa Hauwa ma ta sha addu’a, tace yadda ya tsayawa Hauwa-Kulu wadda a yanzu za’a kira maariniya miskiniya ta samu ilmi daidai gwargwado duk da makantar ido, Allah ya tsayawa tashi Hauwar ko bayan ransa, yasa tayi ilmin da zata zamo mai amfani ga al’ummar duniya.
Ita da kan ta Inna data nisa, taji yadda lafiya ta wadace ta, bata san sanda ta ce ta tuba tabi Allah ta bi asibiti ba! Daga yau ta daina kin asibiti tunda gashi ciwon shekara da shekaru ya tafi cikin sati biyu. Ta kara da cewa Sarham “ashe abin naku dace ne!”.
Sai bayan kwana uku da yin haka aka sallami Inna, Sarham ya zo da mota ya dauke su zuwa gidan su na unguwa uku yace “Inna koda abinda zaku dauka a gidan ku dauka, ku fito ina jiran ku” Inna tace “ai nan ne gidan mu likita, yanzu anan muke zaune tun da jimawa” ya ce “na sani Inna, zaku raka ni unguwa ne bazamu jima ba, amma dai in har kin yarda da ni, to ki kwaso komai naku”.
Inna ta hau kwasar kayan tana kaiwa boot din motar Sarham tana fadin “yarda da musulmi irin ka wajibi ne!”. Haka Hauwa ma, ta dauki kayan ta tsaf, suka kama hanya, Hauwa na gidan gaba Inna na baya. Sarham na tuki cikin nutsuwa da kwarewa, bai tsaya a ko’ina dasu ba, sai a kofar gidan su, gidansu na BADALAR Kofar Na’isa, dama sun riga sun shirya gidan dai dai gwargwado da taimakon Malam Isa da Salele. An zuba komai na amfani mai saukin kudi.
Inna tunda taga an doso kofar Na’isa ta soma hawayen tuna baya, kirjinta ya hau yin sama da kasa, ita ta dauka zai kaita ta gaisa dasu Maikosai ne.
Amma sai ta ga anyi fakin a kofar wani sabon gida a bayan Badala, in har bata yi kuskure ba, kuma idan har ba idon ta ke mata gizo ba nan din lungun su ne kuma unguwar su, da ko daga makanta irin ta Hauwa ta warke itama zata gane su, tunda ga gidan Malam Isa nan ba abinda ya canza shi.
Sai ta kalli Sarham a gigice, bayan ya kashe motar a kofar gidan. Sai a lokacin yayi musu bayani cewa gidan su ne ya karba musu.
“Ka karba mana kamar yaya?” Inji Hauwa, (sounding extremely puzzled). Inna kuma tace “ko dai ka gina mana?” Muryar Inna ta tambaye shi cikin kuka, don dai a kan idon ta taga lokacin da aka rushe gidan nasu wato gidan Malam Bilyaminu.
Sarham yace “Allah ne ya nufa gidanki ya dawo gare ki Inna, ni kawai na taimaka ne, kuma kiyi hakuri zan yi wani shishshigi, a gaskiya zan yi karar kanin Baban Hauwa akan abinda yayi”.
Inna ta fara kukan farin ciki da dariya a tare, ta ce “Dan nan me zan ce maka? Wace irin addu’a ya kamata in yi maka? Na rasa kalma a bakina da zata gode min kai.
Amma ka bar maganar Zakari, ni kam me zai sake hada hanyata da Zakari? Na roke ka ka rabu da shi Allah na kaiwa karar sa kuma na tabbata zai saka mini. Na bar shi da fitowar rana da faduwar ta”.
Ta share hawaye da habar mayafinta ta sake cewa. “Dan nan me zan ce maka?” A karshe Inna ta fashe da kuka tana ce da Hauwa “gidan mu ne Hauwa-Kulu! Sarhamu ya kwato mana da karfin mulkin Allah”.
Hauwa wani irin shock ta shiga na wucin gadi bayan fahimtar hakikanin halin da ake ciki. A yau ma dakacen nan ta kara yi na shekara da shekaru, mai fatan “INAMA TA GA FUSKAR LIKITA SARHAM!”
Suka karasa cikin gidan Inna rike da hannun Hauwa shikuma ya dauko bakko kayan su ya kai su har dakin da ya zama na Inna, an saka katifa a kasan kafet dirkekiya an shimfide ta da sabon zanin gado. A gefe ga kwabar saka kaya an yi mata. Haka dakin Hauwa ma amma ita a daki aka yi mata toilet don kada ta sha wahalar fitowa tsakar gida. Ga safayan daki da ba kowa yace na Baban Hauwa ne duk ranar da Allah ya dawo musu da shi. Sai kamshin sabon fenti da suminti gidan yake yi gwanin dadi.
Dakuna uku ne aka yi musu kamar da, kitchen kuwa da toilets na zamani aka yi masu masu tangaran (tiles) da Inna tayi ta shafawa da hannun ta a gaban Sarham tana shi masa albarka.
Hauwa duk jikin ta yayi sanyi musamman in ta tuna yadda ta ke share Sarham a baya, da kullacin wai ya makanta ta, Sarham is beyond her imagination a kaunar fisabilillah da yake yi musu.
Aka kai Hauwa nata dakin aka nuna mata direction na sallah dana zuwa toilet da madannin flushing. Ga dan karamin firji a gefen katifar ta (bed side fridge) Sarham ya ajiye mata don ya san ta da son shan abu mai sanyi tun baya, kai yau Inna da Hauwa farin cikin ya fi gaban ayi masa kuka ko dariya sai dai kawai ayi kurum, kamar yadda Hauwa tayi kurum!
Bayan sun gama zaga gidan sun zauna suna hira shi da Inna. Ya ce “wai ta yaya ma aka yi takardun gidan suka je hanun Zakari? Bayan kowa ya shaida ya sayarwa da malam Bilyaminu gidan kamar yadda Malam Isa ya bashi labari?”
Inna ta ce “umh, ai in kana neman hatsabibi ka samu Zakari ka gode Allah, maiyuwuwa yana da na kwarai dinne ya bawa Malam na jabu, ko kuma yasa an yi masa na jabu, oho, tunda har gobe na gonar su Baban Hauwa ya gayamin suna hannun sa, gab da batan Baban Hauwa, yace min sai ya karbi hakkin sa gun dan uwansa Zakari, wanda yake boyewa don a tunanin sa ya dauka Malam bai san da su ba.
Ina nufin gonar mahaifin su ta Panshekara wadda girman ta ya kai na naira miliyan daya”.
Sarham ya shiga mamaki mai yawa, ashe shiyasa Baban sa baya son sake aure? Kullum sai yace masa yana tsoron rarrabuwar kan su ne, shiyasa bai yi musu ‘yan uba ba.
Sun dade suna zantawa kamar Da da uwar sa, Hauwa kuwa tunda ta shige daki ta kwanta a sabuwar katifa bata kara fitowa ba don daga baya ma wani ni’imtaccen barci ne yayi awon gaba da ita, irin wanda rabon ta da shi tunda Inna ta fara kwanciya ciwo.
Da ya zo tafiya ne jin ta shiru ya dan leka dakinta, nan ya ganta tayi dai-dai tana kwasar barci da nutsuwa da kwanciyar hankali, numfashin ta yana hawa yana sauka freely, ashe tafi kyau in tana barci irin mutanen da ake kira sleeping beauty. Ya dan kalleta na ‘yan sakanni yana jin ta kamar Sumayyah a ran sa, ya kudurce a zuciyar sa zai tsayawa rayuwar ta, zai ingantata, zai mata abinda idan Sumayyah ce nakasar idanu ta sameta zai tsaya ya yi mata.
Daga nan gidan su ya koma, a falo ya tadda iyayen sa, kallo daya zaka yi wa Dr. Sarham yanzu ka tabbatar yana cikin nutsuwa da kwanciyar hankali ba kamar watannin baya ba, gashi Madinah ta cika masa ciki da abinci mai dadi, so bai waiwayi abincin sa dake bisa tebir ba ya zauna gun Abba Prof. amma ya killace bakin sa baiyi zancen su Hauwa ba, don ya lura bat un yau ba Abban (is not interested) akan zancen su, musamman da ya ga ya dauki al’amarin su da muhimmancin da yake neman wuce kima, kuma ya tambayeshi meye alaqar su ta hakika ya tsaya yi masa kame-kame. Tun daga lokacin yace,
“to in babu wata kebantacciyar alaqa da musuluci ya yarda da ita, to ya cire damuwar rashin ganin su daga ran sa, ya bar su a hannun Ubangijin da ya halicce su, tunda uban su ma da ya bar su ai basu kasa rayuwa ba.
Don haka baima kowa zancen ya ga su Hauwa ba, bai sani ba tuni Mai Shari’ah wato Barrister (Mama) ta dade da ramfo shi.
Kafin kwana uku duk makwabta sun san da dawowar Hauwa da Innar ta, aka yi ta shigowa ana ma Inna barka da arziki, da dawowar ta gidan ta, ana hirar yaushe gamo, aka yi ta tuna baya ana tattaunawa kan girman yara na yanzu, musamman ‘ya’ya mata da ba wuya sun girma, dubi dai yadda Hauwa ta gandame, ana tattaunawa a kai, kusan duk jama’ar Badalar Kofar Na’isa sun san Inna da abinda Zakari yayi mata saboda kyakkyawar mu’amalar ta da kowa, sannan yanzu sabon gidan nasu ya fito da gidan sosai. Har an sawa gidan suna sabon gida. A yanzu sai ya zamana babu gida mai zubin zamani da kuma kyawun nasu a bayan Badalar ta Kofar Na'isa.
Washegari da suka wayi gari a kwana na uku da tarewar su. Inna ta ce da Hauwa zata shiga gidan Malam Isa su gaisa da iyalinsa, tace saboda ta ga kowa ya shigo mata murna banda Maikosai. Hauwa tace “toh Inna kada ki dade” tace “kada ki damu bazan jima ba”, ta fita.
Tayi sallama gidan Malam Isa, Maikosai, wadda sunanta na ainahi Talatu, ta gama suyar kosan safe ta sayar, tana wanke kayan suyar ta a gindin rijiya ta amsa sallamar Inna, sannan ta juyo don ganin mai shigowa sai ta ga Innar Hauwa, nan da nan ta yi fuska ta juya ta cigaba da abinda take yi ta barta anan tsaye, sai da ta kammala tas ta zo ta zauna ta baiwa Innar Hauwa kujera ‘yar tsugunne, itama ta samu waje ta zauna akan tabarmar kofar dakin ta, suka gaisa kadaran kadahan sai Inna tace.
“Zuwa nayi mu gaisa Maikosai, naga kowa na zuwa muna gaisawa, ke kadai ce ban gan ki kin zo ba, shine na shigo in gaida ke, Allah dai yasa lafiya”, inji Inna.
Mai kosai ta ce “in kinji shiru ai shine lafiya, lafiya ke buya ba rashinta ba, don haka ni lafiya ta kalau, har kin yi GAIBAR ne kin dawo?”
Cikin rashin fahimta Inna tace “menene kuma GAIBA?” Maikosai ta kalle ta a lalace tace “kina nufin ni zaki binne a baibai? Ko ba da hausa nake magana ba? Kin dauka ban ji me kuke shiryawa ke da bazawarin ki Malam Isa Mai Itace ba, na kiyi Gaiba ki dawo ya aure ki?
Allah na tuba ko meye abin likewa tsoho kamar malam Isa oho, yana fama da kakhi da majinar tsufa?”
Inna tace “innalillahi wa’inna ilaihi rajioun, ni Safiya me nake ji haka? Da auren nawa na likewa Malam Isa? Ni Safiyar ko dai wata ce kike nufi kika dauka ni ce?” Maikosai tayi tsaki tace.
“Ahap! Da bakin sa ya gayamin kin dawo zakuyi Gaiba ya aure ki, ko kin dauka akwai abinda yake boye min?”
Inna ta mike tsaye tana fadin “Maikosai baki da lafiya, ina rokon Allah ya baki lafiya”, daga haka ta fice ta barta tana ta sakin maganganu marassa kai bare kafa.
A zaure ta ci karo da Malam Isa zai shigo, cikin far’a Malam Isa yace “a’ah, Innar Hauwa da kan ta yau a gidan mu? Maraba lale”, wani kallo da Innar Hauwa ta yi masa yasa nan da nan ya sha jinin jikin sa, yayi tsuru-tsuru kamar bafaden da yayiwa sarki karya, tasa kai ta wuce abinta ba tareda ta ce masa kanzil ba.
Malam Isa ya fada gidan sa kamar an jefo shi, yana kwalawa Maikosai kira, a zaune ya sameta tana ta kunkuni ita kadai yace “uban me kika cewa Safiya?” Tayi tsaki tace “munafurcin da kuke kullawa na gaya mata na san komai” Malam Isa ya yi salati yace “amma Maikosai anyi dabba a cikin garke, kin jika min aiki, tsakanina da ke Allah ya isa”.
Maikosai ta tafa hannu tace “kace haka mana, saboda kafi so ku cigaba da ninke ni a baibai, saidai inji sallamar kishiya a kaina, duk abinda kuke ciki na sani, da zaryar da kake tayi a gidan su, har kuka yi kulla-kullar da kuka nemo ta kuka dawo da ita unguwar nan duk don kana kulafucin ta”.
Malam Isa bai iya tsayawa ya cigaba da sauraron ta ba ya juya da sauri ya bi bayan Innar Hauwa.
Tana isa gidan shima ya iso sabida saurin da yake yi saura kadan babbar rigar sa ta tadiye shi.
Tana shiga gidan ya doka sallama sai Inna ta dauko mayafinta data rataye a jikin kofa ta fito. Sabanin da da zata yi masa iznin shigowa yanzu sai ta fita ta tadda shi a zauren.
Suka gaisa Malam Isa yanata rawar jiki yana bata hakuri wai bai san me Maikosai ta gaya mata ba. Inna ta dube shi da manyan idanun ta irin na Hauwa masu neman fadowa kasa sabida girma ta ce.
“Malam Isa, mutunci da makwabtaka ne tsakanin mu, ina ganin girman ka da mutuncin dake tasakanin ka da maigidana, da hakkin makwabta da kake saukewa dare da rana, bai kamata kuma ka yi min kazafi ba ban ji ba ban gani ba, yaushe nace zan yi GAIBA? Balle har na aure ka?”
Malam Isa ya hau gumi yana bata hakuri yace wallahi shi da bakin sa bai yi zancen nan da Maikosai ba, ya dai yi zancen cikin hira da Dan ta Sunusi, inda yace masa “da ace zata yi Gaiba….”.
Bayan wannan bai kara komai ba, watakila Sunusin ne ya gaya mata, ita kuma ta canza maganar yadda taga dama, amma ta yi hakuri. Inna tace “baka yi min laifin komai ba sai alkhairi Malam Isa, amma ka sani ko Malam Bilyaminu bai dawo ba bazan yi wani aure ba, daga nan har gaban abada!
Burina kadai a duniya “Hauwa ce”. In rayu tare da ita, in kula da ita, in tsare mata mutuncin ta. Amma bayan wannan bani da wani sauran abu da ya rage min a rayuwa ta sai fatan cikawa da Imani”.
Malam Isa dai hakuri yake bayarwa, ya kuma roketa kan kada hakan yayi sanadin bacin zumunci da makwabtakar su, ya bar zancen har abada ba zai sake tada shi ba, don Sarham ma ya hanashi. Maikosai kuma zai ja mata kunne itama. Inna tace babu komai. Ya wuce.
Daga nan ya gaya mata maganar dabbobin ta daya kiwata mata, suna nan garke guda a cikin kangon gidan sa. Inna ta rasa da me zata godewa wannan karimin makwabci, ta yi masa godiya mai tarin yawa don tana matukar son dabbobin ta. Tace ya bar su anan su cigaba da zama tare da nasa, zata cigaba da bada abincin su. Wanda yayi a baya Allah ya biya shi da aljannah. Nan yake gaya mata ai SARHAMU yafi shekara yana sayen dussar su da harawar su.
Mamakin Inna da Sarham ya kara

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login