Showing 42001 words to 45000 words out of 45645 words

Chapter 15 - Hauwa Kulu Book 2 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

140

Ya dago ya dubeta da jan ido, a lokacin taga idanuwansa sun kada, yace “a’ah Summy ce yau a gari? Saukar yaushe?” Tace tun dazu na sauka, ta gabana fa ka wuce, har ido mun hada, ka san mun yi hutu shine fa nace bari kawai in taho ganin Hauwa’u”.
Ta zauna a kujerar ‘sofa’ kwaya daya dake dakin, ta ce “Bhaiya duk ka birkice, you are upset, anya lafiya kake kuwa? Na ganka ‘moody’ tunda ka shigo”. Yace “Sumayyah, bansan yadda zaki fassara abinda ya sani a damuwar ba idan na fada miki, ba wani abu bane serious I don’t know why I made it serious, abun ne ya bani mamaki, ya kuma bata min rai, wai Hauwar nan da kika sani ko ido bata da shi, amma ta iya tsayawa zance da saurayi a soro???
Ni ban taba ganin abinda ya bani mamaki ya rikitani irin wannan ganin dana yi ba”.
Sumayyah tana sane tace “Hauwa wacce? Baby Hauwan mu?” Ya harareta, “ke bana son sakarcin banza. Hauwa ‘yar Inna mana, kanwata ta kofar Na’isa” Sumayyah ta wani ce “au ho! Ka ce min kawai Hauwar Inna, HAUWA-KULU ‘yar cikin BADALA!”. Sai ta hau tuntsira dariya tace “Bhaiya, yanzu ganin Hauwa da saurayi shine abinda ya birkita ka haka?”
Sarham ya harareta yace “Sumayyah yaya ina miki magana ‘serious’ za kina dariyar rainin wayo, Hauwa fa, wadda ko ido bata da shi, ina zata kai wani namiji da sunan soyayya?
Ganin ta nayi da wani cousin dinta suna zance fa, zance na saurayi da budurwa! Wai sunan sa Jamilu, dan kanin Babanta ne”.
Ai kuwa Sumayyah ta kara tuntsirewa da dariya sai da tayi mai isarta, shi kuma ya shaka sosai, saida dariyar ta lafa mata ta ce.
“Bhaiya makaho ba mutum bane? Ko kuwa makaho bai san SO da mai son sa ba?
Don tana makauniya shikenan sai akace bazata yi aure ko soyayya ta ji dadin rayuwar ta kamar kowanne dan adam ba? Ko in bata saurari masu son ta ba kai din auren ta zaka yi?
Yau nake ganin ikon Allah, yau ina ganin abinda ya gagari Kakata Kulu, kai ka dafe dahir har da ‘yar ka tubarkallah, shine ita zaka yi mata fatan ta tsufa a dakin uwar ta, alhalin kai ba son ta kake yi ba, wannan fa shi ake kira karfin hali barawo da sallama ko in ce, Bhaiya na, da tsabar son kai tsagwaro. Wani hali da ban san shi da shi ba.
Ni wallahi gani nake ma babu wanda ya dace da ya aureta kamar dan uwan nata, tunda jinin su daya, ya san darajar ta, zai yi hakuri da nakasar ta, ya riketa da daraja a gidan aure, don kai kam Bhaiya, baka da alqiblah.
Ayi magana cibi ya zama kari!”.
Ta sake tuntsirewa da dariya ta ce “sai amara kirazan biki, mu ne manyan kawayen amarya Hauwa’u, a bikin ta da Yayanmu Jamilu”. Sumayyah har da dan gudu-gudunta ta bar dakin, tana cigaba da tillika dariyar shegantaka. Don ta san ta gama kunna shi in ta kara minti uku a gabansa zai iya losing control kai mata duka. Don tana ganin yadda yake girma idanunsa tunda ta soma shegantakarta.
Maganganun ta dinnan, suka taru suka zamewa Dr. Sarham “a warm food for thought!” A tsayin wannan daren bakidayansa kona rabin away a kasa runtsawa.
Sarham sai faman juyi yake a kan gadonsa, daga wannan gefen zuwa wancan, yana tauna maganganun Sumayyah a kwakwalwarsa, yana kuma fassarasu a zuciyarsa cikinma’auni na hankali da tunaninsa. Daren da yazo masa da tarin ‘alterations’ koko ‘revolutions’ wadanda a can baya bai taba hango yiwuwar makamantansu ba.
Ko na minti daya ya kasa rintsawa. Idan ya tuna maganganun Sumayyah. A ganin sa Sumayyah maganganu ta gasa masa masu zafi ta cikin ruwan sanyi, koko yace jirwaye tayi masa mai kama da wanka, don dama tana kullace da shi akan abinda yayi mata, don kawai ta tambaye shi ko son Hauwa yake yi shekarun baya, bazata manta ba yayi mata wulakancin da bata zata ba, kiris ya rage ya doketa. A nata bangaren Sumayyah, ta dade tana kiwon mu’amalar sa da su Hauwa ta rasa alkiblarsa, musamman in ta tuna abinda yayi mata daga ta tambaye shi ko son Hauwa yake? Ta tuna a ranar dukanta ne kawai bai yi ba, shine abinda take nufi da “ayi magana cibi ya zama kari”.
Da gasken gaske ya kasa barci a daren, sai faman tauna maganganun Sumayyah wadanda ya kira jirwaye mai kama da wanka.
Washegari ya samu kansa da kasa zuwa gidan Inna, saboda har zuwa lokacin ransa a bace yake, haka a sauran kwanaki ukun da suka biyo baya ko hanyar kofar Na’isa bai kalla ba, yana like wajen su Waheedah, kamar ya maidasu ciki, don a can yake samun sanyin ran sa, daga zafafan maganganun Sumayyah da haushin Hauwa (a ganin sa bakaken maganganu ne Summy ta gasa masa son ran ta), da suka dade suna dafa shi kamar dafaffiyar masara, kuma ya kasa cewa Sumayyah komai a kai again bayan kuma ita kadai ce zai iya zancennan da ita. Madinah ta samu lokacin sa sosai a wannan satin, don yanzu kullum yana wuni tare da su baya zirga-zirgar gidansu Inna.
Inna na talgen tuwo a yammacin yau da Sarham ya kwashe kwanaki bakwai bai zo gidan su ba, sai ya fado mata a rai, ta dubi Hauwa dake wankin sittirun ta a bakin famfo tace.
“Kuluwa!”
Hauwa ta tsuke baki ta kuma tsuke fuska bata amsa ba, ai ta san in ta ce mata Kuluwa bazata amsa ba, sai ta ce “ni kuwa kin lura da abinda na lura da shi?” Hauwa tace “me?” “Likita Sarhamu, yau kwana bakwai bai zo gidannan ba, tun ranar da ya zo yace min kansa na ciwo, yanzu haka jikin ne ya matsa masa tunda har kika ga yayi wannan dadewar bai zo ba”.
Hauwa ta yi shiru bata ce komai ba, ta cigaba da wankin ta, ashe ba ita kadai ta lura da rashin zuwan nasa ba. Inna ta sake cewa.
“kin ga da ace na san gidan su sai in je in duba shi”.
A nan ne Hauwa ta bata amsa,
“kai su Inna akwai wuce gona da iri”.
“Ba wuce gona da iri bane Hauwa-Kulu, baki ji fadar bahaushe ba? Yace KA GAIDA MAI GAISHEKA KO DA BAZAI AMSA BA!”
Wannnan magana ta karshe da Inna ta yi, ta yi ta ne a kunnen dan halak din wato (Sarham), don a lokacin ya iso tsakar gidan da kasaitattar sallama a bakin sa.
Nan da nan Inna ta bar abinda take yi a madafin ta fito, ta washe baki tana amsawa, “maraba da Da na Sarhamu, likita Sarhamu na ne tafe? Dan halak yanzu nake zancen ka, sai gaka”.
Sarham ya tsugunna a kofar kitchen din yana gaida Inna, Inna ta koma ta kashe wutar tuwon, ta taso suka shiga falon ta tare, suka kara gaisawa, Inna sai taga duk ya rame mata, tace “Likita jikin ne ya boye ka ne?” Ya ce “a’ah Inna lafiya ta kalau, kwana biyunnan dai ban cika fitowa ba, ina can wajen su Hauwa’u karama kullum”.
Hauwa ta shigo da sallama tana dan dafa bango, ta isa kofar dakin ta sannan ta juyo saitin da ta ke jin tashin tattausar muryar Sarham, ta ce cikin girmamawa “Dr. barka da zuwa, ina wuni?”
Ya dago kai ya kalle ta kadan, kayan jikin ta sun dan jike sun manne a fatar jikin ta, Hauwa yar shekara sha takwas ta gama samun duk wani dirin jikin da jikinta zai bayar, da kyakkyawar suffa na abinda ake nema a tare da budurwa ‘teenager’, nata har ya zarta yawan shekarun ta, don tsammani zakayi ta kai shekaru ashirin da daya.
Tun asalinta Hauwa bata da rama haka take ‘yar duma-duma, lubu-lubu (luscious). Dr. Sarham ya yi wata ‘yar ajiyar zuciya ba tareda ya san ya yi ba, yana tuno kwailancin ta na shekaru biyar a baya, wai itace haka yau a gabansa, yace a hankali “lafiya kalau, ina Saurayin ki dan polo dan gayu?” ‘yar dariya Hauwa ta yi, ta shige dakin ta bata ce masa komai ba.
Sai Inna ce tayi kwafa ta ce, “ai ka bar ni da Hauwa da Jamilu kawai, nice maganin su da rashin kangadonsu, da ni suke zancen wallahi, na sa uwarsa Rumanatu tayi musu iyaka, idan yaji toh, in bai ji ba na rantse zan iya kai shi kotu don alkali yayi musu iyaka.
Na fada na kara ni fa bazan taba yi wa Hauwa wani aure ba, balle in bawa dan Zakari.
Allah na tuba ko dan shugaban kasa ne ya zo neman auren Hauwa, wallahi bazani bayar ba, balle dan Zakari tsatson zalunci.
A cikin burika na masu kyau a kan Hauwa, babu batun yi mata aure a ciki, babban burina shine ta yi karatunnan na zamani mai zurfi in dai makafi na iyawa kamar yadda ta fara, ta samu abunda ko bayan raina zata dogara da kan ta, kuma in karfina ya kare kada nata raunin ya bayyana dalilin rashin karfi na, ko in ta Allah ta kasance min hakan ya kassarata.
Ni din nan nice karfin Hauwa, ni ce kuma idanun ta, bazan taba bari a wulakanta min ita da sunan aure ba, ko a ci mutuncin lalurar ta a dalilin aure, shi yasa na gwammace in adanata a gabana, in kula da ita, tayi ta karatu, duk da ni ma ba karatun nayi ba, amma alhamdulillahi ni lafiya ta kalau, zan rayu ko ba ilmin zamani ba tare da na zamewa kowa labiliti ba.
Amma Hauwa fa? Ai duk wanda na bawa auren ta na kware shi, domin na hada shi da aiki da jidali. Itama kuma na sayo mata rashin kwanciyar hankali. Don haka maganin kada a ji, kada a soma.
Gashi bani da matallafi namiji wanda zai tsayawa Hauwa ta samu ta yi karatun nan tunda ni bansan kansa ba, da wannan yau nake baka amanar Hauwa-Kulu Sarhamu, ina mai baka amanar ta don na amince maka, na kuma amince bat un yau kaunar ka damu ta saboda Allah ce.
Don Allah likita ka taimaka min, wajen cikar burika na a kanta, na tayi karatu mai zurfi wanda zai amfani al’umma ya kuma amfane ta duk da nakasar ta. Bana so nakasar nan tata ta zame mata rauni, so nake nakasarta ta zama ado a gareta.
Inna ta soma sharar hawaye ta ce “gashi Bilyaminu ban san inda yake ba, bansan a halin da yake ciki ba, yana mace ne ko yana raye Allah masani, na tabbata da ace yana tare da mu, shima burin sa zai zama irin nawa ne akan Hauwa, don a komai muna kasancewa da ra’ayi daya ni da shi.
Allah ya gani bazan iya baiwa Jamilu auren ta ba duk da na san a shirye yake da ya tsayawa Hauwa, ba don komai ba sai don ubansa, amma ba don yayi min wani abu ba, ko bai cancanta a bashi aure ba.
Ko Hauwa-Kulu zata tsufa ba aure, tana nan a kwibi na, (a kusa da ni) ba inda zata da sunan aure”.
Hauwa daga dakin ta duk tana jiyo abunda Inna ke fadi akan ta, sai ta samu kanta da dimaucewa, don fisabililahi ko ba’a fada ba ta san zuciyarta ta amince da Yaya Jamilu dari bisa dari, yau ga Inna na cewa a dakin ta zata tsufa. Ya Allah! Itafa mantawa take da makantar nan tata, idan har ba bude littafi da zummar yin karatu taga duhu didim tayi ba, mantawa take bata da ido, saboda rayuwar ta cike take da baiwarwaki da kuma alfarmomin Ubangiji masu yawa da wadatar zuci.
Ji take babu wani abu da mai lafiya yake yi a rayuwar duniya wanda bazata iya ba, musamman aure da hayayyafa.
Inna da Sarham sun jima suna hira, yana zaune dirshan a gabanta. Inna nata kashe zuciyar Sarham da kalamanta masu nuna hakikanin MOTHERHOOD a kan diyarta Hauwa-Kulu, yau ya fahimci ba karamin so Inna take yi wa Hauwa ba.
Ya ci tuwon da Inna tayi kafin ya tafi wanda tuwon masara ne miyar yakuwa, ta zuba masa soyayyen manshanu a ciki da yankan naman rago biyu. Ta kuma hada masa lamurje/zobo mai sanyi wanda tasa a firjin Hauwa yayi sanyi.
Dr. Sarham tunda ya bar gidan su Hauwa ba tareda yau ma ya iya tsayawa a kofar dakinta yadda ya saba ya yiwa Hauwa sallama ba, kasa shiga Sorondinki yayi yau, saboda halin da ya samu zuciyar sa a ciki a kan maganganun da suka yi yau shi da Inna heart-to-heart, ta gama fede masa zahirin abinda ke karkashin zuciyar ta akan miskiniyar diyar ta, HAUWA-KULU, wanda dan cikin ta kadai zata iya gayamawa, amma shi yau ta zaunar dashi ta gaya masa duk wani abu dake karkashin zuciyarta a kan future dinta bisa radadin da take ji na nakasar diyarta.
Kai tsaye ta bayan gidan ya wuce ya lallaba ya shige dakinsa, ba tareda kowa ya san da dawowar sa ba.
Sarham ya kulle kansa don kada Sumayyah ta zo ta dame shi da dumi, dama kuma Inna ta ciko masa cikinsa taf da abincin ta, don haka baya bukatar karin cin abincin Mama yau.
Ya kwanta a ranar a tsakiyar gadon sa yana tunanin maganganun Inna, ya kuma debo na kanwarsa Sumayyah na rannan ya kara akan su, wato yayi addition, yana tarawa yana debewa, tsakanin maganganun Inna da maganganun Sumayyah….
Sumayyah ta ce “Hauwa mutum ce kamar kowanne dan adam, tana da right din yin aure da bukatar yin sa kamar kowa ‘in spite of her disability’, Uwarta kuma ta ce ko zata tsufa a gida bazata bata wannna damar ba.
Ba don komai ba sai don tana guje mata wulakanci da tozarci a dalilin nakasar da shi Sarham yayi mata lasisin ta.
Bayan kuma addini da al’ada da ‘yancin dan adamtaka duka sun bata damar yin aure. Shin tsakanain Inna da Sumayyah, waye mai gaskiya akan future din HAUWA-KULU???
A take kaso mafi rinjaye na zuciyar Sarham ya ce “Sumayyah ce mai gaskiya!!!
Ita Inna ba wai bata so Hauwa tayi aure bane a’ah, gudun kada a wulakanta mata ita ne da sunan aure, da guje mata tozarci da dawainiyar aure da take da tabbacin bazata iya ba sabida rashin ido, yasa ta gwammace tayi ta ajiyar ta a daki. Wato abinda ka san bazaka samu ba hada shi da bana so! Amma ita Hauwa din tunda har take kula Jamilu, to ya tabbata tana son tayi auren kenan ko bata furta ba. Don Inna ta gaya masa yadda Hauwa ke sakewa da Jamilu ita kanta abin yana bata mamaki matuka. Sai ya samu kansa da tambayar kan sa to KO DAI HAUWA SON AUREN JAMILU TAKE YI?
Sarham sai yaji ran sa yayi wani iri mummunan baci, a take wani tunani ya bijiro masa, me zai hana shi Sarham din ya aure Hauwa kowa ya huta (ko da baya son ta so irin na soyayyah irin wanda yake yi wa matarsa Madinah, don shi kadai ne solution ga rayuwar ta (shi Sarham din), da zamowa maslaha ga mahaifiyar ta, hakan zai fi alkhairi fiye da auren Jamilu ko wanin sa ga Hauwa. Tunda maganar Hauwa ta dauwama ba aure ba dabara bace so-karbau, a matsayin ta na ‘yar adam mai cikar lafiya da ‘sexual hormones’ kamar kowa dole tana bukatar yin aure.
A take Sarham ya shiga gayawa kansa; zai auri HAUWA-KULU domin wasu dalilai masu tarin yawa da ya dade yana dambarwa da zuciyar sa a kansu, amma ba don kalmar SO ta gitta ko zata gitta nan gaba a tsakaninsu ba. SO guda daya ne a zuciyar sa; kuma na matar sa MADINAH uwar Hauwa-Waheedah ne.
Zai auri HAUWA ne a dalilin ya san ta kullace shi, akan-karan kan sa kuma yana son kankare wannan kullacin nasa dake kasan zuciyarta, har gobe ya kasa yafewa kansa zama sanadin makantar ta. Babu kuma ta hanyar da zai iya kankare wannan tabon nasa daga ran Hauwa in ba ta sanadin aure da hayayyafa ba.
Zai kuma yi amfani da kwarewar sa ta yanzu, wajen ganin ganin ta ya dawo, koda ba duka ba, da iznin Ubangiji.
A karshe ya gayawa kansa zai auri HAUWA domin yana tausayin Inna, kuma yana kaunar ta, don haka zai karbi amanar nan data bashi ne ta hanyar AURE wanda ta hanyar sa ne kadai zai iya cika mata burin ta, na kular mata da ilmin Hauwa da rayuwarta gabadaya, zai yi kokari wajen cikawa Inna burikan ta a kan HAUWA-KULU ne kadai idan ya samu damar auren ta tunda shi ba mazaunin Kano bane. Auren Hauwa gareshi ta kowanne bangare JIHADI ne maigirma kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login