Showing 21001 words to 24000 words out of 45645 words
ya zauna yace “wash! Abba, kai na!” Ya kama kannasa da hannu bibbiyu. Abba ya ce “sannu, Sumayyah kawo masa ruwa da abinci, hajijiya ai yunwa ce, me ke faruwa?”
Sarham bai san lokacin da yace “Abba na neme su na rasa, ba inda ban dub aba, ba Badalar Kano da ban zagaya ba, ko mai kama dasu ban gani ba, duniyar nan cike take da azzaluman ‘yan uwa Abba, kowanne dan uwa ya samu faraga sai ya ci amanar dan uwan sa in baya nan, why?”
Surayyyah ta saka kuka don ta dauka wannan maganar da ita Sarham yake ta ce “wallahi Bhaiya ban yi da niyyar cin amanarka ba, na tuba ni kam na shiga uku! Ka dauki abinnan da zafi har fiye da kima Bhaiya” wata uwar harara daya zabga mata ya ce a fusace “na saka ki a cikin magana ta? Kin san wa nake nufi ko su wa nake magana akan su?”
Mama ta ce “kayi hakuri Sarham, zancen nan ya wuce don Allah bazata sake ba na mata fada sosai”.
Yace Mama ni ba zancen ta nake ba Mama, already na yafe mata, na fadawa kaina da kaina na yafe mata yafi sau shurin masaki, tun fita ta ban fita da ita a raina ba, zancen su Inna da Hauwa nake,”
“Su waye kuma Inna da Hauwa kuma?”
Abba da Mama har suna hada baki wajen tambaya, da tunanin ko gamo yayi, ya ce “yarinyar da ta makance a hannu na, (excuse me) na makanta ta by mistake, tun daga lokacin kuma nake kula da karatun ta.”
“Au ho!” in ji Mama, ai kuwa ban manta da zancenta ba, da yadda ka shiga damuwa a lokacin, har yanzu idon nata bai gyaru ba? Kuma wai basu da Uba ne?”
Sarham ya baiwa iyayen sa kaf labarin su Inna, tun ranar da suka fara haduwa a asibitin Murtala, da aikin da yayi mata da sabon da ya shiga tsakanin su aftermath wato bayan hakan, da yadda aka yi ya kai Hauwa makarantar (Special School Kano), da yin sallamarsu lokacin da zai tafi Jeddah, zuwa yanzu da ya dawo yaji abun da ya faru da su daga kanin Baban ta, ya kuma gaya musu batan Malam Bilyaminu tun kafin haduwar sa da su.
Mama don tausayi har da kwallah tace “Allah to ya jefa su a hannu nagari, ya kuma bata lafiya a duk inda take, kai kuma ya baka ladan taimako”. Abba yace “amin, Allah kuma ya saka musu. Ya bi musu hakkin su. Amma don Allah ka ci abinci, ka huta, ka nutsu, ka tuna cewa kaifa sabon Ango ne akwai nauyi yanzu a kan ka.
Ya gaya masa cewa sunyi waya da Daddyn Madinah dazu, nan da kwana uku za’a taho da ita Kano, ba sai ya koma Jeddah dauko ta ba, Babanta yace ya daina cewa ango ya zo ya dauketa kasa-ya-kasa tun daga abinda ya faru kan mijin ta na fari, ina ya tanadar mata domin a sauke ta?
Sarham babu wani doki a tare da shi don zuciyarsa bakidaya bakikkirin take, yace shi ginin da ya fara bai kammala ba, sai dai Abba ya ara masa gidan sa na Rimin Gata (nan baya sabuwar jami’ar Bayero) a sauketa acan. Yace amma in son samu ne shi ya fi so Madinah ta zauna a nan gidan su tashin farko, ba don komai ba sai don ta saba da su Mama tunda na dan lokaci ne zasu koma Jeddah.
(A baya baiyi niyyar komawa Jiddah ba amma yanzu Kano ta fice masa a rai). Daddy ya ji dadi sosai, don a yadda na gina rayuwar iyalinsa da so da kaunar juna, kwarai yake so matar duk da Sarham ya aura ta zamo daya daga cikin iyalin sa, baya so don yayi aure yayi nesa dasu, musamman saboda shakuwar sa da kanwarsa Sumayyah, shakuwar dake tsakanin su har tsoro yake kada yayi aure mace ta zamo sanadinta, Abba ya ce,
“shike nan hakan yayi kyau, madallah, ita Sumayyah sai ta koma dakin Surayyah, su zauna tare for the mean time, sai a gyara ma Madinah dakin Sumayyah ta zauna har zuwa lokacin da zaku koma Jeddah din, Abba ya tambayeshi ko ya gama kwas din sa? kuma yaya batun aikinsa na Murtala da yake batun komawa? Ya gaya masa cewa ya gama, amma zai koma bikin kammalawa da karbo shaidar kammalawa, shi da Madina har yanzu basu zauna (officially) sun magantu sun yanke shawarar inda zasu zauna ba. Amma yanzu kam yafi so ya koma Jeddah.
Bayan ya koma dakin sa yayi wanka ya yi sallolin dake kansa sai ya samu kansa da zama dirshan akan dardumar sallahrsa ya rasa abinda ke masa dadi, abun mamaki ga kiran Madinah na ta shigo masa akai-akai don tun bayan da aka daura musu aure basu yi magana ba, amma ga mamakin sa ya kasa dagawa, a lokacin damuwar da yake ciki tasa komai ya fita kan sa, ya samu kan sa da daga hannu yana yiwa su Hauwa addu’a, damuwa tasa a ranar ko runtsawa na awa guda bai iya yayi ba.
Washegari yaje ya kai kudin filin gidan su Hauwa, ya karbi takardun filin a gaban kwararan shaidu dattijan unguwa su malam Isa da sabon mai unguwa, kowa yana ta mamakin ko me zai yi da filin, shi ba dan unguwar ba, ba kuma dan Malam Bilyaminu ba, amma dai ai yace shi dan uwan Innar Hauwa ne.
Wayar da ya sayawa Inna sai ya samu kansa da mallakawa Malam Isa, ya kuma karbi lambarsa yace zasu dinga gaisawa kuma zai dinga turo masa kudin abincin dabbobin Inna da yake kiwata mata, ya fadi hakan ne a lokacin suna cikin garken dabbobin, suna zagawa yaa kallonsu, ya ga yawan su ya karu nesa ba kusa ba akan sanin da yayi musu, sosai ya jinjinawa Malam Isa da iya kiwon dabbobi da zuciyar makwabtaka irin ta mutanen da, ya kuma yanke shawarar taimaka masa akan kiwon dabbobin shima daga ranar da kudin abincin su.
Malam Isa yana ta murnar mallakar waya, saboda a lokacin bata zama a hannun talakawa, ya sakawa Sarham albarka yafi cikin carbi. Da zasu rabu kuma Sarham ya gaya masa niyyar sa, wato yana so ya gine filin nan, so yake ya a gina musu gida kwatankwacin nasu a filin su, gini na zamani, ya ce shi ba mazauni bane don haka zai turo magina kuma zai bar komai a hannun sa da masu ginin, yana so Malam Isa ya kula da ginin har a gama, don zai jima bai dawo Kano ba.
Malam Isa yana ta mamaki, ko meye alaqar wannan matashin mai kirki da kyakkyawar zuciya da su Innar Hauwa haka, haka suka yi sallama bayan Sarham yayi masa kyautar kudi, kuma a washegari aka saka tubulin harsashin ginin gidan su Inna da kudin da jima yana Tarawa don yin nasa ginin gidan.
Kwana uku bayan nan, ba abinda Sarham yake yi sai yawo a cikin garin Kano yana faman neman INNA da HAUWA har tambaya yake yi ko an san su, ya fasalta kamannin su, maimakon ya maida hankali wajen shirin taryar amaryar sa Madinah-Munawwarah mai isowa daga Jiddahn Saudi Arabia.
Amma ko wanda yace ya san mai kama da su bai samu ba. Wannan yasa duk zaman garin Kanon da dokin amarcin dake gaban sa ya kara fita a ran sa. Ya sa a ransa da Madinah ta zo bazasu dade ba kamar yadda yayi niyya zasu koma Jeddah, in yaso ya karbi tayin aikin da aibitin “SAUDI-GERMAN” suka yi masa, wanda a baya yaki karba, don ya so ne ya dawo gida kwata-kwata ya cigaba da aikin gwamnati a manyan asibitocin Kano da ya tabbatar sun fi bukatar sa, in yaso ya bude private clinic nasa na kansa ya hada, amma a yanzu bai san haka zuciyar sa ta dauki su Inna da matukar muhimmanci ba sai yau da take gaya masa rashin su ba zai sa ya ji dadin zaman Kanon bakidayanta ba, duk da gatan iyaye dana ‘yan uwa dake baibaye da shi, ga na cikar buri, wato na mallakar Madinah abar son sa.
Amma duka ya kasa enjoying ko daya. Saboda wasu bare? Ya ilahi, wane irin abune haka??? Shi kansa yana mamakin karfin ‘bond’ din dake tsakanin sa da ‘Inna’ don bazai ce ‘Hauwa’ ba.
Don haka sai mu ce Amarya Madinah ta shigo kasar Nigeria da kafar hagu, don kuwa likitan zuciyarta Sarhamu babu walwala kota kwabo a tare da shi, gabadaya ya birkice da neman Inna da Hauwa, har iyayen sa suka fara damuwa da saka ayar tambaya, suka zaunar da shi suka ce ya gaya musu gaskiya, bayan tausayi da taimako, meye alakar sa da mutanen nan ne?
Ta yaya zai yi sabon aure amma ya raba hankalin sa da nutsuwar sa, ai sai suma ya saka su a damuwa.
Sarham ya ce babu wata alaqa tsakanin sa da su, sai kauna ta fisabilillahi da haduwar jini, yace shi kawai yana tunanin a wane hali suke ciki ne, yana tsoron fadawar su mugun hannu ko fadawa hannun kanin uban Hauwa wanda baya kaunarsu kuma azzalumi ne, sannan basu da kowa da zasu kira nau in ba shi din ba (Zakari).
Mama tayi fuska ta ce daga yau bana son ka kara fita neman su tunda dai ba kananan yara bane, Allah shi yake kula da bayinSa marassa karfi da masu karfi, kafin ka shiga rayuwar su ai babu uban nasu, kuma hakan bai hana su rayuwa mai kyau da shaker numfashi ba. Saidai ban sani ba ko kana da wani dalilin a kasan ran ka a kansu bayan wannan?”
Wai meyasa mutane suke kasa fahimtar sa ne akan Hauwa da Innarta? Zai iya rantuwa babu wani dalili a kasan ransa a kansu bayan wanda ya fada musu. Kwatakwata kenan babu alaqa ta mutunci da zumunci a tsakanin al’ummar Annabi sai mai kunshe da MANUFA? Haka mafa Sumayyah ta taba cewa wai….. abun babu ko dadin ji domin kuwa yadda yake kallon ta muharramar sa haka yake kallon HAUWA-KULU.
Can tsakar kansa ya tsinkayi sautin Abba yana cewa “talakawa nawa ne a Nigeria da suke cikin halin kaka-nikayi? In ka ce duka sai ka tsayawa rayuwarsu ka hada kan ka da abinda ba zai taba yiwuwa ba, tunda dai kayi taimako iya yinka wanda dace ya kamata ka bar su a hannun Ubangijin da ya halicce su haka, ka maida hankali ga abinda ke gaban ka yanzu. Wato sabuwar rayuwar ka ta girma da yah au kanka”.
**** **** ****
THE ARABIAN BRIDE
M
adinah na gidan kakannin ta bayan saukarsu a Kano, a daren ranar za’a kawo ta wajen Mama, an gyara dakin Sumayyah da kyau wato inda za’a sauke ta da ‘yan uwanta. Gidan ya dauki kamshin turaren wuta dan Maiduguri ko ta ina mai dadin kamshi, Mama da kawayen ta su Barr. Hannatu Mahdi da ’yan uwanta suka shirya karbar amarya da danginta.
Har falon Mama aka shigar da Madinah-Munawwarah cikin lullubi, kafin a yi addu’a ta musamman ‘yan rakiyar amarya da ‘yan karbar amarya duk suka watse, gidan ya rage sai mutanen gidan kadai.
Rana ta farko dasu Mama suka ga fuskar Madinan Sarham. So beautiful da ita, karshen gayu karshen class, Masha Allah.
Mama ta ce a ranta dole kam Sarhamunta ya kamu ya tsunduma iya wuya, Madinah ko daga cikin lullubi kafin a ganta a zahiri an san matar manya ce kuma ‘yar manya ce.
Tayi fatan Allah ya basu zaman lafiya da zuri’a mai alkbarka. Ya kade fitina, ya basu ikon sauke amanarta da aka damka musu.
Yau Madinah ta samu kanta a gidan surukan ta wato iyayen Sarham suna ta haba-haba da ita. Sumayyah da Surayyah ma ba’a bar su a baya ba wajen kula da bakuwar tasu, Surayyah kuwa duk da ‘yar tsamar dake tsakanin ta da Sarham sai da ta kasa shiru, da ya shigo gaida Mama bayan ya dawo gidan da daddare sosai tace dashi.
“Yaya Doctor, wallahi ka iya zabo mata, class iya class malam, kyau iya kyau, dubi mata kamar hurul- eeni, kamar ita tayi kanta don kyau da gayu.
Wata mummunar harara Sarham ya zabga mata yace “ki fita idona in rufe, ki bar shiga harkata, na rantse Mama ki raba ni da Surayyah”. Sannan ya gaida Mama da gajiyar hidimar jama’a, wadda keta dariyar masifarsa, Mama tace “ban taba ji ko ganin ango yana masifa ba, duk wani ango far’a yake yi da farin ciki banda kai, tashi ka shiga dakin Sumayyah Madinah din tana can”, cikin jin nauyin Mama irin wanda bai taba ji ba a rayuwarsa yace,
“Mama ki barta, sai da safe in Allah ya kaimu zamu gaisa in sha Allah, a barta ta huta, na san ta gaji, gata bata jure hayaniya”. Nan kuwa kunyar idon Mama ya hana shi zuwa yiwa Madinah barka da sauka cikin rayuwarsa.
Sai da ya koma dakin sa yayi shirin kwanciya sannan ya kirata a waya, Madinah ta fito wanka kenan tana saka kayan barci zata kwanta kiran sa ya shigo mata, sai da ta ja aji, don taji haushin kiran data yi masa bai dag aba kuma bai biyo bayan kiran ba, kafin ta dauka da kyakkyawar sallama a bakin ta, maimakon ta ce tayi fushi, saboda bai zo inda take ba tun saukar ta a Kano, ko irin kananan korafin nan na amare da ke cikin lokacin da ake mararinsu, ina! Madinah nata salon daban ne, da wuya kaga bacin ranta akan abu, komai tana kokarin maida shi ba komai ba a rayuwarta (banda kishin Sarham), don ko shi Sarham zai rantse bai san me yake bata ran Madinah ba, sai ta karya murya cikin rangwadarta da zakin muryarta tace,
“daga jin muryar ka mura kake, ina fatan angon Munawwarah yaci abincin dare?”
Sarham yayi wata wawuyar ajiyar zuciya, tuni ya manta da kishin da yaci alwashin gasata akansa da zarar ta shigo gidansa, wato fushin aurenta da AVM Alkali, ya samu kansa da cewa “kayya! Anyway, kin zo lafiya Madinahtul-Munawwarah, ya gajiya ya aka ji da zafin garin mu?”
Madinah tace “garin ku kai kadai? Ai ba’a canzawa tuwo suna. Zafi kuwa ai yana Saudi Arabia”, yace “kiyi min alfarma mu Arabian Bride, na san ke dinnan ma’abociyar tsinkaye, fahimta, da yi min uzuri ce, bazan iya shiga dakin Sumayyah inda kike ba kusa da dakin mahaifiyata ne, ba zan iya tsallake dakin Mama a gidannan in dinga zuwa inda kike ba, amma already nayi kokari nayi mana booking na komawa Jidda, don ni garin Kano ya fita kaina, zamu tashi rana ita yau in sha Allah muje mu ci duniyar mu da tsinke.
Na yanke shawarar karbar aikin nan na Saudi-German”.
Farin ciki mai yawa ya cika fuskar Madinah da zuciyarta, don dama tana cikin tunanin yadda zata iya rayuwa a garin Kano, ta shiga damuwa akan yadda zata iya rayuwa a Nigeria ma in general, tana dai daurewa ne albarkacin soyayya da yadda kowa nata ke lallashin ta, yayyenta kuma suke gaya mata aure babu inda baya kai mutum har bukka a jeji, amma hakika tafi son cigaba da rayuwa a Jeddah.
A can aka haifeta acan ta rayu, acan ta girma. Abinda ta sani ta kuma yarda da shi kawai shine; ko a cikin ruga zata iya rayuwa in dai da Sarham Abbas ne, kuma in dai zasu kasance tare karkashin alfarmar aure da ni’imarsa itada shi har karshen rayuwar su.
Sarham ya katse mata tunani, “kin amince ko?” Da sauri Madinah tace “haba-haba ai nima zan fi son hakan, da kunya kam mu kebe ko na minti biyu ne alhalin Mama da Abba suna cikin gidan, Allah ya kaimu lafiya, ni da ka kara mana wani satin ma a kan dayan ya zama munyi biyu tareda su kafin mu koma”. Yace “no, zamu tafi rana ita yau in sha Allah bana son zaman garin ne”. Ya tambayi Madinah ko me take yi yanzu? Ta ce ta yi wanka ne zata kwanta, ta gaji sosai, tace tun saukarsu a Kano bata huta ba. Sarham ya ce,
“ai kuwa baki ga ta barci ba, kamar yadda nima ban ganshi ba. On this special day, ki tashi ki dauro alwallah ki yi sallah raka’a biyu nima zan yi yanzu, mu godewa Allah da ya cika mana burin mu da cikar alkawuran da muka yi wa juna yau shekaru goma!
Kada ki manta a cikin sujjadar ki ta karshe ki roka mana ‘long life, prosperity, blessed children, unending love, and infinite peace. Madinah ina fatan ki zamo min ‘shelter’ kamar yadda birnin Madinah ya zamowa Annabin mu Shelter, refuge, security, safety and peace!”.
Madinah ta lumshe idanunta cikin farin cikin da bazai misaltu ba, tace “kaima ina rokon ka roka min aljannah, don Hajjah Ramlah ta gaya min aljannah ta yanzu ta tashi daga dugadugan su ta dawo bisa dugadugan ka.
Ka roka min ‘ya’ya masu yawa tare da kai kuma masu albarka, ka roka min Allah ya mallakamin zuciyar Sarham dina, nikadai raina bakidayan ta, don itace