Showing 45001 words to 45645 words out of 45645 words

Chapter 16 - Hauwa Kulu Book 2 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

138

solution ga rayuwa da zukatan bayin Allah masu yawa. Ba sai don SO kadai ake aure ba.
Ya san dole ce ta sata yanke hukuncin kin yi wa Hauwa aure, amma ba don bata so ba, tunda burin kowacce uwa shine ta kai ‘yar ta gidan miji, idan ta isa munzali.
Ta amma ta wacce hanya zai fara? Wadanne matakai zai bi wajen ganin tabbatuwar hakan? Ya san dai wannan hukuncin da ya yanke daidai yake da a ce ya daukowa kansa Dala babu gammo. To amma ya shirya kinkimar wannan Dalar, ya dora a kansa, koda kuwa babu gammon babu gudu babu ja da baya, in sha Allahu ruwa ko iska babu mai hanashi aiwatar da shawarar da ya yanke shi da zuciyarsa ta sanya HAUWA’U CIKIN IYALIN SA.
Sai dai kuma ta ina zai fara? Abin nufi ta wane bangaren???
Ta matar sa abar kaunar sa masoyiyar sa GIWAR SA MADINAH? Ko kuwa ta rigimammiyar uwar Hauwa wato INNA SAFIYYA? Wadda ta ci layar ko dan shugaban kasa bazata bawa auren miskiniyar ‘yar ta ba don kada a tozarta mata ita sabida nakasarta?
Ko kuwa ta bangaren mahaifin sa ABBA PROF.? Wanda tun asali alamu sun nuna ko zancen su baya so? Koko ta bangaren MAMANSA Mai Shari’ah Haj. Maimunatu???
Kowanne daya daga cikin wandannan bangarorin ya dosa da hukuncin da ya yanke, ya san babu sauki wai ciwon arne.
Dr. Sarham ya aje numfashi, ya muskuta ya gyara kwanciyar sa ya koma rigingine, daga kwancen da yake yana hararo jan aikin dake gabansa. Ya san da gaske ya daukowa kansa DUTSEN DALA da na GWAURON DUTSE kai har ma da duka KOFOFIN KANO da BADALOLINTA bakidaya ya kinkima ya dora a kan sa.
Shin ko wa zai taya Dr. Sarham saukewa kansa nauyin wannan kuduri da ya dauka? Ni dai na san mutum mai kyakkyawar zuciya da kyakkyawar manufa a kullum mai nasara ne akan duk abinda yasa gaba. Kuma kamar yadda Hauwa tace ne shi din mutum ne mai ‘abstract reasoning’ komai cudewar lamari baya kasa warware abinsa. Don haka ina yiwa Dr. sarham fatan nasara da fatan alkhairi da taya shi fafutukar kaiwa ga cikar kudirinsa na alkhairi.



MURFIN LITTAFI NA BIYU

Mu biyo “HAUWA KULU-AKA- (‘YAR CIKIN BADALA)” a littafi na uku, Ubangiji dai yayi alkawarin cewa “cikin dukkan tsanani akwai sauki”. Sannan a cikin biyayyar iyaye akwai babbar NASARA. Hauwa kuma tuntuni tayi aniyar yiwa Inna biyayya ta danne kwadayinta na dukkan dan adam, wato ta hakura da rayuwar ‘marital life’ da ‘motherhood’ daga yau har karshen rayuwarta domin yin biyayya ga Inna.

Shin kwadayin Hauwa na can karkashin zuciya zai tabbata? (Hauwa za ta samu damar yin marital life da motherhood kamar kowacce diya macen data kai munzali duk da lalurar makantarta? Ko kuwa zata dauwama ne a gaban Innarta tana kaf-kaf da abarta yadda Innar ta zabar mata tayi rayuwa???
Shin HAUWA-KULU zata yi rayuwar aure da tara iyali a yadda Ubangiji ke son ganin ta ko kuwa zata dauwama bisa tsarin Innarta?

Ina labarin Malam Bilyaminu har yanzu ne? A mace yake ko a raye?
Amsoshin duka wadannan tambayoyin in sha Allahu suna cikin littafin HAUWA-KULU kashi na uku.




Taku har abada;
Sumayyah Abdulkadir (Takori).
2/09/2023
07030137870
(WHTSAPP ONLY)


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login