Showing 1 words to 3000 words out of 41393 words

Chapter 1 - Mulki Ko Sarauta Book 1 Complete Hausa Novel

Nawarty   

01 Oct 2025

380

??ࡱ?>?? ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F?WordDocument????1?0Table???????? Data
???????????????????? P???KSKS?1?Y????????rrOc?4???? ? ? ? ? ? ? ? ? $O? *r? ? ? + ?c+ ? c? + c? ? c [2/3, 6:20 PM] Nawarty: Ms




Littafina na kud'i ne, dan Allah kada ka karanta idan baka biya ba, ga mai buqatar siya ya tuntubi wannan number 08169334980.

Saukar Abba gidan yaga abinda nayi matuqar tayar da hankalin sa sakamakon jin afiya ta dad'e da barin qasar, ransa yayi matuqar baci saura qiris ya kori suzana a gidan yanda yake fada sosai maaikatan gidan sun tsorata tabbas da ya sami afiya a ranar Allah kad'ai yasan me xai mata.

Haka ya kira ya sanar da sarki, amma me afiya ke nufi ta yafe su gabaki d'aya baxata koma gare su bane ko me dai dai lokacin kiran aiman ya shigo.

Tun da yaji labarin afiya ta bar qasar Portugal hankalin sa yayi matuqar tashi, ina ta nufa, me take nufi, sai yaji gajiyar dake jikinsa ta warware, cikin qanqanin lokaci yayi wanka ya shirya xuwa asibitin da aka kwantar da fadila, har lokacin babu wani cigaba tana cikin matsinancin hali.

Ya Allah ka bar fadila raye ka bata lafiya da duk musulmi da bashi da lafiya a wannan lokacin aiman ya fada idanun sa akan ta, duk kamannin ta sun canxa kamar ba ita ba, ya dubi mahaifiyar ta yana fad'in xuwa gobe xan shigo naga likitocin.

Allah ya kaimu yasa muna ganin goben.

Amin ya fad'a yana barin asibitin, bayan ya koma masaukin sa ga mamakin sa sai ya sami ilham a ciki bai kulata ba ya soma dialing number afiya da waccan wadda ya taba kira ta shiga wannan karon ma bata xuwa, ya kira Abba yana tambayar afiya ya sanar dashi tabbas afiya bata qasar.

Ya jefar da waya yana fad'in meyasa afiya take guduna a yanxu, why?

Ilham ta dubesa kamar baxa tayi magana ba sai kuma tace meyasa kake yawan kiran sunan ta a gabana, nima fa matar kace ya kamata ace ka fahimci haka,

Qirr yayi mata da idanu kamar mai son gano wani psycho a tare da ita a matsayin sa na likita, da kyar ya bud'e baki kamar xai yi magana sai kuma ya fasa.

Ta dawo gabansa tana fad'in amma meyasa kake min haka yarima, wallahi ina son ka, ko wane daqiqa na xuciya ta dake bugawa tare yake da qaunar ka, ta share wasu hawaye yana tare da fad'in ina da haqqi akan ka amma ka kasa bani har tsawon shekara biyu, na kasa samun kulawar ka, dariyar ka ko murmushin ka sai dai nagani kana yiwa wasu meyasa?

Da kyar yace kina so ki d'ora min wata damuwa akan wacce nake ciki a yanxu, matata da d'ana na rasa a yau amma har kike min maganar ina yawon ambaton afiya a gaban ki, wacece ke meyasa baxan yi maganar afiya a gaban ki ba, kinsan matsayin ta a guna kin gama sanin wacece afiya kuwa.

Ta girgixa kanta tana fad'in koma wacece ita nasan bata fini komai ba aiman, nima kyakkyawa ce ka sani, tana taqama da kud'i nima ina da su, menene afiya xata nuna min ko ta fanni sura wanda ni bani da shi, ta fada tana cire kayan jikin ta, duk abinda take aiman yana tsaye yana kallon ta har lokacin.

Ya rage daga ita sai shimi da under wear, ta d'ora hannunta a qugunta ta juya masa baya kafin ta sake juyowa, ka gayamin menene na rasa da kake gudu na ka kasa sona har yanxu aiman.

Ki cire sauran kayan dake jikin ki ya fad'a cikin halin ko in kula d'innan, kunya ta lullube ta taya xata iya bayyana jikinta ba sutura akai ya gani, wannan ma tayi qarfin hali ne tayi.

Ki cire kayan dake jikin ki yanxu ya qara fad'a cikin rashin damuwa da tsoron da ya bayyana a fuskar ta.

Ganin da gaske yake ta soma inda inda tana masa magiya, ya tsare fuskar ta da idanu yana fad'in don't allow me to repeat my self, ashe qaryar iskanci kike, idan kika bari raina ya baci you will regret kuma xan baki takardar sakin ki a yanxu.

Jin abinda ya fad'a cikin matsinancin tashin hankali ta soma cire undis dake jikinta ya rage daga ita sai pant da bra jikinta sai rawa yake.

Komai xaki cire, just only you nake son gani kafin raina ya baci, nan take kukan da take dannewa ya kwace mata ta tsugunna wurin had'e da riqo qafafun sa sosai tana kuka tana bashi haquri akan baxata qara ba.

Yanayin kukan ta ya sanyaya jikinsa yaji tausayinta sosai idan ya tuna cewa tabbas tana da haqqi akan sa amma meyasa take nuna masa ta halin ko qaqa sai ya kula ta ya so ta bata san cewa shi ba irin wad'annan maxan bane da take tunanin xata canxa su, rarrashi da biyayya su suke janyo xuciyar aiman kamar yanda afiya tayi dashi, hannuwansa ya saka ya d'ago ta ya had'a ta da jikinsa, bakinsa ya kai dai dai kunnuwanta ya soma magana a hankali wanda ya saka ta shiga wani yanayin da bata taba tsintar kanta a ciki ba.

Afiya ta fiki komai ki yarda ko kar ki yarda, ki daina kishi ko jin haushin matata domin itace uwargidan yarima, nuna min jikin ki da xakiyi baxai taba tayar da hankali na ba, ni likitan mata kuma likitan xuciya matan da suka fiki na gansu, Afiya kad'ai nake iya gani a haka na rud'e baxan jure ganin ta haka ba, ya fad'a tare da sumbatar ta a wuyan ta, ya janye jikinsa a hankali tare da fad'in am sorry wannan kad'ai xan iya maki a yanxu, ina son ki bana son ki duk ban sani ba har yau ban san matsayin Afiya a xuciya ta ba but she mean everything to me, ya juya ya fice ya bar ta tsaye wurin.

*
Kwana biyu da xuwan su Jordan ta kasa samun wayar ta, ta rasa inda wayar ta shiga neman duniya tayi bata gan ta ba sai ta soma tunanin ko ta barta gida Portugal ko kuma ta barta a jirgi, wayar ta qarama ta d'auko ta kunna ta soma kiran layin wayar baa d'auka ba, a wannan lokacin ilham na tsaye har lokacin bata dawo hayyacin ta ba, tsurawa wayar ido tayi dake haske, ta leqa kad'an dai dai wayar ta tsinke pic d'in afiya da sultan ya bayyana tana rungume da shi da qaton cake a gaban su.

Sun yi matuqar kyau sosai, ta fad'a tana fad'in shiyasa take rufe fuska da niqab ashe ita d'in kyakkyawa ce, sosai matar dake screen d'in wayar da yaron ta sun burge ta, may be ana kiran wayar ne saboda aji inda take, to idan aiman yaje bada wayar ya ganta kyakkyawa haka fa, qila ma bata da aure yace xai auri matar, sai taji kishin matar da bata sani ba, tayi sauri ta kwashe wayar gabaki d'aya kada aiman ya gani.

Afiya jin baa d'auki wayar ba ya sakata kiran saifullah kamar wanda ke jira ya soma yi mata fada sosai akan guduwa da tayi bayan mahaifin ta har qasar yaje neman ta bai same ta ba, sannan ta yanke hukunci batare da sanin sa ba dan da yana gidan bata isa ta barshi ba.

Tace koma menene naji xan koma gida nan bada jimawa ba Saif na fiso naje ta hannun sarki akan Abba ya riske ni da kansa wallahi xai iya kashe ni, mutum ne mai tsatstsauran ra'ayi ka fahimce ni.

Bai yi magana ba ya kashe wayar cikin takaici.?
[2/4, 7:01 PM] Nawarty: Littafina na kud'i ne, dan Allah kada ka karanta idan baka biya ba, ga mai buqatar siya ya tuntubi wannan number 08169334980.

Qara dialing number saif tayi ta dad'e tana ringing kamar baxai d'auka ba, ya d'aga batare da yayi magana ba.

Am so sorry amma dan Allah kaxo Jordan.

Can kika tafi kenan?

Ta gyad'a kai kamar yana ganin ta, tace dan Allah ka saurare ni wallahi xanje gida Nigeria very soon, dole xanje na nemi saki na a wurin sa saboda kai xuciyata tafi aminta da ita.

A tunanin ki kina ganin aiman xai iya baki takardar saki.

Eh mana xai iya, baya sona bai taba sona ba dan na nemi saki a gurin sa xai bani batare da damuwa.

Yace shikenan afiya nan da kwana biyu xan xo ki kula da sultan pls.

Ta sauke numfashi a hankali tare da fad'in ok tam, ta katse wayar.

Kallon sultan tayi da yayi kwance a jikinta kamar ba shi ba, ta shafa kansa a hankali tana fad'in?? cikin yana ciwo ne, yayi mata shiru ta leqa fuskarsa suka had'a ido sai ta sakar masa murmushi tana fad'in shine kake kyale mami yau sultan, ya saka hannu yana ture fuskarta ta soma dariya tana fad'in fushi kake da mami, ka manta na gaya ma babu kyau fushi da iyaye kome suka yi, ta rungumosa tana fad'in ai xamu je gida inda suzana xaka je skul and meet your friends shikenan.

Yace mami harda wurin New friend d'ina xaki kaini.

Waye shi kuma sultan?

Ya tashi yana kallon ta, nayi New friend mami a hospital.

Tace aush shikenan xan kai ka wurin sa.

Yace mami sunan sa iri d'aya dana daddy na Uncle ya hana na gayamasa sai ya d'auke ni kuma mami shi baya allura ni bai yi min ba sai yayi min pic wai muna kama dashi hakane mami?

Ta gyad'a kai tana kallon sa cikin murmushi tace xan kaika sultan very soon it seems you are happy with him.

Yes mami ya fad'a yana kallon ta tace shikenan.

*

Wayar aiman dake qara a hankali ta tayar da ita daga barcin da take, kamar xata janyo wayar sai kuma ta fasa saboda tsoron janyowa kanta shiga wata matsala.

Tana ji wayar na cigaba da ringing bata yi yunqurin d'auka ba dai dai lokacin ya fito daga wanka daure da towel a qugunsa, tayi saurin d'auke kanta gefe, bai masan tana yi ba ya d'auki wayar sa dake ringing.

Yarima jikin fadila ya rikice sai fisge fisge take likitoci suna kanta.

Hankalin sa ya tashi, batare da ya kashe wayar ba ya cillata kan bed ya soma shiri a hankali kamar ba ya so amma shi a gurin sa sauri ne yake hakan.

Ilham ta juya tana kallonsa ganin yana shirin fita tace har da yau fita xaka yi ka barni yarima, tun d'axu naxo amma baka kula ni ba har barci ya soma d'auka na, shine yanxu kuma kake shirin fita ka barni?

Batare da ya dube ta ba yace ashe naxo Jordan ne saboda na xauna tare dake ina kallon ki, sai kuma ya juya yana kallon ta kafin yace baki san darajar sarki kika ci ba har nayi wannan tafiyar da ke, ke kin isa.

Tayi shiru had'e da sunkuyar da kanta qasa wasu hawaye masu xafi na xubo mata, ance aure yana saka farin ciki da kwanciyar hankali ita har yau bata sami daya daga cikin wannan ba bayan tarin damuwa, wulaqanci da nadama, ina Ma wanda ke son ta ne ta aura take wulaqatawa a maimakon ita da ake wulaqantawa yanxu, tabbas ta rasa masoyi na haqiqa mai son ta da gaskiya wanda yayi alqawarin kasancewa da ita komai qunci na rayuwa yau ta guje shi ta kawo kanta inda bata da qima da daraja a wurin sa, tana kallo ya gama shirin sa ko kallon ta bai yi ba ya saka kai ya fice.

Ko da aiman ya isa jikin fadila ya tsanan ta sosai ga likitoci akan ta suna qoqarin bata taimakon gaggawa, kallo d'aya aiman yayi mata jikinsa yayi sanyi sosai hankalinsa ya tashi matuqa, mutuwa xata yi ya fada a xuciyarsa bayan ya kai hannun sa a karan hannun ta yana sauraren pulse d'in ta.

Ta bud'e ido da kyar tana kallon aiman, tace ina Bilal aiman wane hali yake ciki dan Allah ka kira shi na ganshi ko sau d'aya ne nasan mutuwa xanyi ina ji a jikina.

Aiman ya d'auke kansa gefe batare da yayi magana ba, Karo na farko a tsayin rayuwar sa da ya soma xubar da hawaye akan wani bayan mutuwar Bilal da ta xama dole yayi masa kuka, ya kasa had'a ido da ita ya rasa da wane ido xai dube ta da wane baki xai gaya mata Bilal ya tafi ya bar su har abada.

Ta damqo hannun sa cikin matsinancin axabar da take ji a jikin ta, kayi shiru yarima ina Bilal d'ina, ina so naga mijina dan Allah ka taimaka min.

Ya share kwalla a fakaice batare da ya bari ta fuskanci halin da yake ciki ba ya juyo yana kallon ta cikin murmushin qarfin hali yace da mama muka xo kin ganta ko na kira maki ita.

Tace na ganta yarima na tambaye ta Bilal itama bata cemin komai ba kamar yanda kai ma kake gudun amsa min inda mijina yake, meya sami mijina aiman.

Yace yanda kika ganni babu abinda ya same ni haka babu abinda ya sami Bilal, duk cikin mu uku da muka yi accident d'in ke kad'ai ce kika sami rauni, Bilal yayi kuka ya shiga damuwa sosai da rashin farfadowar ki fadila, gani yake kamar xai rasa ki ne har abada, mun jima sosai anan asibitin dashi baki farfado ba sai a jiya ya koma gida Nigeria saboda wani uxuri gobe xaki gansa ya dawo kada ki d'aga hankalin ki.

Ta sauke nauyayyen ajiyar xuciya tana jin wani sanyi na ratsa jikin ta ta ko ina, kallon sa tayi d'auke da murmushi? fuskarta, aiman ya juya ya bar d'akin xuwa ganin likita.

Fitar sa d'akin da wuya jikinta ya rikice, banda Kalmar shahada da take babu abinda ke fitowa daga bakin ta ko kafin su aiman su xo tuni rai yayi halin sa, kullu nafsin za'iqatil maut.

Aiman ya kira ya sanar da mutuwar fadila a nigeria sosai hankalin kowa ya tashi, sarki ya bada umarni ba sai an dawo da ita ba suyi mata duk abinda addini ya tanadar acan su bar ta can ne qasar ta.

Ilham ma taji mutuwar fadila sosai a xuciyar ta duk da basu saba da juna ba amma xuwa da take asibiti duba ta tana matuqar tausaya mata.

Bayan komai da kwana biyu suka tattara suka dawo gida Nigeria a yanxu babu abinda ruhi da xuciyar sa ke so kamar yaje Portugal neman afiya duk da Abba ya sanar dashi bata qasar akwai inda taje ta buya.

Ta ina xai soma daga neman afiya meyasa ya damu da ya neme ta a yanxu, meyasa ma yake damuwa da al'amarin ta, meyasa baxai yi watsi da lamarin ta ya daina damuwa da ita kamar farko ba.

I can't ya fada a hankali, na rasa Bilal na rasa afiya da yaro na baxai yiwu ba, yana buqatar afiya a rayuwar sa ko da baxai so ta ba xai nuna mata kulawa saboda ya saka ta farin ciki.

Ya qara kallon qayataccen falon nasa yana tuna sanda afiya take gidan bata yarda wata baiwa ta gyara sashen sa ba tun ranar farko da ya soma bata sharuddan sa ta d'auka duk yanda yayi da ita bata bari sai tace xata yi da kanta wani lokaci idan rumaisa tana gidan tare suke gudanar da komai, ya gashi wata baiwa sai hidima take a falon na ganin ta gyara shi kamar ko yaushe wanda baya ganin kyau duk gyaran da xaa yi masa idan ba afiya tayi ba, waccan ballagaxar da aka aura masa bata taba kwatanta yi masa wani gyaran daki ko kawo masa abinci yaci ba amma kullum bata da magiya kamar yaqi kula ta baya son ta yaqi bata haqqin ta sai kace ita tasan haqqin aure, ya ja qaramin tsaki dai dai lokacin baiwar dake gyara sashen sa ta fito d'akin sa ta russuna har qasa tare da miqa masa wayar dake hannun sa.

Ranka shi dad'e naga wannan ne a kayan da kaxo dasu yanxu ta fad'i shine na kawo ma Allah yasa banyi kuskure ba.

Batare da ya duba ko menene ba yace ajiye anan idanunsa na kan wayar sa, ta ajiye jiki na rawa ta tashi ta fice, ya bi abinda ta ajiye da kallo cikin mamaki yace acikin kayan sa kuma ina ya sami wannan wayar, sam ya manta da batun wayar shi, to ko a hotel d'in daya sauka wani ya bar wayar ya tattara yaxo da ita bai sani ba.

No ya tuna wannan wayar ta wannan matar ce mai niqab da suka had'u da ita a airport, ya kunna wayar yana fad'in qila tayi ta nema tana kira bata samu ba sam ya manta da baxai dawo da ita bai bada ta can a Jordan d'in ba.

Wayar na gama budewa pic d'in Afiya da sultan ya bayyana baro baro a screen d'in wayar.
[2/5, 8:12 PM] Nawarty: Littafina na kud'i ne, dan Allah kada ka karanta idan baka biya ba, ga mai buqatar siya ya tuntubi wannan number 08169334980.

Ya jujjuya wayar yana sake kallon pic dake kan wayar domin idanun sa sun kasa gasgasta abinda yake gani tamkar almara.

Har ya ajiye wayar ya sake d'auka tare da duba gallery cos wayar ba security afiya bata sakawa saboda sultan dake yawan game ko kallo da wayar.

Bai gama kallon pics d'in ba ya tashi a rude wannan wayar afiya ce, kenan afiya ce na had'u da ita ranar da niqab, ina tare da afiya ban sani ba taya hakan ta faru, meyasa take boye kanta gare ni, a ranar da ta bar Portugal kenan tare suka xo Jordan, ya salam ya fada a hankali tare da barin falon nasa.

Umma afiya tana Jordan, gobe xanje Jordan neman afiya umma.

Wane irin xance ne haka yarima, afiya da akace tana Portugal me kuma ya kaita Jordan ka kwantar da hankalin ka insha Allah xaa nemo afiya a duk inda ta shiga.

Umma da gaske na had'u da afiya Jordan ya fada yana nuna mata hotunan wayar, kingani umma amma a ranar ban san ita bace saboda ta saka niqab, umma afiya ta ganni ranar bata kula ni ba bata ji tana son ta dawo ta xauna da ni ba sai qara guduna take, meyasa umma?

Umma ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login