Showing 42001 words to 45000 words out of 153569 words
Chapter 15 - A Duniyata Book 1 Complete Hausa Novel
LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*
*_KAMAR SU_*
Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes
*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
____________________________
"Ranki ya dade.....girmanki ne ai" Idanunta ta lumshe sannan ta budesu,shima dai kaman sauran,gwanayen dadin baki da iya tsara mace,abinda basu da masaniya akai....ya zuwa yanzu babu wani d'a namiji da yake burgeta duk duniya. Sunan soyayya kawai da labarinta tana daukanshi a mazaunin wani wasa ne.....wasa da qwaqwalwa da wani salo na batawa kai lokaci.
Ya'aqoub,daya daga matasan mazan dake sharafinsu,kuma giyar soyayya da ta sha'awar sabreen suka yiwa qawanya. Daya daga cikin mazan da sukejin zasu iya kashe komai......zasu iya bada komai,hakanan zasu iya salwantar da komai saboda ita
"Ayimin afuwa nasan wataqila nazo da takura......ba wani abu nake bida ba illa a bani dama zan turo dan saqo da aike"
"Ka wuni lafiya?" Ta katseshi ya hanyar tambayar lafiyarsa. Wani boyayyen numfashi ya aje,daya daga cikin dabi'unta da suka banbanta dana sauran matan da ya sani wadanda suke rayuwa shigen tata......dabi'arta guda daya dake tsundumashi a kokwanto da tunanin WACECE ITA?,YADDA ZAHIRINTA YAKR HAKA BADININTA YAKE?.
Yana da tarin buqatu da yakeson gabatar mata dasu,saidai kwarjininta da wani irin shakkarta yakan daki zuciyarsa a duk sanda yayi yunqurin hakan. Ta sha bashi damar haduwa sama da damarmakin da take bawa kowa......hakan kuwa baya rasa nasaba da yadda yake kame kansa a gabanta
"Lafiya qalau.....saidai tsananin kewarki......na iso qasar nan da burin ki zama mutum ta farko da zan fara tozali da ita....... Amma inajin nauyin tambayar hakan don kada na aza miki abinda ranki baiso"
"Banayin abinda baniso......hakanan bana yin abinda zan takura" Ta fadi mishi kai tsaye kaman yadda halayyarta take.
"Na sani nadeeya" Ya amsa mata da karsashinsa,har sai da boyayyen murmushi ya kubce mata. NADEEYA shine stamp din ya'aqoub,kaman yadda muhseena yake stamp din MASHKUR,mashkur din da tayi imanin zuwa yanzun qila ya kusa zaucewa da rashin samunta a waya da bayayi. Shi kansa ya'aqoub din wata irin saa ya taka a sanda yayi katarin samun number wayarsa. Dashi da mashkur dukkansu ta hadu dasu ne a rana daya,saidai kuma a mabanbantan gurare da lokuta.
"Zaa yimin wannan alfarmar?" Ya tambayeta yana langabar da kansa tare da sassauta muryarsa da kyau
"Zan duba"
"Zuwa yaushe please......zuciyata a jigace take nadeeya.....i beg you karki sakamin lokaci da nisa....."
"Baka da damuwa" Ta sake bashi amsa a gajarce
"Dan saqo na yana iya isowa?"
"Sharada yahaya gusau road,najbil road" Ta fadi a nutse tana yanke kiran.
Wayar ya cire a kunnensa yana binta da kallo. Ya zaci inda yayi mata aike wancan karon wannan karon ma can za'a kai mata?. Iska ya furzar daga bakinsa,bata da wuyar canzawa tamkar waya hawainiya. Har yanzu bashi da wani yaqini ko tabbaci a kanta. Baisan komai a kanta ba banda suna da kamanninta. Yana da buqatar abubuwa masu yawa game da ita amma bata bashi dama ko qanqani a kanta ba.
"Allah yakai damo ga harawa" Ya fadi yana furzar da iska daga bakinsa. Ya miqe a hankali yana ture kyakkyawan mulmulallen table na glass dake gabansa cikin qawataccen falon nasa da ya tanada domin hutawarsa yana laluben number wayar babban yaronshi. Yanason saqon ya isa gareta da wuri,don yanason ya sanya qaimi ya matsa da kyau don samun kyakkyawan kusanci tare da ita.
A yadda ya ganta baiyi tsammanin za'a dauki wani dogon lokaci ba tare da ya samu abinda yakeso ba. Saidai duk sanda ya tuna yanayin jin kanta,miskilancinta da shariyarta,sai yaga eh.....ba abun mamaki bane,mata irinta daban Allah yake halittarsu.
Baki ta tabe tana ajjiye wayarta a gefe,sai kuma taja dan siririn tsaki tana sake bada duka hankalinta akan system din.
Folder da takanyi rubuce rubuce ta adana a duk sanda zuciyarta ta buqaci abokin hira ta shiga,ta budeta,sannan ta fara rubutun daga dukkan abinda taji tana da buqatar amayarwa.
Wata irin rayuwace da babu qawa ko aminiya......babu aboki ko amini......qawayenta sune qannenta da suka fito daga tsatso guda......saidai har kwanan gobe bata bari sun zame mata aminai ba.......saboda batason tunaninsu da hankulansu su gurbata ya zuwa wani tunani na daban. Tana jin itace dole.....kuma tilashin daukan alhakin komai yana a wuyanta.
Awa guda harda qarin wasu mintuna ta dauka kafin ringing na wayarta ya janye hankalinta. Ta dauke idanunta da suka dan sauya launi tana mayarwa kan wayartata,daidai sanda take iya jiyo hayaniya da ifce ifcen wasu daga cikin jikoki da yaran gidan. Bame son hayaniya bace sam,zata iya rayuwa cikin muhallin da babu motsin kowacce halitta sai ita......tana da wannan damar ta samarwa kanta irin wannan muhallin da kuma wannan rayuwar......amma qaqqarfan dalili guda daya tal zaya hanata kaiwa zuwa ga wannan burin nata,tna buqatar tsira da sauran burbushin MUTUNCINTA tana son ta sake tabbatarwa da kowanne me zargi abinda yake zargi a ransa yaji haka ne?,ko kuma ya sauya bigiren ra'ayinsa a kanta.
A nutse ta karanta sunan dake saman screen din,sai ta tattara dukka hankalinta akan kiran ta ture system din tana jingina sosai da makarin kujerar tata.
A nutse tayi mata sallama
"Wa'alaikumussalam" Aka amsa daga daya bangaren cikin matuqar nauyin jiki dana murya.
"Lafiya kike titi?" Sabreen din ta tambaya murya a sanyaye itama. Tana jin dukka wata gaba ta jikinta tana yin sanyi
"Alhamdulillah sabreen.....,saidai......"
"Aisha ko?,ayshatu?" Kai titi take jinjinawa tana qoqarin hadiye abinda yake taso mata. Saita kass cewa da sabreen din komai,bataso ta bijiro mata da abinda take da tabbacin itama yafi qarfinta......bataso ta bijiro mata da abinda zai hautsina nutsuwarta,duk kuwa da tarin qoqarinta.....sadaukarwa da tsaiwar dakanta akan yarinyar
"Titi ki fadamin me ya faru?" Ta sake jefa mata tambayar tana jin kamar ta tashi a daren ta iskesu a inda suke
"Ki nutsu sabreen.....Allah yana sane da halin da take ciki......kinyi iya yinki......kinyi kuma iya abinda zaki iya,mu barwa Allah komai"
"Titi ki fadamin!" Ta furta adan tsawace,tsawar ma da batasan ta yita ba
"Sabreen.....naira million takwas suke da buqata wajen aikinta" Wani qaramin jiri taji tana niyyar kayar da ita tana daga zaunen. Tayi luuu da idanunta tana son furta addu'a ko qwaya daya ce amma bakinta ya kasa lalubota.
"Tabbas titi akwai abinda kika boyemin......baya rabuwarmu wani abu ya biyo baya amma titi baki gayamin ba......tabbas" Ta fadi muryarta tana rawa. Tana ji har tsakiyar zuciyarta da ruhinta tausayin aisha kamar zai kasheta.
"Wannan wacce irin DUNIYA ce dake cike da al'umma masu tsananin son kansu?,duniyar da kowa kansa ya sani?" Ta fadi a sarari tana iya jiyo kukan titi wanda takeson boyewa.
Kasa riqe kanta itama tayi,sai kawai ta tsinke wayar,ta dora Fuskarta saman hannun kujerar da take kai. Ba zata iya riqe quncin da takeji saman qirjinta ba,ciwo nauyi da kuma radadin ya mata yawa. Abinda ta saba kamar kullum shi tafi buqatar yi a yanzu wato KUKA. KUKA abu guda daya daya zame mata solution na dukka matsalolinta,duk da ta dade da sanin kukan baya maganin komai.
A hankali take rera sirin kuka wanda take kokawa rayuwar su da rayuwar aisha. Tsananin talauci da rashin galihu ya sanya ta tsinci kanta a halin da take ciki yanzu. SON ZUCIYA da rufewar idanuwa da tsananin zallar rashin imani ya sanya yayi mata silar zamowa daya daga cikin mutanen dake ziyartar asibiti domin ganin LIKITAN ZUCIYA.....ciwon da yakai minzalin da take buqatar TIYATA don ceto rayuwarta
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:@Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 25
__________________________
*_ALBISHIR A GAREKU!!_*
*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*
*_KAMAR SU_*
Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes
*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
____________________________
Ita kanta batasan yawan lokacin data dauka a wajen ba,batasan kuma ta jima a wajen ba sai data fara jiyo muryoyin yaran gidan cikin wadanda ke zuwa islamiyya sannan ta tuna da HUDA NADRA DA HANEEFA.
Ta tabbatar muddin suka shigo suka sameta a irin wannan yanayin sai hankulansu ya tashi. Wani irin soyayya da kulawa suke mata,wadda sam sam basa qaunar abinda zai tabata komai qanqantarsa.
Da azama ta miqe tana leqa fuskarta tsakanin labulen falon zuwa filin tsakar gidan. Tanaso ta fita ta wanke fuskarta ta kuma daura alwala,amma bataso taci karo da kowa ballantana su tunzura hali da yanayin da take ciki.
Idanunta ta maida ta lumshe muryar titi tana mata amsa kuwwa a kunneta. Cikin duhuwar idanuwanta tana hangen aisha da wannan innocent face din nata. Har yanzu bata huce ba daga abinda azzalumin ya aikatawa aishan ba.....duk da burinta ya cika na danganashi da gidan kaso da tayi. Har yanzu tana jin kamar hukuncinsa yafi qarfin wannan hukuncin da akayi masa a yanzun.
Lokaci guda taji hankalinta yana neman tashi
"Million takwas" Sautin adadin kudin ya ratsa kwanyarta. Ta ina zata soma nema?,ta ina kuma zata samu?.
"Mashkur" Zuciyarta tayi mata hasashenshi farat daya. Tsam tayi da ranta tana juya sunan cikin zuciyarta. A hankali sai kuma ta dinga gyada kanta,tana bawa kanta da kanta tabbacin yes......a jikin mashkur yafi cancanta a hada wadannan kudaden,iya wannan tunanin ya sanyata juyawa zuwa dakin nasu da gaggawa tare da mantawa da niyyar fita zuwa tsakar gida da takeson yi.
Zama tayi sosai saman gadon daga gefe. Locker gadon dake hannun damanta wadda ba kasafai ta fiya budeta ba ta bude. Tarin tarkace ne a idanun mai kallo,amma a wajen sabreen wasu ajiyayyun abubuwa ne dake da tarin muhimmanci da amfani a wajenta a mabanbantan lokuta. Har ma idan ka tambayeta a wani lokacin tana iya ce maka SUNE SABREEN.
mitsitsiyar akwati ce wadda bata fi girman akwatin sanya zobe,ta saka hannu ta daukota sannan ta bude. Wani qaramin layi ta ciro ta rufe akwatin ta maidata,sannan ta dauki wata farar qaramar Samsung's ta bude gefanta ta zura layin ta maida wajen ta rufe sannan ta danne madannin dake gefen damanta. Take ta kawo haske,bayan bayyanar tambari da sunan kamfanin komai ya dawo daidai yadda ya dace.
Batakai ga danna komai ba saqonni suka fara turmutsutsun shigowa. Tsai tayi da idanunta tana kallon notifications din har suka gama jerin gwanon shigowarsu suka qare. Kaman ta sharesu ta isa kai tsaye ga abinda zai sadata da mashkur sai kuma ta sauya tunani.
Ma'ajiyar saqonnin ta shiga,ta fara bin sunayen mutanen da suka aje mata saqon daya bayan daya don bata jin tana da isashen lokacin da zata tsaya budewa da karantawa.
Kamar yadda ta zata,ta samu saqonnin mashkur da yawa fiye dana kowa,saita wuce kowanne saqo ta tafi saqon daya tura mata na qarshe kwanaki biyu da suka wuce.
Sallamarsa kadai ta amsa,ta tura masa ta maida wayar ta aje saman locker tana bin fuskar wayar da kallo,zuciyarta na shirya mata yadda komai zai tafi.
Ta jima da ajjiye mashkur saboda yadda zalamarsa ta fito a fili. Ta jima da ganin ta barshi a gefe saboda yadda halinsa yasha banban dana kowa cikin mutanen da ta taba tarayya dasu cikin rayuwarta. To amma yanzu silar matsalar aisha tana ganin wannan shine right time da zata koya masa darasi shima yabi sahun sauran mazan da suka shude cikin rayuwarta.
Agogon dake manne saman kanta ta kalla tana qoqarin dawo da nutsuwarta waje guda. Zuciyarta ke wani irin rawa tamkar dai ta soma gajiya da al'amuran da suke tunkarota cikin rayuwa. Wasu su shude,wasu kuma suna ci gaba da fuskantarta da babbar BARAZANA.
kamar mintuna goma sha biyar sun qaru akan lokacin dawowarsu daga islamiyya na ainihi. Aje dubanta tayi saman hijabinta na sallah,saita miqa hannu ta dauka tana miqewa da zummar duba inda suka maqale. Bata wasa da duk wani abu da ya shafesu musamman fita da dawowarsu gida. Duk da su din kwata kwata basu san ko ina ba idan ka dauke hayoyi da layukan dakan sadasu da makarantarsu.
Kaman jira akeyi tayi taku uku daidai wayar ta dauki ringing. Duk da ta jima bataji ringing din wayar ba amma babu abinda ta manta daga sautinta.
Taku ukun ta sakeyi ta dawo tana duban wayar bayan zuciyarta ta gama ayyana mata waye din me kira
"Mashkur" Kaman yadda ta aje number dinsa. Siririn murmushin da bata shirya ba ya subucewa labbanta. Tana tsaye tana ci gaba da duban wayar har ta qaraci burarinta ta yanke. Bata da niyyar daga kiran kwata kwata a yanzun,don ba tsarinta bane samun komai daga wajenta cikin sauqi ba. Ta yardarma kanta tana da tsada,tsadar data sanya kowanne namiji da zai ratsa ta cikin DUNIYARTA yarda da hakan,ya kuma bita da tsarinta a yadda ya sameta.
Kaman yadda ta zata bazai kira sau daya ya bari ba haka taji wayar ta sakeyin qara,salin alin ta koma ta maidata silent,sannan ta jawo Locker ta wurgata ta rufe ta kuma soma takawa hanyar falonsu tana zura hijabin saman wuyanta. Shimfidadden kwarjinin dake boye bayan fuskarta ya sake bayyana sosai tamkar ta sanya hijabin ne don ado ba domin biyan buqatarta ba.
Slippers dinta masu taushi ruwan hoda dake daga bakin qofar da zura ma fararen qafafunta,ta murda handle din qofar ta bude ta tura ta fito.
Fayau tsakar gidan nasu yake da wadataccen filin nan da baya rabo da tsafta duk da iyalin da gidan ke qunshe dashi. Kamar kowanne lokaci kamar kuma yadda suka maidata ABUN KALLO. Kowanne motsinta yana saman idanun mafi yawa daga cikinsu,bawai don su bata kulawar data dace ba....bawai don suyi mata gyara idan tayi kuskure ba......badon kulawa ta qauna ba.......saidai don wani radin kansu da biyan buqatar qashin kansu.
Tana da wani irin kaifin nazarin fahimtar meke kai kawo a kewayenta. A zaune take ko tafiya take?. Wani yanayi da a baya baya cikin dabi'unta,kuma bata dashi,amma yanayi da salon rayuwa ya tilastata kasancewa hakan.