Showing 24001 words to 27000 words out of 153569 words
Chapter 9 - A Duniyata Book 1 Complete Hausa Novel
Duk yadda lokaci yakai ga wulwula gudu,duk yadda zamani yakai ga fara yin tsaho da nesanta bawa daga dukkan tunani radadi da damuwoyin abubuwan da suka shude amma ya gaza yin nasara a kanta ta wannan fannin. Mahaifiya daban take cikin rayuwar 'ya'yanta,babu ma ya mahaifiya irin tata......jajirtacciyar uwa data zamewa maraicinsu sutura,ta zame musu bango abun dafawa,ta hana musu kuka akan rashin mahaifinsu.....sai gashi a yanzun suna kuka.....irin kukan da kunnuwa ba zasu iya ji ba,idanuwa ba zasu iya gani ba.......ta saka dukkan wani qarfi da iyawarta ta tare wannan shingen maraicin......tozarta da wulaqantar rayuwa dake shirin danne musu numfashi har ya zuwa lahirar duniyarsu.......tallafewar data sabbaba mata tarin ciwuka.......nauyi me yawa a qirjinta da rayuwarta......ya kuma bude mata qofofi masu fadin gaske cikin rayuwarta......ya maida JARUMA a mafi yawan lokuta.....wani lokacin kuma MAFARAUCIYA dake bude dukkan qarfin qwanji dana zuciyarta don cimma burikanta.
Ya dasa mata abubuwa masu yawa cikin ZUCIYARTA ya kuma sanya dolen dolen ta sauya akalar rayuwarta ta fanni da dama. Ta koma tamkar tarwada me wahalar kamawa cikin ruwan da take ninqaya. Ta kuma koma tamkar hawainiya dake canza kala a duk sanda taso hakan,ta bace ta kuma saje da duk yanayi ko launin da takeso ko kuma taga dama.
Tana da tarin sunaye masu yawa da a duniya a yanzun bayan ainihin sunanta na yanka SABREEN. Sunayen da ba'a yiwa yanka ba don tabbatuwar samuwarsu a kanta.
Akwai idanuwa bakuna da hankula masu zafi da batasan adadinsu ba a kanta. Kowanne kuma da irin nashi kallon.....hasashen da furucinsa dangane da ita.
Karon farko ta sakarwa fuskar nan tata murmurshi data fito tawai bisa fuskar madubin dame gabanta duk kuwa sa siririyar qwallar dake kwance cikin qwayoyin idanunta masu sheqi kaman an diga ruwan zaiba. Karaya da kuma qwarin gwiwa na karakaina tsakanin qirjin nata,saidai ko sau daya bata aminta ta dauki FADUWA TSORO ko kuma ja da baya ba.
K'aramin towel da yafi kama da handkerchief ta sanya ta tsane qwalla don kada ta bata daman fitowa,ta miqa hannu ta jawo stool ta zauna a kai tana saka hannunta tana kokawar daure sassalkan gashinta dake qoqarin kwancewa daga daurin farko datayi masa.
A nutse ta jawo set na kayan shafarta da take amfani dasu. Skin care product ne da suke mahadi da shower gel cream da sauran tarkace,wanda kudinsu duka zai tasamma dubu arba'in.
Kudi ne me nauyi da ciwo a wajen me qaramin qarfi,to saidai ta wajenta amfani dasu sun zame mata jiki kaman yadda suka zame mata wajibi. Tana son ado,tana qaunar tsafta da qamshi,wanda da a baya bata basu muhimmanci ba,saidai daga bisani ta gama karantunta tsaf......ta fahimci kowanne taku a rayuwa akwai abokin yinsa.....akwai sauyawar yanayi da ta zamewa jiki da rayuwa dole......dole sai an aiwatar da wasu abubuwa ake samun wasu abubuwan,dole sai an gusa koda da taki daya ne sannan ake samun wasu sabbin damarmakin suke shigowa rayuwar dan adam.
Gayunta na daya daga cikin abinda ya sake sama mata MUMMUNAR SHAIDA da kuma mummunan zato daga bakunan mutane da dama. Zaton daya kamata ya qona mata rai.....ya sanyata fidda qwalla masu zafi.....a maimakon hakan saidai kawai ta murmusa,ta kuma motsa ta barka a wajen da salon abun nan dake nuni da BANI DA LOKACINKI/KA.
Tsaf ta duk wani shafe shafe nata,ta kuma gyars gashinnan me tsanani yauqi sheqi da tsaho,ta dameshi cikin ribbon me dan girma,abinda ya sake bawa ainihin kamanninta fita ras kenan.
Koda ta bude ma'ajiyar kayanta tsaiwa tayi tana tunanin suturar da zata dace da jikinta a wannan lokaci. Shaqe take tafff da tarin suturu na alfarma,masu tsadar da koda ba'a gaya maka ba kai kanka ka sani. Suturun da a tashin farko xakasan sunfi qarfin wanzuwa cikin wannan wardrobe din.....kaman sunfi qarfin ma ace akwai wani cikin gidan daya mallaki masu darajarsu.
Juya zagayyayun idanunta tayi tana dan lumshesu kadan zuwa bangaren abaya. Sai data gama nazarinta sannan ta jawo daya daga ciki. Egyptian abaya ce me asalin daraja da kuma kyau wadda kudinta ya tasamman dubu arba'in da 'ya'ya. Sam sutura me tsada ba damuwarta bace,tana iya mallakarta a duk sanda tayi marmari ko kuma muradin hakan.
Da sanyinta dinnan da yake cikin halittarta take daura belt din da abayan yazo dashi bayan ta saka ta farko ta kuma dora alkyabbar da abayar tazo da ita. Siririn mayafi ta zaba daya dace da rigar tayi rolling me kyau da ma'ana,take zagayyar fuskarta ta fito cif tsakiyar veil din,sai ta kuma duba handbags dinta dake rataye sama da goma sha biyar kowacce da takalminta mahadi a qasanta.
'Yar qarama ta dauko qirar kamfanin D&G da takalminsa,ta natsa gaban madubi ta dauki turarenta ta bintike kan ta feshe jikinta dashi,sannan ta zari wayarta ta jefa a jaka tana duba agogon dake daure a tsintsar hannunta ta doso falon.
Jakar ta ajjiye tana jawo tea flask dinsu tana qoqarin budewa. Bata fiya son cin abinci da wurwuri da safe ba,to amma kuma tana tunanin zaiyi wahala idan ta fita din ta iya tsaiwa taci komai tasan halin kanta da kanta sarai.
A tsaitsaye take kurba kyawawan idanunta zube fes saman qaramar waya me keypad data dora saman cinyarta tanata qoqarin kiran wata number.
Bugu biyu aka dauka,muryarsa ta bayyana cikin wayar da wani irin shauqi da doki
"Da wacce irin saa yay na wayi gari ne?,ya Allah" Ya fadi yana zama gefan gadon bedroom dinsa.
Taqaitaccen murmushi me qaramin sauti ta sake tana kai cup din bakinta,can qasan ranta wani abu yana yawo gami da kai kawo a ciki. Gaba daya ta manta da rayuwarsa,taso kuma ta gogeshi a babin rayuwar tata gaba daya,to amma data tuna wani abu,sai take ganin ya kamata ko yaya shima a bashi darasi.
"Ina kika shiga don Allah,ina kika boye hanan?"
"Dukka wadannan tambayoyin basu kamaceka ba,tunda dai gani din na kuma kira ai sai ka ajjiyesu ko?"
"Haka ne ranki ya dade" Ya amsata da sauri ba tare daya damu da yadda matarshi ke tsaye saman kanshi tana dubansa cike da qunar zuciya da kuma takaici ba.
"Zaka iya samuna nan da mintuna goma a gaban flavours na gadon qaya?" Ta jefa masa tambayar tana ajiye cup din hannunta,daidai sanda yaron ya daga labulen falon bayan ya turo.qofar ya shigo. Washe mata baki yaron yayi,abinda ya sanyata murmusawa tana miqa masa hannunta dake daure da agogon fatan daya kwanta a jikinta sosai,gefe guda kuma tana sauraron amsarsa
"Ko mintuna biyar kika ce zanyi qoqarin kawo kaina"
"Yayi,saika qaraso" Ta amsa masa tana dan kauda wayar ba tare data kashe kiran ba.
"Wace tayi kiranka?,ina zaka je?,wallahi baka isa ka fita a gidan nan ba" Sautin muryar matar ya ratso ta cikin wayar. Lafiyayyen zagin da taji ya fita a bakinsa ya sanyata datse kiran ba tare data shiryawa hakan ba,ta lumshe ido tana jin yadda qirjinta yake quntata
"Har yanzu yana nan a yadda yake......har yanzu babu wani abu daya sauyashi" Kalaman dake karakaina a kwanyarta kenan
"Am sorry.....am sorry" Ta fada murya can qasa tana motsa labbanta.
Sanyin hannun yaron daya taba nata hannun ya sakata bude idanunta. Har ya qaraso inda take ba tare data ankara ba
"Antyn huda" Ya kira ta da sunan daya saba kiran nata
"Kaci abincin safe?" Ta tambayeshi tana dubansa. Girgiza kai yayi da sauri,sauta juya gefanta tana masa nuni da doguwar yatsarta
"Dauko wancan plate din ka cinye duk abinda yake ciki na barmaka" Da zumudinsa ya juya din yana nufar wajen. Zama yayi sosai bayan ya bude yaga abinda ke cikin,soyayyen chips da ragowar soyayyen qwai,ya fara kaiwa bakinsa yana murmurshin jin dadin garabasar daya samu.
Qananun surutai da muryarsu tun kafin sukai ga isowa falon shine yaja hankalinta. Ta kafe qofar falon da kallo har zuwa sanda suka yaye labulen suka bayyana,yana gaba tana binsa a baya......
*_TURQASHI_*
*_BIGI SAI BIGI_*
*_BABBAN GORO SAI MAGOGIN QARFE_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_Kina da burin samun ingantaccen TURAREN WUTA me TSANANIN KAMA GURI?_*
*_TURAREN WUTAR DA ZAKI SANYAWA DAKI AMMA HATTA DA LABULAYE KAYAN SAWAN DAKE SAQALE A DAKIN SU KAMA DA QAMSHI?_*
*_TURAREN WUTAR DA KUJERUNKI ZASU KAMA QAMSHI DARAM?_*
*_KI BANKADA LABULAYENKI KIJI SASSANYAN QAMSHI?_*
*QAMSHI IYA QAMSHI 24HR*
*HUMRA ME TSAYAWA A ZUCIYAR ME GIDA*
*NASAN ZAKI TAMBAYI KANKI A INA ZAN SAMU WANNAN?*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_tayi muku tanadin abubuwa da yawa irinsu_*
Khumra
Turaren wuta
Kulaccam
Lablab
Oil perfumes
Original musk tahara
Multipurpose spray
*karki kuskura kada kiyi ganganci ayi babu ke,kai tsaye tuntubeta ta wannan number*
08032119803
Ko ki lalubeta ta nanππΎππΎππΎ
*Instagram handle_incense by kabo daughter*
*Facebook_kabo daughter*
*Twitter_kabo daughter*
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:Huguma*
PAGE 16
___________________________
*_CIKIN DUBU DABAN TAKE_*
*_TABBAS AKWAI TURARE AKWAI MUNA TURARE_*
*_NA GWADA NA GANI_*
*_YA SUBHANALLAHI_*
*_QAMSHI NA TASHIN KAN ME GIDA_*
*_QAMSHIN DAKE DAGAWA KISHIYA HANKALI_*
*_NATACCEN QAMSHI DAKE KAMA GURI DARAM_*
*_WANNE GANGANCI NE YA SAKAKI TSAIWA SANYA?_*
*_ME KIKE JIRA?_*
*WANNAN DIN GUARANTEE NE FA*
*TASTED AND TRUSTED 100% PERCENT*
*KI SIYA KI GODEMIN HAJIYA*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_DUNIYAR TURARE ME BADA ASALIN QAMSHI ME KAMA JIKI DA MUHALLI,NUTSATSEN QAMSHI ME SANYAYA ZUCIYA DA DADEWA A WAJE_*
*_IDAN KINA DA MATSALA KINA NEMAN TURARE ME KAMA WAJE,KINASON SAKEWA OGA SABON QAMSHIN DAKI DA PARLOR,KE KANKI KINASO KI SHIGA WAJE A DINGA TAMBAYAR WACE TA ISO NE?_*
*MAZA MAZA JEKI KI GWADA WANNAN_*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER 08032119803*
*_zaki dariya za kuma ki godemin_*
*_gani ya kori ji_*
*hakanan sai an gwada akan san na qwarai*
_________________________
Idanunshi a kanta sanda yake shigowa zuwa cikin ainihin falon da yake da banbamci da sauran faluka dake gidan. Itama shi take kalla,kaman yadda suma bambanta a kamanni da mahaifinta haka suka bambanta a halaye da kuma dabi'u.
"Kai....kai,ubanka.....cireshi daga bakinka......tashi!" Matar dake biye dashi a baya ta furta a zabure bayan shigowarta dakin,idanunta kuma suka fada akansa sanda yake cin Chip's din hankalinsa kwance. Debe idanunta tayi daga kansu ta maida kan yaron da ya tsorata sosai saboda yasan halinta,ba shiri ya miqe tsaye har farantin chips din dake saman cinyarsa ya fadi,tsirarun dankalin ciki da yayi saura ya tarwatse a wajen.
Gewayesu yayi da gudu gudu zai fice yana matsawa daga wajenta amma duk da haka bai tsira ba,bayan uwar harara da take narka masa sai data bishi da ranqwashi tana cewa
"Bansan inda ka dauko kwadayi ba don ubanka,saidai daga can bangaren uban naka,don mu nan ba makwadaita bane,masu kwadayin ma addu'ar shiriya muke musu.....ba zaka jazamin masifa ba......cin abincin da aka da kudin haram?,ina zamana lafiya?,to muddin zaka ci gaba da shigowa dakin nan kuwa sawuna a likkafa zan maidaka gidan naka uban" Tayi maganar tana daga tsaye tana kallon qofar da tuni ya riga ya fice daga ita.
Dauke dubanta tayi daga kanta,don gugar zana irin wannan tash ba kasafai ta fiya damunta ba. Idan d sabo ta jima da sabawa da ita din,ta kuma zame mata jinin jiki.
"Ni zan fara gaidaki ko kece zaki fara gaidani?" Muryarsa ta dawo da hankalinta daga duniyar tunanin data fara nausawa. Fararen idanunta ta aza a kansa,mutumin dake a mazaunin mahaifi a gareta.....wanda ya kamata a ce a yanxun basu da tamkarshi,koda baiyi ya mahaifin nasu ba.....amma ya zamana ya toshe wani babban kaso cikin gibi da rayuwarsu zata samu.
Qaramin bakinta ta motsa wanda sauri yakan kira da shegen bakin rashin d'a da rashin mutunci,da wannan muryartata da sautinta ke cike da sanyi da nutsuwa tace
"Ina kwana kawu?"
"Lafiya qalau na kwana,sai uban baqinciki da takaicinki dake shirin hallakarmin da rayuwa" Ya furta cikin hargagi tamkar dama yana jiran ta gaidashinne.
Har yantsu dogon yatsanta yana saman labbanta,yayin data kafe mutumin data kira a dazu da kawun nata da idanunta,tana dan motsa yatsan nata saman lebenta tana kuma nazarin fuskarsa furucinsa dama motsinsa.
Ko sau daya bata taba ganin mutunci kima da martabarsa ba......daidai da misqala zarratin bata taba daukarshi da wani babban matsayi ba......abu daya ta sani,komai lalacewar fura tafi kashin shanu......komai kashinsa da zabgewa gami da lalacewar martabarsa a idanunta sunanshi kawunta kuma qani ga mahaifinta.
Maida idanunta tayi ta lumshe kawai kaman yadda ta saba masa a yawancin lokuta......tasan me ya sanyashi wannan zuwan,wani boyayyen buqatarsa ne dake a qasan rai da bai samu biyanta ba. Ta tuna haduwarsu ta qarshe dashi a wancan satin daya wuce. Dama ta sani ba zai haqura ba.....shine zai fake da wasu abubuwa wanda shi kansa ba kubuta yayi daga su ba.....yazo ya samu wannan matar da qiyayyarsu ta jima da yin tsiro da jijiyoyi a cikin jikinta. Takai qarshen maganar sanda take bude idanunta saman fuskar bibo.
Haduwa idanunsu sukayi waje daya da nata,ta juya qwayar idanunta tana watsa mata wani kallo
"Ki dain kallona da wadannan tsayyayun idanun naki na rashin kunya masu kama da idanun mage.......kai ya kamata ka tsaya a kanta saboda tana jawowa bawan Allah zagi,wanda ya jima da mantawa ya zauna a duniyar.....amma ina kyautata zaton kullum ta Allah sai mala'iku sun tadashi zaune sun nuna masa qazantar da d'iyar cikinsa ke aikatawa. Ya rasu yabar yara sama da goma sha takwas amma ba wadda ke hana masa kwanciya lafiya a kabarinsa sai ke?,ai wallahi Allah wadai da haihuwar d'iyoyi irinki.....indai haka haihuwar take gwara mutum ya zauna a haka" Tana maganar tana jujjuya hannunta guda daya gami da yarfeshi,idanunta a kafe saman fuskarta,kaman yadda itama tunda ta fara maganar ko sau daya bata dauke dubanta daga kan bibo ba.
Maganganun nata sunkai mata iyaka,tana jin ta gama daukar iya abinda zata dauka a iya wunin yau,saboda haka a nutse ta sauke qafafunta qasa ta miqa hannunta ta dauki handbag dinta ta miqe tsaye tana gyara rolling din mayafinta
"Fita zanyi,kuma ina da buqatar na kulle mana dakin kafin na fitan,idan ba damuwa ko zamu koma tsakar gida mu qarasa maganar a can?"
"Kaji ko?......dama ai na sani,babu wani sauran wanda take gani da kima a duniya.......yau koda fadima zata dawo duniya bata isa ta juyata ba bare alhaji" Tayi saurin cafe zancan.
Wani irin juyowa tayi gareta ta zube mata manyan fararen idanunta
"Kaman bakiji me nace ba ko?,nace muje tsakar gida mu qarasa......bankai ga furta cewa banda lokacin sauraro ba" Ta mata maganar dalla dalla tana kallonta.
Sosai bibo ta kafeta da kallo,har yanzu babu abinda zai sauyata......wannan rashin shakkar da rashin tsoron suna nan rubuce baro baro cikin ayyukanta da dukka motsinta,dakiyarta da shariyarta da daukan abu me zafi ta wulwulashi ta sauya masa mizani idan taso.
"Idan ta fito kawu qofar kawai zakaja jam lock din zai shige,ka sameni a qofar gida muddin baka wuce minti biyar ba" Tayi furucin sanda take takawa zata fice a falon tana riqe da vail din abayarta daya zame tana qoqarin mayar da rolling dinta yadda yake.
"Tashi muje na sameta a waje din inji da wacce hujjar zata kare kanta kuma" Ya furta dukka jikinsa na nuna zumudi da qaguwar yaga ya bita.
Da kallo bibo ta bishi tana daga zaune a kujerar ba tare data motsa ba baqinciki yana kasheta. A yau tana jin kaman ta tashi ta rufe rufa'i da duka. Yau ya tabbata mara amfani kwata kwata a garesu gaba daya.
"Ko nayi gaba kya rufe musu dakin?" A zafafe ta miqe tana gyara daurin dankwalinta
"In zauna inyi me a nan?,Allah ya sawwaqe,ai ni tawa son zuciyar bai fara sauka har takan kayan haramun ba" Ya jita sarai,ya kuma san da biyu take