Showing 114001 words to 117000 words out of 153569 words
Chapter 39 - A Duniyata Book 1 Complete Hausa Novel
cikin tsananin mamaki. Bai taba umartarsa da abu ba ya saba.....sai gashi s yau yana qoqarin bijire masa.......tabbacin akwai wani qaqqarfan dalili da kuma hujja kenan
"Abba...." Ya kirayi sunansa yana jin nauyin abinda zai furta din. Shurunsa ba abinda zai harfa tsakaninsa dashi sai gurguwar fahimta,bayaninsa din kuma bawai abu bane me dadin ji ko sauraro ba.
"Kasani Muhammadu.....koda baka bayar ba ni zan dauka na bata da kaina"
"Zan bayar abba.....zan bata amma bawai don zuciyata tana so ba......"
"Zuwa yaushe kenan?" Ya sake tambayar sa
"Zan yiwa sadiq magana,zai saka mata"
"Kirashi yanzu yanzu" Ya sake bashi umarni kai tsaye. Dole ya fidda waya ya turawa sadiq din saqon umarnin fidda kudaden,sannan ya aje wayar yana duban abban
"Zai sanya mata in sha Allahu". Ajiyar zuciya abban ya sauke. Shi kansa yasan akwai qalubale masu tarin yawa cikin rayuwarsa,to amma ko meye zaiyi yana yine saboda kyautatuwar rayuwa da kuma gobensu.
Kamar yadda ya saba lokaci bayan lokaci baya gajiya da yi musu nasiha dukkaninsu,yanzunma nasihar ce dai yayi masa.
Haka kawai sanda yake barin falon yaji hankalinsa bai kwanta ba. Muddin maamah tazo gidan to ya tabbatar akwai wani abu maras dadi daya biyo baya. Ko mene kuma ya farun yasan babu me gaya masa cikin gidan,daga amna sai musaddiq wanda baya gidan.
Yana takawa a farfajiyar gidan yana lalubar number amna din. Bugu daya ta daga tana amsa sallama a nutse
"Fito waje inason magana dake"
"To hamma" Ta amsa masa tana sauke plate din hannunta data gagara cin abincin ciki. Wayar tabi da kallo har yanzu muryar matar tana amsa kuwwa a kunnenta. Maganganunta sun girmi kunnuwanta,batasan komai a kanta ba amma tana ganin rashin kirki qarara daga dukkan wani motsi nata.
A tsaye ta sameshi idanunsa saman qananun shukokin dake bawa wajen iska me kyau da yanayi me dadi
"Zauna" Yace da ita yana nuna mata kujerar dake gabansa tare da qoqarin karantar fuskarta. Ba musu din ta zauna tana jin jikinta yana qara sanyaya daga kallon da taga yana yi mata
"Akwai baquwar da tazo gidan nan dazun?" Ya tambayeta yana kallon tsakiyar idanunta. Kallonsa itama tayi sai tayi qasa da kanta tana tuna gargadin da anni tayi mata
"Ba ruwanki da abinda tazo ta fadi,wannan ba abinda ya shafeki bane.....ba'a gaban kowa kuma akayi ba saike kadai...... Kada na soma jin zancan nan ya fita" Gargadin annin kenan bayan ta bar falon ta isketa a kitchen.
"Ehnnnn......kina nan sanda ta shigo na tabbatar......akwai wasu abubuwa data cewa anni da abba?" Ya sake tambayarta yana kallon fuskarta. Ba zata iya kallonsa kuma tayi masa qarya ba......hakanan ba zata iya saba maganar anni ba,don haka ta zabi sunkuyar da kanta ta kuma girgiza masa kai. Qaramin murmushi ne ya subuce masa wanda ba komai cikinsa sai bacin rai
"When kika fara yiwa hamma qarya amna?" Tambayar tasa saita rudata gaba daya,taji bata da sauran zabi illa ta shaida masa gaskiya.
Tambayar farkon data jefawa abban ita ta sanya fuad jan kujera shima ya zauna wani nauyi yana saukar masa. Ya ilahi.....wannan wacce irin jarabawa ce?,me yasa UWA take jin tasu jarabawar rayuwar?.
"Tashi kije" Ya bata umarnin daya sanyata miqewa da sauri tana barin wajen.
Tafin hannunsa ya sanya yadan daki goshinsa yana lumshe ido. A mizanin hankali da tunani da sanin ya kamata......yayi zaton maamah zata kasance ne cikin sahun farko na mutanen da ko kansu sukan sanya a gaba suka yanka ba zata ce komai ba.
****A hankali take takawa cikin layin zuciyarta na bugawa a hankali a hankali. Bugun zuciyartata ne batasan meye ainihin dalilin faruwarsa ba. Tsoron ganinsa takeyi ko kuma shauqin ganin nasa?.
Tun daga wancan ranar daya aike mata wasiqa ta qarshe bata sake jinsa ko kuma ganin motsinsa ba,har kawo yau da suke shirin cinye satin gab daya a kuma shiga sabon sati.
"Assalamu alaikum" Sautin sallamar daya sanya zuciyarta wani irinn bugawa ta ba zata,mamaki kuma da tsoro suka hanata amsawa saboda yadda taji alamun muryarta a shaqe take. Kasa waiwayawa tayi har zuwa sanda ya tako yana cimmata a inda take,ya zagaya kuma yana yiwa kansa matsaya a gabanta dab da ita. Yanayin kallon daya rutsata dashi ya hanata janyewa baya kaman yadda takeyi a duk sanda ya tsaya kusa da ita kamar haka
"Banga alamar kinyi kewata ba......inacan soyayyarki zata kasheni?" Ya furta yana karyar da wuya tare da komawa kalar tausayi ainun.
Idanunta ta fiddo waje tana dubansa
"Me ya sameka?" Ta samu bakinta da subucewa gami da tambayarsa kai tsaye.
"Ciwon sonki" Ya fada wani mayaudarin murmushi yana subuce masa. Nasararsa yake hange muraran daga idanun yarinyar,ya tabbatar yana dab da cika burinsa......yana kuma gab da daukan fansa.
Wata ajiyar zuciya taja tana sauke numfashi
"Bakiyi kewata ba huda sam sam" Ya sake fadi yana kalmashe wuya idanunsa cikin nata,yanason ya sake dasa mata dafin da zaiyi wahalar gogewa daga ranta. Yanason ya cimmata sosai,ya kuma nutsar da ita cikin tafkin qaunarsa fiye da yadda yayarta ta jefa masa qugiyar da har yanzu ya gaza zameta daga ruhinsa. Baya jin akwai wata mace da zata iya kashe masa qishirwarta. A kanta yakejin komai kuma ita kadai zata iya sama masa da wannan nutsuwar.
Saidai kuma ya karanci hakan wani abu ne da bazai taba samunsa ba.....don haka gwara yayi daukan fansan da zata gwammace bashi rayuwarta yayi yadda yaga dama da ita.
"Don Allah me kyau kice wani abu mana" Ya fada yana marairaice mata
"Nayi kewarka mana....." Ta samu kanta da furtawa. Yadda ya fidda idanu yana gwada mata mamakinsa ya sanyata jin kunya gami da mamakin kanta. Wani abu ne da yake faruwa da ita karo na farko a rayuwarta da bata taba tunanin zuwansa a nan kusa ba
"Da gaske kike?" Ya fadi har yanzu idanunsa a waje,sai tasa hannunta kawai ta lullube fuskarta dasu tana sakin qaramin murmushi,abinda ya sake fidda kamanninta sosai da sabreen.
"Don Allah yau daya ki bani aron mintunanki biyar" Ya fadi yana hade hannayensa waje guda. Mintunan biyar din da yake sanya ran a cikinsu zai qarasa dashen da ya dauko.
"Don Allah karkice aah,bazan sake neman wata alfarma ba daga wajenki ba daga wannan" Ya sake maganar yana qara marairaicewa da kyau.
Rabuwa biyu zuciyarta tayi,wani sashe na zuciyar tata yana cewa ta bashi damar.......yayin da wani sashen kuma yake cike da tsoro,tsoron da kusan kullum a cikinsa take.
Batasan yadda akayi ya shammaci rayuwarta har ta soma sabo dashi take kuma jin wasu baqin abubuwa a kansa ba,irin abinda bata taba jinsa akan kowa ba,koda kuwa cikin duniyar mafarkinta ko kuma hasashe.
Cikin qasa da mintuna biyar din daya dauka ya qarasa wargaza duk wani tunani nata. Sanda take takawa zuwa gida dauke da kalamansa masu nauyi.......ji ta dinga yi duniyar tamkar ita daya ce mace a ciki......dama haka zukatan dake da masu furta musu kalamai masu dadi sukeji?. Yau daya ta gasgata kalaman daya taba furta mata
"Har yanxu ke yarinya ce.....ba zakisan dadin rayuwa ba sai kinso kin kuma bada dama an soki......kowacce rai tana da buqatar wanda zai sota.....a lokacinne zaki karanci martaba da darajarki da kuma zamowarki cikakkiyar mace duk da qarancin shekarunki.
Hannunta takai tana shafa qaramar wayar daya bata wadda ke dauke da layi da kuma number dinsa. Ita kanta batasan adadin yawan roqon da yayi mata ba kafin ya karya zuciyarta ta aminta da karbar wayar ba
"Zanyi tafiya me nisan xango,a qalla zanyi watanni biyu ban saki a idanuna ba......bazan iya jurar rashin ganinki ba......" Kai take girgizawa a tsorace
"Yaa sabreen......"
"Ita kike tsoro?,zanje na nema dama a wajenta,kada ta rabani da abinda raina yakeso,zan roqeta ta barni na dinga jin muryarki....."
"Baka da hank......" Taji bakinta ya subuce da fadi.....sai kuma ta yiwa kanta waigi daga furta abinda tayi niyyar fada din a mugun tsorace. Yaa sabreen din da kullum kwanan duniya cikin kwatanta mata ta kaucewa sauraren kowanne d'a namiji har sai ta isa minzali?,yaa sabreen din da bata lamuncewa kowa mu'amala dasu ba komai kusancin dake tsakaninsu?,shine a yanzun yake neman kai kansa da kansa gabanta?.
"Huda......zan iya komai a kanki.....zan kuma iya komai saboda ke,ni kadai nasan zafin sonki da nakeji a raina.....don Allah ki karbi wayar nan......muryarki kawai xanji,daga gaisuwa idan kinso ki kashe wayar" . Ido ta zuba masa a mamakance jikinta kuma yana yin sanyi,wai dama haka soyayyar take?. Qwallar data gani shimfide a idanunsa suka karya duk wani qwarin gwiwa nata,kafiya da kuma dagiya,ta karbi wayar ba tare da tana da masaniyar ta karbi shiryayyen abu da zai wargaza musu rayuwa ba dukkaninsu......
Sake dafa wayar tayi sosai,qasan ranta tana jin qarin tausayinsa yadda yake faman marairaice mata,da alama soyayya ba qaramin kamu tayi masa ba. Dama wannan itace soyayyar?,dama haka akeji?,dama haka take iya canza mutum daga ainihin yadda ka sanshi?.
Ita kanta mamakin kanta takeyi yadda ya iya canzata gaba daya cikin qanqanin lokaci haka,amma kuma hakan fa yana nufin nan da shekara daya ko biyu kenan aure zatayi?. Tayi aure kuma yana nufin tabar yaa sabreen?,tabar nadra tabar haneefa?.
To wai ta yaya ma zata fuskanci yaa sabreen din da shi?,tace mata me?,bayan tsahon tasowarta idanunta basu taba gwada mata yaa sabreen din tana soyayya ba da kowa ma ballantana aure?,kullum zancanta yadda zasuyi zuzzurfan karatu kuma su zama wasu a gaba......wannan qudurin zai cika kuwa?.
Eh.... Wata zuciyar ta bata amsa daga wani gefan
"Shi karatu ai baya hana aure......kaman yadda aure baya hana karatu" Ta tuna da wata hira data jiyo 'yammatan ajinsu sunayi,abinda ya sanyata sakin murmushi kenan dai dai sanda take sanya qafarta cikin falon nasu.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 61
Dai dai lokacin sabreen din ke aje wayar mashkur wanda ya sanyata a lissafin yadda komai zaya kasance.
Shine mutum na farko daya matsanta mata da son ta bishi wani guri wajen garinsu. Da fari yaso ace dubai suka wuce,saidai tayi duk wata hikima tata ta kansile tafiyar da a baya ya tayar dayi musu shirinta gadan gadan. Baisan wace ainihin sabreen ba.....shi yasa ya gaza fahimtar dukka wadannan shirmen basa gabanta. Taqi kadan take jira ta yasar da qwallon mangwaro ta huta da quda.
A matse take.....kuma cikin matuqar buqatar kudaden saboda aikin ayshatu data tabbatar gab zuciyarta take ga kaiwa ga matakin da zata daina moruwa. Ko a jiya data ziyarci gidan jikinta yayi sanyi.......ta kuma sare sosai da yanayin jikin nata,har sun fidda rai da ita a wunin ranar,amma da yake shi rai idan yana da sauran shan ruwanshi a gaba to tabbas fa sai ya sha.
Motsin shigowarta ba tare da sallama ba ya sanyata daga fararen idanunta ta zubesu a kanta.
"Meye hakan kuma yau?" Tayi mata tambayar tana duban fuskarta wani abu yana darsuwa a ranta.
Fuskarta da fara'a ta juya tana fadin
"Au.......mantawa nayi wallahi" Saita tsaya daga qofar tana yin sallamar kamar yadda suka saba.
Sai data danyi jim kadan sannan ta amsa mata,ta bude labulen ta shigo,sabreen ta bita da kallo can qsan rabta wani abu yana kai kawo
"Sannu da gida" Ta fada tana nufar hanyar dakinsu,don sam ba'a sake take ba,Allah Allah take ta samu waje ta yiwa wayartata ajiya me kyau. Tasan halin yaa sabreen din qwarai da gaske,tana da mugun fikira da saurin dago wani abu dake a boye,a yanzun haka kallonta da takeyi din gani takeyi kaman tana kallon wayar ne tarwai bisa idanunta.
Bata iya amsa mata ba,tadai bita da kallo har zuwa sanda ta wuce dakin. Janye dubanta tayi daga bakin qofar dakin tana sauke numfashi. Bataso taji kokwanto ko shakka ko kadan akan 'yaruwarta......to amma haka kawai jikinta yake bata wani yanayi daban wanda bata saba jinsa ba akan huda din.
Duk da tasan ba kowa a dakin amma hakan bai hanata kallon gabas da yamma hagu da dama na dakin ba kafin ta ciro wayar daga aljihunta,ta kuma daga katifarsu daidai inda tafi kwanciya ta jefa wayar. Tana dagowa sabreen na daga labulen dakin ta shigo hade da sallama.
Wani mummunar faduwa gabanta yayi,ta amsa da sauri tana kuma waiwayawa,sai suka hada idanu da ita. Tsoronta ya qaru,ta dinga ji kamar ta ganta ne sanda take ajiyar.
Kanta da taga ta dauke shine abinda ya bata relief,ta sauke boyayyar ajiyar zuciya ta fara fidda uniform din jikinta.
"Huda" Tayi kiran sunanta sanda ta zauna bakin gadonta.
"Na'am" Ta sake amsa mata tana sakin rigar uniform dinta data kama zata fidda.
Idanunta ta zube mata,kafin tace komai haneefa da nadra sun shigo,wanda already sun rigata dawowa harma sun sauya uniform dinsu zuwa kayan gida
"Gashi yaa" Nadra ta fada tana miqa mata Leda
"Kuje falo a samu plate a juye yasha iska,gani nan fitowa" Ta amsa musu tana binsu da idanu har suka fice kafin ta maida dubanta ga huda
"Zo nan huda" Ta umarceta tana ci gaba da karantarta. Ba musu ta ajjiye dan kwalin hannunta sannan ta tako ta zauna a inda sabreen din tayi mata nuni.
Zuba mata idanu tayi tamkar yau ta fara ganin fuskarta,abinda ya sake sanya ma huda fargaba da shakku
"Kinsan na tsani nayi tambayar meke faruwa?,akwai matsala?......a bani amsa da babu komai....bayan kuma da matsalar.....akwai kuma abinda yake faruwar" Ta qarashe maganar idanunta har yanzu cikin na hudan.
Har cikin qashinta taji tambayar tata tamkar taba hango komai tar tar,saidai kuma wani sashe na maganarsa ya bata qwarin gwiwa tare da hikimar kaucewar tuhumarta
"Tunda har akwai tsoron yaa sabreen a ranki,bai kamata ki bari a yanzu tasan muna tare ba,har sai mun sake shaquwa da junanmu.....ta yadda koda ta tashi rabamu,tausayin yadda mukeson junanmu zai sanyata ta haqura......akwai lokacin da na ware da zamu sanar mata......kinga koda kuwa na girme mata nesa ba kusa ba.....amma dole nayi mata biyayya kema na tayaki yi mata biyayya ko ba haka ba?" Wasu daga cikin kalamansa da a yau suka sake sanyawa ta sake masa. Yadda ya mutunta mata yayar da duk duniya bata da abu mafi girman daraja irinsa.....bata jin zata kasa sonshi a ranta.
"Me yake faruwa huda......kome qanqantarsa kada ki boyemin" Ta furta tana kallonta.
Kanta ta girgiza tana narke fuskarta
"Me kika gani yaa sabreen......?" Itama kanta ta kada zuwa gefe guda gami da cije lips dinta na qasa,daga qasan zuciyarta ana gaya mata lallai akwai wani abu da ba dai dai ba.
"Canji nake hangowa dan kadan huda......wanda kowanne canji cikin rayuwa daga kadan kadan yake farawa" Ta amsa mata kai tsaye ba wani kwana kwana.
Zama tayi sosai hudan tana dubanta
"Ba komai yaa sabreen fa.....idan ma akwai din ni bazan boye miki ba"
"Kin tabbata?" Ta jefa mata tambayar da wani nannauyan sauti dake tabbatar mata tambayar me girma ce dake dauke da tarin fassarori da ma'anoni.
Kalamansa sukaci gaba da bata confidence,har ta daga kai cikin tabbatarwa
"Na tabbatar" Ido ta lumshe tana gyada kai
"Shikenan" Sai ta miqe itama tana daukar daya wayar tata wadda ita ta shigo da ita dakin.
Mika'il takeson tabowa.......tana da buqatar fara kawar dashi daga layin,koda kudin visa passport da bill na asibitin ta samu daga gareshi,idanma so samu ne ya zamana komai ya fita daga jikinsa,ta yadda duk abinda zai samu daga bangaren mashkur din zai zamana tamkar ribar qafa ce.
Akwai abubuwa da yawa da