Showing 48001 words to 51000 words out of 153569 words
Chapter 17 - A Duniyata Book 1 Complete Hausa Novel
/>
*_ALBISHIR A GAREKU!!_*
*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*
*_KAMAR SU_*
Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes
*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
_________________________
Duk da a qasan zuciyarta ba haka bane.
Idanunsa a kanta kaman bazai iya daina kallonta ba yana nashi seat din ya zauna
"Finally dai after wasu watanni......har na debe tsammani sai gashi......" Ya fada yana dan watsa hannayensa irin na gogaggun samari
"Me ma bahaushe yake cewa?.....me haquri ko?" Ya aza mata nauyin amsa tambayar ta hanyar kallonta da idanunsa.
Qaramin murmushi kawai ta saki tana maida bayanta ta jingina sosai da kujerar da take kai din,yayin data daba hankalinta gida biyu. Wani a gurinsa,wani kuma yana kan yanayin wajen dake cike da 'ya'ya mata. Tayi imanin dukkaninsu uwaye ne suka haifesu,koda ace akwai na gaba da fatiha to kadanne. Son rai son zuciya kwadayi su sukayi musu jagora zuwa ga turbar da suke kai a yanzu?. Ko kuma suma kamar ita dinne?.
"Yauwa......thanks" Taji ya furta,saita maido dubanta kanshi.
Idanu ya kashe mata cikin salon jan hankali me zafi,ya kuma sake matsowa sosai har yana rungumar table din da suke kai zuwa qirjinsa,sannan ya aje manual din da aka kawo ta hannun waitress.
"Choose babe" Ya fadi yana lanqwashe murya kamar wani mace gami da kanne mata idanu. Manual din da ya tura mata ta sauke idanu a kai. Tarin abinciccika ne iri daban daban,wanda ko kaffara ba zatayi ba idan ta qiyasta maqudan kudaden da za'a lasa ta sanadiyyar cinsu. Sai data qare musu kallo gaba da baya,yayin da shi da waitress din ke jiransa ba tare da sun qosa ba,saita maida ta ajiye saman table din. Ta motsa bakinta zatayi magana kenan sallamar da akayi da wata raunanniyar muryar taja hankalansu.
Dukkansu shi da ita suka maida dubansu ga wajen. Matashiya ce mai matsakaicin haske wadda idan ka kalleta a qiyasin da zaka fara yi mata duka duka shekarunta ba zasu haura ashirin da bakwai zuwa da takwas ba da haihuwa. Sanye take fallen zanin atamfa da kai tsaye zaka kirata da atamfa leda ko roba,duba da yadda ta cukuikuye a jikinta saboda tsufa da rashin quality da kuma yanayi na dan busawar iska data hadu dashi. Qasan zanin a cinye yake abinda zai wassafa maka kenan shekarun da atamfar ta dauka a duniya ana amfanarta. Hijabi ne a jikinta daya fara gajiya da rayuwa,tsananin sussuqewarsa ya sanya ya baiwa me kallo daman hango yaloluwar rigar dake a jikinta.
"Ke kuma fa?,daga ina wa kike nema?" Mashkur dake dubanta sama da qasa da wani irin qasqantaccen kallo ya jefa mata tambayar.
Rusunawa qasa tayi cikin matuqar taushi da karyar dakai ta hade hannuwanta biyu waje daya
"Taimako nake buqata yallabai......don Allah ka taimaka min da duk abinda Allah......"
"Wait.....wait mana" Ya fada a tsawace har hakan ya sanyata miqewa ta tsaya saman qafafunta. Waiwayawa yayi zuwa ga waitress din
"Yaushe wajen nan naku ya lalace?,yaushe kuka fara bawa mutane irin wadannan daman shigowa gurin nan.....wait.....wai bakusan kowa na zuwa irin nan bane don ya huta ya kuma yi uzurin gabanshi ba tare da kowa da komai yayi disturbing nashi ba?".
Duk joint din da basusan fuskar mashkur ba to tabbas ba cika joint ba......imma darajar wajen tsada da kuma darajarsa batakai ba......ko kuma dai kawai wajen bai cikin tsari da ra'ayinsa. Wannan abun ya sanya cikin rudewa ta soma bashi haquri tare da qoqarin nesanta matar daga wajen,duk da yadda kuwa take roqon su taimaka mata.
A nutse Sabreen ke kallon matashiyar zuwa ma'aikaciyar ma gaba daya. Yar uwarta nace ke qoqarin rabata da gurin don dai kawai kada ta batawa customer rai ta hanyar da babu girma arziqi ko darajta dan adam. Yanzun inda ace cikin kyakkyawar shiga take.....inda ace cikin dressing me kyau take......inda ace jikinta a gyare yake......inda ace zata koma hakan tabbas basai ta tsaya bagging a taimaketa ba. Ta cikin ruwan sanyi matasa dama manyan ire iren wadanda ke zaune yanzu haka a wajen zasuyita miqo mata buqatunsu,wanda yadda ta karba da hannu bibbiyu......kwatankwacin hakanne zata samu nata biyan buqatar.
"Dakata......barta ta dawo" Sabreen din ta samu kanta da furtawa idanunta da suka canza launi suna saman fuskar waitress din.
"Kamar yaya?,ki barta......" Mashkur ya furta yana maida idonsa ga matashiyar data fara takowa a hankali zuwa inda suke din
"Nooo" Ta amsa masa da wani sauti da yake tafe da wani irin zafi da ya motsa mata zuciya. Ganin matar kawai ya tuna mata abubuwa masu yawan gaske,ganinta ya fama mata wani babban ciwo,sai ta sanya hannunta cikin mitsitsiyar handbag dinta sannan ta zaroshi da dukkan kudin dake cikin jakar ta miqa mata.
Cike da mamaki take kallon fuskar sabreen din. Saita motsa kanta tana mata nuni da kudin. Wani irin karyewa zuciyar matar tayi,sannan ta sulale da wani irin qarfi ta tara hannuwanta tana amsar kudin. Jiki da muryarta dukka rawa suke sanda ta fara jera mata addu'a da godiya
"Ya isa jeki" Mashkur din ya fada yana fatan ta gusa ta basu waje ba tare data bata masa budget ko ta bata masa lokaci ba.
Cikin jikinta taji cewa ita din mashkur yake kallo. Ta lumshe idanunta tana qoqarin daidaita mode dinta,sai kuma daga bisani ta sauke mata wannan kallon nata dake saurin waftar hankali
"Are you okay?" Ya jefa mata tambayar cikin matuqar nuna kulawa. Sai da ta danyi gyaran murya sannan ta gyada kanta
"Am okay....."
"Am sorry ko?,irin wadannan mutanen dear ki daina gaggawar amincewa dasu ko basu taimako.....they are wicked wallahi at so many times......yanzun kalli yadda ta bata mode dinki gaba daya?" Gyara zamanta sosai tayi tana maida qafarta daya ta dora saman dayar,sannan ta sarqafe yatsunta saman qafarta tana sake zuba masa idanu. Rashin tausayi rashin imani da kuma rashin bawa dan adam darajarsa yana fita fes a tare dashi,wanda hakan ya sanya taji a ranta yayi deserving ayi punishing dinsa qwarai da gaske fiye da yadda ta shirya yi a baya.
Ya daddage yana sharhi akan baiwar Allahn da baisan wacece ba?,meye matsalarta?,meye damuwanta cikin sararin subhana?.
"Is okay ya wuce" Ta amsa masa a taqaice tana kallon agogon da yake daure a tsintsiyar hannunta.
Hankalinsa yadan dauko kadan,a duk sanda yaga tayi hakan alama ce dake nuna tana dab da yin layar zana,layar zanan da idan tayin baka isa bincikota ba sai sanda taga damar bayyanar maka.
"Times up?" Ya fada yana qureta da ido. Kadan ta saki murmushi
"Eh.....kusan haka ne"
"Ban yarda ba.....dole kici wani abu"
"Nop......banjin wannan.......zan wuce.....but soon zamu sake haduwa"
"Am......bamu tattauna komai bafa......if possible a qaramin minti goma kacal.....in sha Allah bazan haura haka ba" Hannuwanta ta aje daga daukan handbag dinta da tayi niyya,ta koma ta sake harde qafafunta tana kallonsa.
Shima idanun ya zuba mata yana jin yadda kowanne sashe na jikinsa yake da buqatarta
"Wai sai yaushe zaki soni kaman yadda nake sonki fateema?" Ya tambayeta bayan ya sauke wata wawiyar ajiyar zuciya. Dukka girarta guda biyun ta dage tana sake nazarinsa ta cikin qwayoyin idanunsa
"Ta yaya zaka zargeni da abinda ba haka bane?"
"U mean......kina sona kaman yadda nake sonki?" Sai data lumshe ido kadan as usual sannan ta gyada kai
"Okay,prove it" Ya fada da wani irin zumudi yana gyara zamansa sosai tare da rinjayar da gangar jikinsa zuwa zuwa mazauninta.
Ido tadan juya,reaction na fuskarta na nuna masa bata fahimta ba,a nutse ta motsa labbanta
"Like?....."
"Dis week nakeson zuwa dubai nayi annual leave dina......zanji farinciki fiye da yadda baki tsammani.....zanyi alfahari dake zan kuma mallaka miki komai da kike buri cikin rayuwarki......." Sai ya bude wallet nashi dake aje gefe,ya zaro wani qaramin littafi me abun rubutu a gefansa,ya buda tsakiyar littafin ya sanya biron,sannan ya aje mata shi a gabanta yana cewa
"Write it down.....,ko meye.....komai girmansa kada ki gaza rubutawa,and zai kasance ne as you wish" Fararen idanunta ta dora akan littafin kamar me nazarin launin takardar
"Musayar mutunci" Zuciyarta ta raya mata hakan. Wani zafi taji har cikin qwayar idanunta,saita dauke idanunta dama kanta daga wajen ta maidasu gefe. Cikin qasa da second biyar zuciyarta ta gama tsara komai,don haka ta waiwayo ta fuskanceshi sosai sanda yake fadin
"What happened fateema?....." Yana leqen fuskarta. Murmushin da ta fuskanceshi dashi ya sanya yaji relief,fatan samun nasararsa daya soma zagwanyewa duk sai yaji yana dawo masa.
"Nothing......kawai gani nayi kazo da qaramar buqatar da bata buqatar dogon sharhi da roqo har haka......kaman ma bata buqatar tafiyarmu wata qasa......nan ma zata iya zama dubai dinmu"
"Really?" Ya tambayeta da wani irin excitement a jikinsa dama fuskarsa.
"Yes" Ta amsa tana daga masa kai da nata guntin murmushin daya tsaya iya labbanta.
"Thank god.....thank you fateema......ban taba tunanin it gonna be easy kaman haka ba"
"Why?" Ta tambayeshi tana dubansa
"Ba zaki gane ba.....your are so unique fateema......alright.....now"
"Not now......am tired.....inason na koma gida na kwanta.....see you next time saimu qarasa tattaunawa"
"When?,ina gudun ki kufcemin fa?" Bata amsashi ba sai data gama gyara zaman rolling dinta
"Wannan ma kai kayi finding dina out ko nice"
"You are the one"
"Tom" Ta fada kawai tana shirin daukar jakarta,saidai kuma shi din ya rigata ta hanyar jawo jakar gabansa.
Duk da bata saka ido da kyau ba,amma idanunta sunga tamkar takardun kudin waje ya saka mata
"Thanks" Ta furta a gajarce ba tare da taga qima ko farinciki da kudin ba ko qanqani.
Ya sani,daya daga cikin rules nata shine baa yi mata rakiya idan zata tafi,don haka a nan yayi tsaye goye da hannayensa yana kallom nutsasen takunta har ta fice daga gurin.
Ko daya bata jin me busari yake fadi sanda suke tafiya a hanya. Gaba daya tunaninta yayi nisa zuwa wata duniyar ta daban.
Lissafe lissafe ne fal kwanyarta,tama rasa da wanne zata fara?,daga ina zata fara?,a ina kuma zaren lissafin nata zai katse. Zuciyarta da idanunta sunason zuwa ganin aishatu,to amma kuma bata so taje ta ganta a halin da take ciki alhalin bata tanadar mata da komai da zaya fiddata daga wannan yanayin ba. Jib ya kirata,ya tabbatar mata aiki duka ya kammalu daga bangare biyu,amma ta gaya masa ya saurara ta isa gida tukunna.
Goma saura busari ya ajiyeta daga gaban gidan nasu,ta sauke hand bag dinta ta zuge don masa ihsani kaman yadda ta saba,duk da shi din bai kawo komai cikin balance din da ha kamata ace ya kawo din ba amma bata damu ba. Sai data zura hannunta a jakar ta tuna bata da komai sai irin kudin da mashkur ya zuba mata. Tadan jawo kudin gaba kadan tana dubansu,sabbin US dollar ne qar dake qyalli da qamshin sabunta,saita maida dubanta a kanshi
"Zan saka maka wani abu busari ta account,ka bayarma inna kace tayimin addu'a,saida safe"
"Kinfi gaban haka......Allah ya bamu alkhairi" Ya fada yana dan bin bayanta da kallo. Yana mamakin kirki irin nata......duk da ita din zuma ce a wani lokuta idan bataso ba,ga zaqi ga kuma harbi. Ya tayar da napep din yana janyeshi da qofar gidan,qasan ransa kuma yana qididdige adadin alkhairinta a tattare dasu.
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 28
Sanda ta isa falon dukkansu ta samesu qudundune saman kujera,kowacce nannade da blanket dinta. Huda ce kadai zaune saman carpet nannade da hannayenta tana kallo a tashar Arewa24.
Tayi mata sannu da zuwa ta amsata tana wucewa ciki don rage kayan jikinta ta sauyasu zuwa da na bacci,gashinta ta kama ta daureshi waje daya ba tare da tasa komai ba,don bata fiya son abinda zai takurata ba duk sanda zata kwanta,ta shafe jikinta da daddadan turarenta me sanyin qamshi data wareshi ne kawai don kwanciya ta dawo falon.
Tsam huda ta miqe ta gabatarata da abinci,saidai bat jima da fara cin abincin ba wayarta ta dauki tsuwwa. Jib ne,qaramin tsaki ta saki,a lissafinta ta gama amsa kowanne kira don bacci take da buqatar tayi,tanaso gobe ta shiga wajen aysha taga yadda jikinnata yake. Abun ya tsaye mata a rai,tana jin cewa idan tana da dama a rayuwa zata sauya rayuwar Yarinyar ne gaba daya.
A kasalance ta kara wayar a kunnenta bayan tayi sallama ya amsa
"Ya akayi?" Ta tambayeshi
"Komai ya kammalu" Ya gaya mata kai tsaye. Dan shuru tayi tana saurarensa,daga yadda yake mata magana ya tabbatar mata fuskarshi qunshe take da fara'a duk kuwa da bata iya ganinsa.
"Okay.....meye result?"
"Bari na fara da abinda yafi damuna yafi kuma yimin dadi......da farko dai zan iya ce miki congratulations.......ina kyautata zaton indai zakiyi amfani da damarki sosai yadda ya dace,kin kusa fara shiga jerin sahun mata masu arziqi......kawai dai" Ya fada yana dan sauke qaramin numfashi
"Wani lokaci duk wani opportunity sai naga kamar kina shuresu ne da gangan......"
"Jib...." Ta ambaci sunansa
"Ina tare da ke,sai na yita tunanin fa me yake damunki?" Yadda yayi maganar a wani sanyaye ya sanyata murmushin dole. Tasan me yake buqata a nashi son rai ace tana yi
"Ka rasa wani abu ne?" Kai ya girgiza
"Ko kadan.....kawai daman da kike samu ya zarta yadda kik amfani da ita......"
"Bani labarin aiki na" Ta zabi shafe wancan maganar gaba daya,don ba me amfani bace a wajenta kamar yadda nashi hasashen yake bashi.
Ajiyar zuciya ya sauke,har tana iya jinsa ta cikin wayar
"Congratulations once again.......daga mashkur har mika'il.....suna daya daga cikin mutanen da suka mallaki manya manyan dukiya........sunyi tarayya ta wajen hali da dabi'a.........amma ta gurin source of income nasu sun sha banban"
"Ehnnnn" Ta fadi tana juya abincin gabanta da spoon ba tare da takai ko loma guda bakinta ba tun bayan kiran nata da yayi
"Mashkur dan kasuwa ne kamar yadda yace.....yana aiki tare da mahaifinsa......mika'il kuma wani babba ne a wani babban kamfani daya boye sunansa......don kamar yana cikin policy na kamfanin ma'aikata irinsa su dinga exposing kansu da rank dinsu cikin company din......saidai iya abinda hangena yakai......company ne babba dake samu da kuma biyan kowanne ma'aikaci albashi me matuqar tsoka" Yakai qarshe yana sauke numfashi tare da sararawa.
Ajiye spoon din tayi tana gyara zamanta, bayanan sun mata dadi sosai,kuma su suka haska mata akwai nasara akan mission nata. A hankali tadan aza dubanta akan huda,duk da hankalinta yana ga kallo,to amma kuma bata bari tayi dukkan wata magana data shafeta a gabansu
"Good job......na gode.....akwai sauran bayanai nasan,ina da sauran tambaya da qarin haske.......amma......bari zuwa gobe mayi waya"
"Alright.....to hakan yayi"
"Allan ya tashemu lafiya" Ta fada tana gintse kiran.
Wayar ta sauke tana bin fuskarta da kallo,tunani ne cinkus cikin zuciyarta. Fuskar matar dazu kawai ke mata yawo a idanu
"Meye amfanin dukiyar da bazaka bayar da ita ba fisabilillahi saidai qarfi ya qwata?" Ta furta a qasan ranta tana tambayar kanta