Showing 138001 words to 141000 words out of 153569 words

Chapter 47 - A Duniyata Book 1 Complete Hausa Novel

aishatu da dan rakiya daya visa na fita qasar india da ita da komai da komai da zaa buqata na asibiti lafiyarta da sauransu wanda ya lashe maquden kudin da suka ninka kudin da akayi hasashen zaa kashe din. Abu na biyu kuma ta zauna ta datse ta share ta kuma sake toshe kowacce hanya ko kafa da zata sake sadata da mikail.....sai data tabbatar ta sanya kowanne shinge da zai nesantata dashi nisa na har abada sannan ta tattare komai nata tana fita daga wajen.

_hmmm,anya kuwa kayan Muhammed fuad jadda zasu tabu 'yammata?,to muje zuwa dai muga yadda wasan zai kaya FUAD dinne keda nasara?,ko SABREEN?_

Karo na farko a rayuwarta da taji shigowar sabreen cikin gidan dama dakin gaba daya amma ta shareta kamar ma bataji ba. Tayi lakur saman gadon tana ci gaba da kwanciyarta.

Hirarsu da hameed yau ta dasa mata abubuwa da yawa cikin zuciyarta dangane da yayartata. Tayi amanna ta kuma yarda hameed mutumin kirki ne na qwarai,daga yadda yake yawan mata nasiha da wa'azin ta kare mutuncinta......ta guji yawace yawace da yawan fita barkatai.....don duk yarinyar data fiya fice fice,qafafunta basa zaman gidan tabbas akwai ayar tambaya a kanta ko taqi ko taso,alamar kamewa ga mace shine ta lazimci zaman gida.

A yau din ayoyi qwalli biyu da hadisai guda biyu suma daya karanto mata sunja hankalinta. Itakam hameed yayi mata,a yanzu dukka burinta shine tayi aure......tayi aure ta matsa daga rayuwar da take sake Fahimtar yaa sabreen din tana yi.....ta auri hameed tayi nesa daga cakwakiyar gidansu.....baqaqen maganganu zallar gori da habaice habaice. Ta tabbatar zata samu irin rayuwar da takeso daga wajen hameed,zai killaceta kaman yadda yake fadi din.

Tayi mamaki sosai da taga qofar tasu a bude,sanda ta shiga kuma falon sai ta tabbatar akwai wani a ciki,sai ta aje jakar hannunta ta kutsa uwar dakin.

Gaban gadon hudan ta qarasa tana kiran sunanta. Da farki sai tayi banza kamar bataji ba,har sai data saka hannu ta yaye bargon da take ciki

"Lafiya huda?" Ta tambayeta tana qoqarin son ganin fuskarta

"Lafiya qalau" Ta samu kanta da bata amsa kai tsaye. Wani irin mamaki yaso kasheta a tsaye,amma sai ta cinye wannan. Hudan a yanzun ta fara zama budurwa,shekara sha biyar ta fara hawa bigiren kaiwa yammatanci,tabbas zata iya faskantar canje canjen halaitada dabi'u a tattare da ita kaman yadda ta tabaji mamanta ta fadi a sanda take cika tata shekara sha biyar din,wanda a yanzun shekara biyar daidai kenan

"Idan har lafiya lau huda me zai hanaki zuwa makaranta kuma uhmmm?". Kamar ta bude bakinta ta gaya mata aure takeso,kamar ta bude baki tace ta bawa hameed ita,kamar tace mata ta gaji da ganinta kullum tana fita babu sahihin inda take zuwa,ba makaranta ba ba kasuwa ba,amma sai tace

"Gajiya nayi,amma zani gobe"

"Gajiya?" Ta maimaita qasan ranta,amma a sarari sai tace

"Allah ya kaimu" Ta juya zuwa sashen kayan sawarta tana fidda kayan jikinta don sauyawa da wasu. Can qasan ranta zuciyarta ta kasa samun nutsuwa,sake gaya mata takeyi

"AKWAI MATSALA.....DOLE KI NINKA SANYA IDANUNKI" da wannan tunanin ta kammala canza kayan sannan ta juya ta koma falon don duba me dame akayi da bata nan.

Da kallo ta bita har ta fice,sai taja qaramin tsaki qasan ranta zuciya da shaidan suna ayyana mata ko dame dame ma tayi sanda ta fitan?,caraf kuma wani sashe na zuciyartata ya kwabeta.

*D U N I Y A TA*

*_H U G U M A_*

PAGE 74

Kaman kowanne lokaci ya bawa kowa daman yayi order na abinda yakeso qarqashin kulawar sadiq da shike handling kusan komai.

Shi daya ya ware kansa a wani table da corner na daban,ya fidda system dinsa da ya sanya sadiq dauko masa ita. Ranshi a tsananin bace yake,amma kuma yana da wani irin abu,ya iya boye fushinsa idan yaso,ya iya kuma danne abinda yake damunsa,dole da rayuwa sun sanyashi iya controlling anger dinsa.

Yana da matuqar sani da zafi gami da kaifi ta bangaren computer.....ya koma da baya daga baya cikin karatunsa,ya zabi computer science ya kashe lokaci akai har sai daya zama qwararre kuma cikakke akan fannin,saidai ba kasafai ayyuka da cushewar abubuwa ke bashi daman practicing karatun nasa ba,amma komai nasa zaka sameshi a tsare da burbushi da alamu dake nuna yasan kan computer sarai.

A nutse ya soma bin komai daki dai cikin matuqar qwarewa tare da sanin makamar komai. Ba jimawa musaddiq ya iso wajen,sai yayi masa alama yayi joining sadiq kawai. Juyawa yayi yana matsawa daga wajen don tunda ya ganshi a hakan ya bawa system nutsuwarshi yasan akwai abinda yakeyi me amfani.

Ya samu sadiq din yana waya wanda ya kasa jurewa ya kira security team din da kansa. Ranshi a bace shima yake wayar,duk da abincinsa dake ajiye gabansa baiko bi ta kansa ba. Dan zuba masa ido musaddiq yayi kafin ya zauna,jikinsa kuma yana bashi lallai akwai wani abu. Jawo tray din yayi yana bude komai tare da warware spoon da fork din dake nade cikin tissue,ya sanya musu cikin abincin ya saita musu komai saidai still hankalinsa yana kan saddiq din.

Kusan mintuna goma sha biyar da isowarsa kafin ya kammala wayar,ya kasheta ya ajiye yana jan tsaki.

"What's going on?" Musaddiq ya jefa masa tambayar yana dage giranshi. Cup din daya zuba musu ruwa ya jawo yana kurba

"Scammers......hackers.....me ma zance ne musaddiq?". Idanu musaddiq ya waro waje yana kallon sadiq

"A'ina?Meye ya faru?"

"Sun diba maquden kudade daga cikin asusun company dazu........security team dinmu sun kasa aiwatar da komai......hamma fu'ad kuma baisan wanne matsaya ya dauka ba.....duk da nasan bazai qyale ba amma sai naga kaman ya dauki abun da sanya.....ina dai kyautata zaton yanzun yakebin kadin abun kamar ba kudi masu yawa aka diba ba" Saddiq yayi maganar yana maida hankalinsa ga fu'ad dake dan nesa dasu wanda baya iya ganinsa sosai da sosai

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Musaddiq ya soma maimaitawa yana rasa abun fadi kwata kwata.

Sannu a hankali ya soma bude idanunsa har ya gama budesu gaba daya

"Wayyo......." Ya furta yana miqewa sosai saman gadon yana jin yadda kanshi da idanunsa sukayi fresh. Komai ya sakeshi kenan,babu wani sauran burbushin giyar a tattare dashi,komai kuma zai tafi daidai yadda ya dace.

Idanunsa ya fara wurgawa cikin dakin bai ganta ba,sai ya barwa ranshi tana toilet ne tana shiryawa,don haka ya jawo wayarsa yana yana duba time

"Kai!" Ya fada a mamakance ganin irin baccin da yayi na kusan awa uku maimakon awa daya kacal kaman yadda yace zaiyi. Jikinsa ya danyi sanyi ganin yadda baccin yayi tsaho,zuciyarsa ta raya masa yarinyar nada wani irin aji da wahalar samu tamkar tarwada cikin ruwa,anya zata zauna duka wadannan awannin tana jira?.

"Da kuwa na tafka babbar asara" Ya furta a sarari gabanshi yana faduwa,sai ya jiye wayar ya miqe da hanzari ya nufi toilet din.

Duka bandakin ya duba ba ita ba alamar ta,sai ya fito ya soma duba dakin har zuwa balcony dake gaban dakin,lobby da sauran gurare,hakanan ya dawo zuciyarsa na harbawa da tsananin baqincikin kufcewar wannan damar a garesa

"Wai me yasa ma nasha barasa duk da sunan farinciki?,wannan tsinannen baccin......" Ya katse zancan bayan ya zauna gefan gadon yana dafe kansa da hannayensa bibbiyu.

Yadan jima a haka yana karatun asarar da yayi,da kuma wassafa yaushe zai sake samun irin wannan damar?.

Tsaki yaja sanda yaji wayarsa tana qara. Ya waiwaya yana duban me kiran,john ne chief of security team.

"Ubanshi zan masa......ya barni naji da asarar da nayi" Ya fada a sarari yana rejecting kiran.

Sake kira yayi bayan sakanni biyar kacal,hakan ya sake qufular dashi,don daga yanzu har wayewar gari har kwana uku bayajin zai huce daga asarar da ta sameshi.

Sake rejecting yayi,bai haqura ba ya sake kiransa a karo na uku. Wannan karon da niyyar cuccusa masa ashar ya dauki wayar,tunda a tsakaninsu kar tasan kar ne,saidai yana dagawa ya jefeshi da tambayar data sanya ya shiga tunani

"Kana tare da wayarka kuwa?,kasan me yake faruwa?,bakasan anyi kutse account din kamfani ba?". Dif wuta ta dauke masa,sai kuma ya bude bakinsa

" Kai john banason iskanci.....ka sanni na sanka,idan giyarka ka shawo ka daina gigin kirana ka bari ta sakeka tukunna,wayata tana hannuna......kuma ba wani abu daya faru,na sani fa ka dade kana harin muqamina,to qaryarka tasha qarya......in kanaso sai ka jira sai sanda matsayina ya qara daukaka a jadda company sai ka shiga takarar neman tsohon matsayi na" Daga haka ya katse kiran yana mitar shi baisan abinda yake damunsa ba zai qara masa damuwa.

Yankewa yayi kawai ya kirata ya lallasheta ya kuma sake shawo kanta,tunda kudin kwana biyu ma ya biya,ya samu ko wuni dayan gobe tayi masa tunda ya tabbatar ba zata taba dawowa a yau ba.

Saqon da idanunsa suka gane masa daga banking da kamfanin nasu ke ta'ammali dashi ya kusa sanya gudawa da fitsari duka yanke masa lokaci guda. Yayi wani mugun gigicewa sanda ya shiga saqon idanunsa suka haska masa adadin kudaden da aka zare daga asusun.

Wani irin abu yaji yana tsirga masa daga kowacce kafa ta gashi dake jikinsa. Gangar jikinsa yakejin kamar ba tashi ba ballantana ayi batun qafafunsa su samu daman iya daukansa,don haka sai kawai ya sulale ya zube ragwab a wajen yana jin kamar numfashinsa zai qwace masa.

Meye ma zaiyi ne?,ihu ko kuka?,hauka zaiyi ko mene?,kudade maqudai?,kudadenma kuma na kamfanin jadda?,kudaden da akansu yau suke lissafi zasu kuma gama lissafinsu a gobe?. Shin waye ya aikata hakan?,waye yake da alhakin aiwatar da hakan?. Yaushema abun ya faru?,wa zai soma kira ya tambaya bayan daga bakinsa ya kamata a fara ji?,wai yaushe ma abun ya faru ne?.

Ko sanda ya duba time na faruwar abun,da sanda John ya fara kiransa sai kawai ya saki wayar ya dora hannu saman kai yana fadin

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Da qarfin gaske,wanda kalmar ma sam batazo bakinsa ba sai sannan. Yana dire kalmar farko hawaye suka fara bin kuncinsa. Daidai sanda kuma kira ya shigo wayar tasa abinda ya sanyashi zabura kafin yakai dubansa ga wayar.

Sir sadiq daya gani a rubuce ya sanya fitsarin dole kubce masa duk kuwa da yadda yaso ga riqeshi. Ya shiga uku ya lalace,yasan tunda yaga kiran saddiq din magana ya gama isa kunnen boss. Da wanne baki zai kare kansa?,idan suka buqaci kuma ya biya a ina zai samu?,ta ina zai samosu?. Yayi imanin koda danginsa zai siyar bazai hada wadannan kudaden ba.

Zuciyar dake da Allah a cikinta......hakanan zuciyar dake da yawan ambaton Allah ce kadai ke samun nutsuwa a sadda bala'i ya durfafo ta,don haka dukka wata dabara da kuma nutsuwa sukayi qaura daga gareshi.

Ya dinga zirya yana kai kawo,ya kasa aiwatar da komai,ya kuma kasa kamo bakin zaren komai. A haka lokutan sallah duka suka shude masa,hakanan qarar kiraye kirayen mutane suka yita shiga kunnuwansa suna fita ba tare daya iya rabar inda wayar take ba.

Duk wani kira da zai shigo wayar tsoro yake bashi,baya qaunar koda rabar inda wayar ma take gaba daya.

Sai kusan bayan sallar ishai ya iya fusgo tunanin baiyi sallah ba,ya miqe yana hada hanya ya nufi toilet don cire jiqaqqen wandon jikinsa daya jiqe da fitsari ya dauraye jikinsa ya kuma daura alwala. Har a sannan sam tunaninsa bai kawo masa sabreen ba,ya mance sam sam da itama saboda tsananin rudanin daya shiga.

"Don't call him again......ka barshi,inason naga iya gudun ruwanshi......kafin sannan ni na gama nawa" Fuad yace da sadiq wanda ke shirin sake kiran mikail din karo na biyu

"Okay" Ya amsawa fuad din yana maida kansa ga titi.

Ring na wayarsa ya katse shurun daya gilma cikin motar. A hankali ya maida kallonsa kan screen din. Anni ce,sai a sannan ya manta bai kira ba bai kuma sanya an kirata ba wunin yau. Zuciyarsa tadan saki daga quntatar da take ciki,ya daga wayar yana sanyata a kunne.

Kusan tare suka yiwa juna sallama ita dashi,sai suka amsawa juna sannan tace

"Nace dai Allah yasa lafiya......daga ku har abbanku yau duka kunyi dare a waje"

"Lafiya lau anni.....ayyuka ne suka riqemu,wasu al'amura kuma suka taso wadanda su suka shagaltar dani daga kiranki"

"Babu komai......kada ka damu,tunda dai dukkaninku kuna lafiya to alhmdlh......farouq yace min kuna tare da musaddiq ko?"

"Eh muna tare anni"

"To Allah ya tsare,ya dawo daku lafiya"

"Ameen ya hayyu ya qayyumu" Ya amsa mata zuciyarsa na sake cika fal da qaunarta da qarin ganin kimarta. Tana taka muhimmiyar rawa qwarai da gaske wajen cike musu wawakeken gibi da ramin dake zukata da kuma rayuwarsu.

Tun da aka kirayi sallar magariba ta gama shirya komai,sannan ta sallami masu aikinta kamar jiya. Tsaf ta shirya cikin embroidery holland gold atamfa da keta sheqi da nuna ainihin tsadar sutturar. Tayi kyau abinta,kai ba zakace itace ta haifi zabgegen saurayi irin muhammad fuad da musaddiq ba. Ita din ba baya bace wajen iya kula da jiki da tattalin fatarta da dukkan abinda zaya qara mata lafiya da kuma quruciya.

Parlor ta koma tayi zaune bayan ta kunna tv ta kuma saita tashar da take ra'ayi. Ta kame saman daya daga cikin sofas din falon tana kallon hagunta da damanta. Kujerun take kallo,a ranta tana wassafa ranar da zatayi gwanjonsu. Duk da tsadarsu da kudaden da aka kashe wajen mallakarsu sam ita bata tuna wannan. Abu daya dake sake tsaye mata a rai shine,labarin katafaren ginin daular data samu cewa yana yi cikin garin abuja. Batasan ainihin wacce unguwa bace,amma me kawo labaran ya shaida mata cikin jerin unguwanni mafi daraja da tsada a garin abuje yake ginin,kamar yadda yakejin qishin qishin din yana nan yana tamfatsa wani a lagos.

*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 75

K'aramar qwafa taja,muddin da gaske wannan villa din yake ginawa.....indai da gaske hoton da me dauko rahotonta ya nuna mata fuad dinta ke ginawa.....to kuwa koda zatayi yawo tsirara ba zata taba bari ameena da hamza su sanya qafafunsu cikin wannan daular ba.

Wayarta ta dauko ya kira hajja harira,a nan suka bata lokaci me tsaho suna sake tsara yadda komai zaya kasance.

Batasan ma lokaci yaja haka ba sai da suka gama waya da hajja harira din. Ta kalli agogo tana mamakin rashin shigowarsu gidan,fargaba na saukar mata na kada fa yau ma a maimaita abun jiya?.

Bata samu fuad ba,amma ta samu musaddiq,ya amsa mata da zasu shigo,don shima baisan fuad din ya gama shirya yadda zasu cinye daren a waje ba.

Ci gaba tayi da duba lokaci mintuna bayan mintuna,saidai duk sanda ta kalli agogon sai ranta ya sake baci,haka ta sake jawo waya da xummar sake trying number musaddiq amma ta kasa samunsa.

Ranta ya sake baci qwarai,dama ta sani samun number fuad ba abu bane me sauqi,sau tari xaka iya kiransa ka kasa reaching dinsa,saboda ba da gama garin wayoyi yake amfani ba don dalili na tsaro da kuma matakin rayuwa da yake kai dole yana buqatar tsari akan komai nashi.

Dukka number dinsa taci gaba da gwadawa,number ta qarshe data kira taji alamun kiran ya soma tafiya,saita samu gefen kujera ta zauna tana furzar da iska

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login