Showing 45001 words to 48000 words out of 153569 words
Chapter 16 - A Duniyata Book 1 Complete Hausa Novel
Dab da rijiyar gidan wadda daga ita sai hanyar da zata sadaka da ainihin farfajiyar gidan ta ganta. Tsaye gaban rijiyar dauke da cup da alama ruwa ta gama sha.
Sanye take da atamfa classic da aka yiwa dinkin zamani riga da skirt daya zauna daidai jikinta. Kanta ba dankwali wannan zai baka damar hango baqar sumarta me sulbi da suka gada ainihi daga mahaifinsu.
Idanunsu cikin na juna na wasu sakanni,sai ta fara janye nata duban daga kanta tana ci gaba da nufar soron.
HADIYYA......Idan har a baya za'a gaya mata rayuwa zata ajeta a bigiren da suke kai a yanzun ita da ita zata qaryata......idan har a baya za'a gaya mata rayuwarsu zata koma kaman yadda take a yanzun zatace mummunan mafarki ne mara ma'ana....wanda bashi da tushe ballantana makama.
Hadiyya 'yaruwar haihuwarta,wanda mahaifi yayi silar zamowarsu jini daya......hadiyyan da suka taso qarqashin rainon mahaifiyarta......cikin daki guda saman shimfida guda,duk da murdadde kuma zazzafan kishin da mahaifiyarta ke bazawa.......amma hakan bai sauya komai ba na kusancinsu.
Sai gashi a yanzun sunyi irin rabuwar hannayen riga. A yanzun haka tana nata karatun cikin makarantar koyon aikin jinya bisa daukar nauyi da kulawar yayan mahaifiyarta......yayin da tata rayuwar tayi matuqar shan banban da ta hadiyyan.......take neman ta nutse cikin neman dauki da tallafin data gaza me kawo mata,har sai da tayi wani irin wawan tsalle da batasan zata sauka a daidai ko kuma garin saukar tana iya gamuwa da karaya da tarin raunukan da zasu zamewa rayuwarta tabo?. Takai qarshen tunanin sanda takai bakin qofar farfajiyar gidan ta farko,saita aza tafin hannunta saman fuskarta tadan shafi fuskar. Tasan bawai kuka takeyi ba,don a yanzun batajin cikin qwayar idanunta akwai sauran ruwan hawayen da suka rage da zasu bata hadin kan yin kuka. Kawai huci da dumin da fuskarta ya dauka takeso taji ya huce,idanunta sake mata dan zugi zugi tanason rage musu adadin iskar dake shiga cikinsu.
Karo sukayi da huda sanda take shirin fita shigowa su suna shirin shigowa. Suka ja baya dukkansu hudan tana dan riqe goshinta
"Ke kuma ina kuka tsaya haka dukka ku ukun har ana shirin kiran salla?" Ta jefa mata tamabayar tana tsareta da ido. Kafin huda tace komai haneefa ta tsinke da dariya
"Anty.......yaa nadra muka tsaya jira......bata bada hadda ba sai malam ya tsareta" Idanunta ta mayar kan nadra wadda fuskarta ke a daure
"Garin yaya?,kin soma wasa da haddar ne?" Kai ta girgiza da sauri,tana shirin magaa hudan ta rigata
"Kallo suka tsaya yi jiya da daren bayan kin kwanta" Fuska a daure ta sake maida kallonta a kansu
"Ashe?,yau zaku jawa kanku,sai na tsinke kowanne cable na kallo dake dakin nan"
"Ah wai.......ni abunnan yana dauremin kai?,wai lalatacce shike tarbiyya" Murya bibo ta ratsa kunnuwanta sanda take dubansu nadra.
Dukansu ido suka azawa bibo din lokacin da take kutsowa cikin gidan. Kaman yadda suka fita ne dazu,ita da daada,saidai kaman dazun ma daada ratsewa tayi ta wuce abinta ba tare data tsaya yiwa bibo tayin su wuce ba kamar dazun.
Motsawa kadan huda tayi wanda motsinta kadai ya sanar da SABREEN abinda take shirin yi. Yatsarta ta kada mata sautin da ya sanyata tsaiwa can tare da hadiyar wani abu me tauri a wuyanta
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:@Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 26
__________________________
*_ALBISHIR A GAREKU!!_*
*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*
*_KAMAR SU_*
Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes
*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
*_inganci da kwalliya shine muradinmu_*
__________________________
"Ku wuce muje" Sabreen tace dasu,suk sai sukayi gaba tana biye dasu a baya. Nadra ta hadawa kayan duka ta wuce musu dashi daki. Ita tayi tsaye dasu kowacce ta gama buqatarta suka daura alwala suka wuce daki.
Sallah sukayi bayan sun sauya uniform. Har a sannan tana ankare da yadda huda din keta hadiyar zuciya. Ta sani muddin tace zata saki huda tayi abinda takeso zaman bazaiwa kowa dadi ba......tafi huda zuciya nesa ba kusa ba......tafi huda dabi'ar take yanke.....amma me?,daga baya ta fahimci me irin wannan dabi'ar ba kasafai yake nasara ba.
Sai data kammala sallar magariban sannan tabi takan wayar. Ta samu miscal biyar hade da wasu saqonnin daga gefe. Tabi number tasa da kallo,sai a yanzu takejin ta shirya saurararsa. Kamar yasan tana riqe da wuyar saiga wani sabon kiran ya sake shigowa,don haka ta miqe a nutse ta koma daki tana matsawa daga inda su nadra dake cin abincin dare suke.
"Laifin me nayi dana cancanci wannan uqubar fateema?" Numfashi ta saki wanda sautinsa ya isa har kunnensa
"Ki gayamin ko meye nayi a shirye nake da na nema afuwa" Shuru ta sakeyi tamkar bata layin,saidai tana sauraren dukka maganganunsa
"Fateema" Ya sake kiranta da sunan da shine nasa STAMP din,sunansa ne shi daya,duk duniya shi ta mallakawa wannan sunan
"Naam" Ta amsa a karon farko tunda ya fara maganar
"Kinsan irin rayuwar dana tanadar miki?,kinsan irin gatan da nakeson miki?,kinsan yadda nakeson maidaki tauraruwa a cikin mata?,kinsan yadda nakeso ki koma tamkar sarauniya?"
"Dukka wadannan dama abinda ka lissafa basu nake da buqata ba"
"Me kike da buqata fateema......ki gayamin,a shirye nake na mallaka miki su......"
"Zamu iya haduwa?" Ta jefa masa tambayar
"Ko a ina nake a duniya a yanzun haka kika ce kina buqatar ganina zan wanzu a gabanki" Maida idanunta tayi ta lumshe sannan ta budesu
"Mu hadu yanzu fateema?,ko dan kadanne inaso naga fuskarki"
"Alright" Ta amsa masa a taqaice,abin da yazo masa a bazata,don haka a rude yace
"Venue?"
"Zan gaya maka,i will call you" Bata sake bashi daman cewa komai ba ta yanke kiran.
Wayar ta riqe a hannunta tana juyata a hankali bayan ta zubawa guri daya idanu. Lissafi ne fal Qwaqwalwarta,dole kafin ta samu abinda take nema saita yi haquri ta sake masa,dole ta dinga bashi mabanbantan gurare har zuwa sanda tsarinta zai fada aikinta zai cimma nasara.
A nutse ta miqe tana wassafa yadda zata fita yau din da dare,abinda sam ba dabi'arta bane saiya zama mugun dole,ba kuma zata iya tuna lokaci na qarshe da hakan ya taba faruwa da ita ba,amma yanzun dole ta fitan,tanason ta amintar dashi sosai a kanta.
Kai tsaye ta wuce ma'ajiyar kayanta tana duba suturar da zata dace da ra'ayinta a wannan lokacin. Da idanu ta gama qare musu musu,daga qarshe ta tsaya saman wasu Turkish dress masu strip skirt long sleeve shirt da doguwan kinomo sai madaidaicin veil da zai lullube saman kanta.
Sam bata da ra'ayin sutura me matse jiki duk kuwa da yadda mutane da yawa suke kallon ita tafi dacewa da irin wannan shigar.
Tsaf ta shirya cikin kayan kalolin navy blue da gray color. Sanda ta gama nada veil din a kanta sai data sake duban kanta sosai ta cikin madubin. Tayi wani irin sassanyan kyau me matuqar daukar hankali. Ta miqa hannu a nutse ta dauki turarenta ta feshe jikinta can qasan ranta tana jin fargaba kadan kadan kan haduwarta da mashkur,saidai kuma wani sashe na zuciyarta yana qarfafa mata gwiwar ba komai,wannan ne haduwan farko,nothing will happen.
Asalin wayarta ta jawo tana lalubar number JIB. bugu daya tak ya dauka,tadan motsa bakinta a nutse
"Ina fatan kana available kuma free"
"Ko ba hakan bane ai ya zama dole nayi creating time wa ke.....me kike buqata?"
"Connection" Ta fada a gajarce
" A daren nan?"
"Haka abun yazo,mashkur......mashkur alqali abdulkreem"
"Done.......wancan aikin ya kusa kammala......akwai ragowar information dana kasa accessing.....but...."
"Karka damu.....mu sanya wancan a mala.....wannan din shine yafi muhimmanci a yanzu"
"An gama.....bani code......let me write it" Ya fada yana dan riqe wayar kadan kafin yace
"Okay.....karanto" A nutse ta karanta masa wasi gajerun lambobi guda uku sannan ta katse kiran. Ta jawo locker madubinta ta ciro Bluetooth tayi danne danne saman wayar tata ta bada wasu sakanni sannan ta maqala a kunnenta. Saita aje wayar,ta dauki wancan Samsung din ta kunnata sannan ta fara yunqurin kira.
Bugu daya tak tayi aka daga,ta kalli wayar da mamaki sanda yake cewa
"Am ready to go princess......ina zaune a mota nida driver a parking lot na gida"
"Yayi.....but if possible ka taho kai daya mana"
"An gama" Ya amsa mata cikin farinciki hankali kwance.
Tana kammala saka takalma huda na shigowa dakin. Kallo daya tak tayi mata taga yanayinta ya sauya. Hudan tadan ritsata da idanu tana dubanta,saidai tun kafin takai ga tambayarta ta bata amsa
"Zan dan fita kadan amma yanzu zan dawo" Iya abinda ta gaya mata kenan ta fara takawa zata fice.
A jikinta taji yarinyar kallonta take,a jikinta taji tana tsaye ne kawai har yanzu,don haka ta tsaya cak sannan ta waiwayo. Ido suka hada,sai a sannan hudan ta kauda kanta. Iya hakan ya gayawa Sabreen maganganune sosai cikin zuciyarta,wataqila girma da kimarta kadai zai hanata ta furta mata su. Taku hudu tayi ta iso gaban hudan
"Dole ce ta saka zan fita huda......amma bazan wuce awa daya ba,idan na dade biyu"
"Amma anty...." Hudan ta furta fuskarta fal damuwa.
Yatsanta ta dora saman lips tana duban hudan,sai kuma daga bisani ta dauke yatsan tana aza dukka hannuwanta saman kafadarta,ta kuma zaunar da ita saman stool na madubin dakin
"Ke daya ce tal cikin mutanen da sukasan wace Sabreen gaba daya baya,kada kiyi tunanin na canza......ban canza ba huda.....kuma har abada bazan canza ba.....nayi alqawari......mommu da abba dake qarqashin qasa bazan bari suyi kaico dani ba" Kai ta gyada a hankali tana kallon Sabreen kamar yadda itama ita din take kallo. To amma a hankali tana rasa wannan yardar wanda tasirin maganganu daga kowanne saqo da lungu na layinsu dama unguwarsu ke kai kawo a kunnuwanta
"Don't lose hope huda......alqawari na.....bazan karyashi ba,ki kula da nadra da haneefa" Ta fadi mata daga qarshe ta juya tana fita a dakin. Nata ruhin yana motsuwa.
Har abada ba zata daina zargin maraici ba......har abada ba zata daina kuka dashi ba......a wani sashen na duniya,a irin wannan lokacin,diya kamarta tana qarqashin kulawar mahaifanta ne guda biyu.......ko kuma qarqashin kulawar wasu amintattun mutane da zasu zame mata makwafin iyayen.......sai gashi tata DUNIYAR ba haka bane,dukka kafadunta dauke suke da wani irin nauyi dakeson fin qarfinta ya kaita qas.
Daga baya baya ta sanya busari ya ajeta kafin akai ga shiga gurin a yanayi salo na kula da takunta kanta dama dukka wani motsi nata.
Sallamar busari tayi tace zata nemeshi idan hakan ta taso,sannan ta fara takawa a hankali tana nufar wajen.
A hankali take ratsa wajen cikin nutsuwa data zame mata dabia,tana takawa a hankali qamshinta da kuma yadda shigar ta amsheta kadai suka soma jan hankulan matasa da yawa wajen. Guri ne da yakan hada matasa maza da mata,wayayyu da suke da gogewa a fannin rayuwa kudi da kuma ilimi. Wajene kebantacce da yawansu suka maidashi gurin nishadi da kuma debe kewarsu,wasunsu a duk daren duniya,wasu kuma jifa jifa.
Yadda take daukan hankulansu haka kwarjininta ke dukansu,wannan ya sanya duk wani dakeson kawo mata caffa ya gaza yin hakan,saidai tazo ta ratsashi ta wuce shi kuma ya bita da kallo.
Tun daga nesa ta hangeshi,ya fita yayi tsaf cikin wani lafiyayyen jeans da shirt da suka dace da takalmin qafarsa. Kanshi pcap ce daya sauko da ita tadan rufe masa fuska. Hannunsa dauke da wayarsa yana latsawa a hankali ba tare daya damu da abinda ke kai kawo a wajen ba.
Ta sani,hankalin gomayyar 'yan mata dake wajen tabbas suna kanshi. Mashkur din ba irin mazan da mace me muradin jinsin maza irinsu zata kall sau daya bane ta iya kauda kai kota wofantar,kusan zata iya cewa ya hada dukkan komai,abubuwa da dama da mazan da suka taba ratsa rayuwarta ba wanda ya gama cikasu irin haka. Yana da kyau daidai gwargwado wanda kudi suka sake qawatashi,yayi karatu har zuwa matakin degree,hakanan dan wulaqanci ne shi,wulaqancin daya zame masa ado a idanun mata marasa kamun kai. Idanunsa a bude suke tarwai,yana da wata irin wayewa data zarta shekaru da kuma iliminsa,wanda hakan baya rasa nasaba da fita qasashen waje da yake yawan yi,musamman qasashen turawa.
Dab da zata iskeshi ya daga kansa sai suka hada ido. Zumbur ya miqe yana zube mata idonshi,har cikin zuciyarsa yana jin wani abu daya qarasa mamaye gangar jikinsa.
Karon farko daya soma jin ra'ayinsa akan mace na neman canzawa. A yanzun kallo daya tak.....cikin qasa da minti daya kacal ya soma ji a ransa kamar ya aureta shine abinda yafi dacewa dashi da ita gaba daya. Kamar alaqar daya shirya da dangantakar daya shirya ginawa a tsakaninsu ba ita ta dace ba,duk da har yanzu gaza fuskantar AINIHINTA....a wanne mataki na 'yammatan wannan zamanin take?. Wasu abubuwan nata na masa kama da dabi'un mace ta musamman.....amma wani motsin nata a wani lokacin sai ya sanya masa shakku akan haka. Kamar dai yanzun,yadda duk da duhun dare ya lullube sararin subhanana amma hakan bai dasa mata shakku ko ya zama dalilin qin fitowa su hadu ba.
A maimakon kujerar daya ja mata don ta zauna saita matsa kujera ta gaba,saidai kuma fuskarta a sake tana maida masa martanin murmushinsa.
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:@Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 27
_________________________